VOICE of Sheikhs

VOICE of Sheikhs Mun bude wannan cibiya mai suna Muryar shehunanmu domin yada karantarwar Ahlulbayt (A. S) +23480363

A cikin Tafarkin Sayyada Fatima (AS): Darussan Juriya da IbadaBincika babban gadon Sayyida Fatima (AS), alamar juriya da...
15/04/2024

A cikin Tafarkin Sayyada Fatima (AS): Darussan Juriya da Ibada

Bincika babban gadon Sayyida Fatima (AS), alamar juriya da imani, gano yadda ƙarfinta da shiru ya ci gaba da ƙarfafa a cikin tsararraki.

A tarihin Musulunci, Sayyada Fatima (AS) ta tsaya a matsayin wata siffa mai ban mamaki mai girman sadaukarwa da ƙarfi. Ko da yake ba a rubuta cikakkun bayanai game da rayuwarta ba, babban tasirinta yana faruwa ne ta hanyar matsayinta na diyar Annabi Muhammad (SAW), matar Imam Ali (AS), kuma uwa ga fitattun 'ya'ya.

Ita mace ce ta kyawawan halaye waɗanda ba kawai abin koyi ba ce, har ma tushe ce a cikin addinin Musulunci. Tarihin ta, na kusancin dangantakarta da Annabi (SAWW+), yana nuna hangen nesa da ta ke dashi na musamman akan juriya, bangaskiya, da ƙarfin tasiri.

Diyar Annabi (SAWW)

Diyar Annabi Muhammad (SAWW) Sayyada Fatima (AS), an karramata da lakabin "Ummul Abiha", wanda ke nuna matukar kulawa da kaunar mahaifinta. Wannan lakabi na musamman, wanda ake fassarawa zuwa 'mahaifiyar mahaifinta', yana nuna irin rawar da ta taka a rayuwar Annabi (SAWW).

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da kansa ya ce: “Fatima tsokar jiki na ce, kuma wanda ya fusata ta, ya fusata ni” (Sahihul Bukhari), wannan ba ya na nuni da irin Dangantakar ta da mahaifinta kawai ba, harma tana ba da misali na kauna da girmamawa marar iyaka dake tsakanin ya'yaye da iyaye.

Matar Imam Ali (AS)

A cikin aurenta da Imam Ali (AS), Sayyada Fatima (AS) ta misalta ma'anar aure ta gaskiya. Matsayinta yana ba da tallafi, ƙarfin hali, da juriya. A lokutan tashin hankali da s**a biyo bayan wafatin Annabi (SAWW), ta kasance ginshikin karfi mai ga Imam Ali, inda ta nuna yadda alaka za ta kasance da mutunta juna da ci gaban addini.

Tarayyar tasu ta kafa tarihi a tarihi a Musulunci, inda ta nuna yadda dangantakar auratayya za ta kasance ta tushe cikin fahimtar juna, da imani da juna, da kuma goyon bayan da ba ya gushewa.

Uwar Shugabanni

A matsayinta na uwa, tasirin tarbiyyar Sayyada Fatima ya yi tasiri wajen tsara halayen ‘ya’yanta – Imam Hassan, Imam Hussain AS), Sayyada Zainab, da Umm Kulthoom. Kowannensu ya zama misalan sadaukarwa, da tsayin daka, suna nuna zurfin ɗabi'ar Musulunci da aka cusa musu.

Dabi'unsu na nuni ne kai tsaye na tasirin mahaifiyarsu, kamar yadda ya zo a cikin Hadisi cewa, “Hassan da Hussaini (AS) su ne shugabannin samarin Aljanna, Fatima kuwa ita ce shugabar matan Aljanna ” (Tirmizi). Wannan ya nuna ba wai kawai matsayinta na uwa mai reno ba, har ma da muhimmiyar rawar da take takawa wajen tarbiyyar ’ya’yanta Addini da ɗabi’a.

Juriya da Qarfin Sayyada Fatima (AS)

Zurfin imanin Sayyada Fatima (AS) da juriyarta ya bayyana sosai a kan ƙalubalen da ta fuskanta, bayan Wafatin mahaifinta, a lokacin da ta tambayi hakkinta. A cikin wadannan fitintinu, imaninta ga Allah bai girgiza ba, kuma juriyarta ba ta gushe ba.

Rayuwar Sayyada Fatima (AS) fitila ce mai haskakawa, tana koya mana darussa masu kima dangane da juriya, imani, da karfin tasiri. Ƙarfinta na shiru yayin fuskantar bala'i, matsayinta na uwa mai raino, da goyon bayanta, ya'yanta sun kasance da hikima.

A cikin yin bimbini a kan rayuwarta, ba kawai tushen ƙarfi da shiriya ba ne, har ma babban misali na sadaukarwa da juriya a lokacin gwaji. Gadonta yana kwadaitar da mu zuwa ga gudanar da tamu rayuwar tare da imani ga Allah da kuma ƙudurta juriya.

MAKIRCIN DA AKE SHIRYAWA ALMAJIRAN SHEIKH IBRAHEEM ZAKZAKY.....Jami'an Tsaro sun ga sun gaza wajen sanya Kiyayyarmu a zu...
12/04/2024

MAKIRCIN DA AKE SHIRYAWA ALMAJIRAN SHEIKH IBRAHEEM ZAKZAKY.....

Jami'an Tsaro sun ga sun gaza wajen sanya Kiyayyarmu a zukatan mutane. Ana ta zagin su da yin Allah-wadai da harin da s**a kai mana a Kaduna.

Yanzu sun bullo da wata sabuwar makida, sun aika signal zuwa barikokin ƴan sanda, wai Harisawa za su kai wa jami'an tsaro harin daukar fansar abinda s**ai a Kaduna Juma'ar da ta gabata a wurin taron nuna Falasdinawa goyon baya wadda Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky s**a gabatar duka faɗin Nijeriya.

A kula, duk wani hari da aka ga an kaiwa jami'an tsaro da sunan da'awar Sheikh Zakzaky ba gaskiya bane, sune a ƙashin kansu s**a kaiwa kan su hari, akai mana abinda akai mana a Zariya ma bamu dauki fansa ba sai wannan?.

Harkar Musulunci da Malam Zakzaky ke Jagoran ta ba kara zube muke ba, muna da tsari da shugabanci, da ba don haka ba da tuni mun rushe, Allah ya ƙara shiga tsakanin na gari da mugu.

Uba Sani, Gwamnan Kaduna Allah ya isa.

Abinda yake ƙasa kwafin takardar ne muka samu ta sirri.

ƁARAYIN DAJI SU KASHE MU, SOJOJI MA SU KASHE MU...Wannan wane irin abu ne saboda Allah? yaushe za a ce wai shi soja bai ...
24/03/2024

ƁARAYIN DAJI SU KASHE MU, SOJOJI MA SU KASHE MU...

Wannan wane irin abu ne saboda Allah? yaushe za a ce wai shi soja bai da aiki sai kisa, kisa dai. Da ɗan abu ya faru tsakaninsu al’umma sai harbi da bindiga kai ka ce an ɗauke shi aiki ne dan ya kashe ’yan ƙasa, ba dan ya kare rayukansu ba.

Jiya Asabar abinda ya faru a Katsina tsakanin Ƙofar Guga zuwa chake (filin bugu) duk wanda ke wannan yankin sai da ya ɗanɗana kuɗarsa da wanda ya ji da wanda bai ji ba, ƙarshe sojoji sun raunata mutane har da kisan mutum 1, tear gas kau ba a magana.

Ai ko da laifin su civilian ne to bai kamata kai Soja ka yi amfani da bullet ba, ai akwai hanyoyi daban-daban da ɓangaren tsaro ya tanada domin tarwatsa mutane ba sai an yi amfani da bindiga ba b***e har abu ya kai ga kisa da live ammunation. Wannan abin zalinci ne kuma gaskiya idan hakan ya cigaba da faruwa to rikici ne zai cigaba da hauhawa a cikin garin Katsina domin jama’a ba za su zura ido a riƙa kashe su haka nan ba.

Saboda Allah, ɓarayin daji su kashe mu, kuma ku biyomu har cikin gari ku riƙa kashe mu, alhali kun kasa kare rayukammu daga ta’addancinsu (Kidnappers). B***e ma bisa binciken da nayi, ya nuna da yawan mutane na kokawa irin yadda sojojin ke wulaƙanta jama’a da keta dokar hanya, idan s**a taho ko waye kai za su bi ta kanka su wuce, ko kuma sai dai ka ji duka. To haka ake tsaro? abin hauka ne, yaushe wanda aka ɗauke ka dan ka kare rayuwarsa kuma shi ne maƙiyinka?

Lallai gwamnatin Katsina ta ɗauki matakin da ya dace tun da wuri, dan nan gaba abin zai iya zama wani abu daban. Daga ƙarshe ina jajanta wa waɗanda aka raunata da kuma ta’aziyya ga iyalan wanda ya rasa ransa, Allah jiƙansa ya tsare gaba. Allah ya wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma ta.

— Bin Yaqoub Katsina ✍🏾
24/03/2024

Dalilin Tallar Mazhabar Gado A HangenaAbubuwa da dama da suke faruwa a wannan kafar na 'Social Media' a tsakanin nan, su...
18/03/2024

Dalilin Tallar Mazhabar Gado A Hangena

Abubuwa da dama da suke faruwa a wannan kafar na 'Social Media' a tsakanin nan, suna kara min fahimtar zurfin gazawarmu ne, da kuma irin kulen da ke gabanmu ta kowane janibi.

Da Cibiyar Wallafa ta fara saka Videos din Tafsirin Alkur’ani Mai Girma na Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), na rika bibiyan shafukan da ake 'Sharing' din Tafseer din daban daban, na ga tsokacin mutane da dama, wanda yake nuna cewa mutane da yawa basu taba kallo ko sauraren Shaikh Zakzaky na Tafseer ba sam.

Na ga tsokaci iri-iri daga mutane, daga ciki akwai masu cewa, an ce bai iya Tafsiri ba, amma gashi sun kalli Tafsirinsa sun kuma ƙaru. Wasu kuma suna cewa, Tafsirin dalla-dalla yake yi, kowace Aya ma'anarta na fita fes, amma matsalarsu ita ce ruwayoyin Shi'a ake fassara da su. Wasu kuma har mamaki suke yi, cewa dama yana ma Tafsirin? A yayin da wasu suke cewa an ce musu ya fi shekara 10 yana Tafsirin Suratul Fatiha bai gama ba, ashe har saukan Tafsirin ya yi?

Sai na fahimci, mutane da dama sun san Jagora (H) ne kawai a jawabansa da muke yadawa na tarurruka, wanda wasu a wajensu jawabi ba karatu ba ne, ko da kuwa ilimi ake fada a ciki, bude littafi a karantar shi ne karatu. Don haka, da ba su taba jin Tafseer ba, ba su saurari tarjama da sharhin Nahjul Balagha ba, sai s**a dauka ba a karantar da karatu ne.

To kuma hatta a jawaban Munasabobi din, mun fi damuwa da yada wanda zai jawo 'trend' ne, ba wanda zai bayyana wa al'umma hakikanin sakon addini da Da'awar komawa gare shi ba. Don haka sai s**a dauka yawanci kamar sauran mutane, Jagora (H) kan yi tsokaci ne shi ma kan wani abu in ya faru irin tsokacin da sauran Amawan Malamai ke yi, amma baya bayani kan manufa da hadafi da salo da gaya na kira zuwa ga addini, tunda ba mu nemo mun sakar musu ba.

Sannan kuma, biye wa Amawan mutane da mukan yi a kan dan abu kankani da s**an ɗago da shi, yana sa mu koma musu aiki, sai ya zama kullum kare kai muke yi, maimakon ya zama muna fito musu da abubuwa ne ko da su za su zama masu korewa ko kare kan nasu.

Idan muka cigaba da gazawa wajen bayyana Da'awar nan yadda ya kamata, muka tsaya aikata shirme da bin salon wawaye na neman 'Likers da Followers' masu yawa a shafukanmu kawai, za a wayi gari makiyanmu su ke shafe lokaci suna bayani a kanmu a gamsu, a yayin da muryarmu zai zama ya dushe ta yadda ko mun yi magana ba zai yi tasiri ba. Daga nan ne sai ya zama ba a san mu a hakikarmu ba, ba a san Da'awar da muke ba, ba a fahimci Aqidarmu ba, sai a fara mana tallar Mazhabar gado, da nasihar mu bar Mazhabar Ahlulbaitin Annabi (S) wanda shi ne sahihin addinin Musulunci.

Ya hau kan Malamanmu, da sauran daliban Ilimi da ke wannan kafar, su dukufa wajen yin Videos, da rubuce-rubuce masu dauke da hakikanin sakon wannan addini (Mazhabar Ahlulbaiti (AS), bangaren Aqida (Tauhidi), da Akhlaq, da Fiqihu, da dukkan fannoni, ta yadda in irin wannan s**a yawaita, za su danne fassarar makiya da s**a bude wuta a kan dole sai sun yi bayani a kanmu.

Kuma a rika rubutu ko bayani din ne ba da sigar ana ma wani raddi ba, da sigar ana karantar da al'umma ne ana bayyana ilimi tare da kiyaye ladabin bayyanawar. Kar kuma a damu da sai mutane sun nuna suna bibiya, ko ana nuna ba a samu ba, a cigaba da yi saboda Allah, yana nan ana amfana, kuma nan gaba za a ga amfanin na sosai, a yayin da kila ma babu ranmu, ba na masu jirkita fahimtarmu.

Allah Ya mana Jagora bakidaya. Ya fahimtar da al'ummar nan hakikanin Wasiyyar Manzon Allah (S), Ya sa su yi riko da shi, don mu kubuta a duniya da lahira.

Dafatan an sha ruwa lafiya. Allah Ya amshi ibada bakidaya.

— Saifullahi M Kabir
8 Ramadan 1445 (18/3/2024).

MUTANE KOMAI SAI SU ƊAURAWA UBANGIJINSU. _ Inji Sheikh Yaƙub Yahaya Katsina.Daga: Hassan Abubakar Ahmad Katsina Allah (S...
17/03/2024

MUTANE KOMAI SAI SU ƊAURAWA UBANGIJINSU. _ Inji Sheikh Yaƙub Yahaya Katsina.

Daga: Hassan Abubakar Ahmad Katsina

Allah (Swt) ya gwada yadda ake komawa wajen sa, kuma ya yi uziri. Bai makamata kuna ɗauko matsalolinku ba, kuna ɗaurawa Allah (Swt) ba. Ba ruwan Allah domin Allah ya gama komai, ya yi mana komi.

Ya ci gaba da cewa: "In ka laluba aljihunka kaji babu komi (kuɗi), sai kace Allah ya tsinewa Gwamnati". Dami ake siyan abinci? Wake buga kuɗi? Kuma kuɗin suna ina? Kuma sai ya zama komi lefin Allah (Swt) ne? Allah ya yi nasa, Gwamnati ta hana nata. To lefin na waye? Saboda haka ya kamata Ku gane wannan ku daina ɗaurawa Allah lefi. Inji Sheikh ɗin.

Muke da lefi amma kowa yafi son lefinshi, Ya kamata Mutane mu gane mu dinga yiwa kanmu adalci. Ka ɗaurawa Allah lefi Mala'iku su rubuta. Kai yanzu in aka tambayeka lefin Allah ne ya zakace? Wannan lefin da ka ɗaurawa Allah ranar gobe Ƙiyama a kawo ka gaban Allah ace maka wannan lefin da ka ɗaurawa Allah lefin Allah ne? Mi zakace? Ya kamata baki yasan mi zai dinga faɗa.

Na'am bamu ce Allah (Swt) baya da hannu a cikin lamarin dake gudana ba. Amma shi Allah (Swt) akwai inda ya faɗa, ba zamuce ya kare kanshi ba. Allah (Swt) yake cewa: "Duk abunda kuka gani na Musiba ku kuka jawa kanku". To kai kuma kace Allah ne?

Sheikh ɗin ya ƙara da cewa: "Gwamnatin Najeriya ina haƙƙinmu"? Ya kamata Ku fito mana da haƙƙinmu. Haƙƙi nawa Gwamnati ta yafe maka? Ta yafe maka haƙƙin biyan wutar Nepa? Da takardunka na abunda hawa s**a ƙare sun yafe maka? To miyasa mu zamu yafe mata? Ya kamata mu yafe mata? Ko kawowa akayi aka raba mana komi da komi sai muce dasu ina sauran suke? Domin munsan basu kenan ba.

In akayi hanya zuwa garin mu, to wannan kuɗin bajeɗin barane ina na yanzu? Ko Bara bamu da haƙƙi a cikin ta? Don haka ya kamata Mutane su san mi zasu dinga ɗaurawa Allah (Swt). Yau da ruwan Sama akayi sai akayi Ambaliya duk sai ya game gari ya buɗe Gidaje ya shiga, sai a yi tamabya ya akayi ruwan nan ya shiga Gidaje? Sai akace Kwatocine s**a cike ko Kwalbatice tayi ƙaranci. Al haƙƙin waye ya yi su? Gwamnati. To in ba a yi ba fa? Suwa s**a rusawa Mutane Gidaje?

Daga ƙarshe ya yi kira ga Jama'a da su san mi bakunansu zasu dinga faɗa.

___Sheikh ɗin ya yi wannan maganar ne a ranar Lahadi ya yin gudanar da Tafsirin Alqur'ani mai girma na shekarar 1445H_2024M. Zama na 8 rana ta 7.

Rubutawa: 17/March/2024M.
Hassan Ɗan Sister Katsina ✍️

YAƊUWAR SHI'ANCI A NIJERIYA AL'AMARI NE IRIN NA ALLAH “Ba za mu iya cewa ko mu muke yada (Mazhabar Ahlulbaiti (AS) ba, w...
17/03/2024

YAƊUWAR SHI'ANCI A NIJERIYA AL'AMARI NE IRIN NA ALLAH

“Ba za mu iya cewa ko mu muke yada (Mazhabar Ahlulbaiti (AS) ba, wannan al'amari ne irin na Allah Ta'ala, wanda za ka ga cikin gajeren lokaci mutane hulululu sun fahimta.

“Saboda haka, yadda mutane suke bumbuntowa (ga Mazhabar Ahlulbaiti (AS), yana da wuyan gaske mu iya kayyadewa mu ce maka yanzu mu kaza ne. Sai dai mu ce maka muna faɗaɗa.

“Kuma fatanmu shi ne, insha Allahu nan gaba ba da jimawa ba, duk Musulmi a ƙasar nan, Shi'a zai zama.”

— Inji Jagora Shaikh Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), a yayin wata hirarsa da wani dan jarida daga Iran, a shekarar 2013.
* Cibiyar Wallafa

HUKUNCE-HUKUNCEN AZUMI (5)Daidai da Fatawowin Ayatullah Sayyid Khamene’i (H)ABUBUWAN DA SUKE KARYA AZUMIMas’ala ta 667:“...
06/03/2024

HUKUNCE-HUKUNCEN AZUMI (5)

Daidai da Fatawowin Ayatullah Sayyid Khamene’i (H)

ABUBUWAN DA SUKE KARYA AZUMI

Mas’ala ta 667:
“Abubuwan da suke karya Azumi guda goma (10) ne;

1&2- Ci da Sha, ta hanyar da aka saba ko ta wata hanyar daban.

3- Yin Jima’i da Halal ko da Haram, an yi ‘inzali’ ko ba a yi ba.

4- Fitar da Maniyi ta hanyar ‘Istimna’i’, ko kuma ta kowace hanya ta daban.

5- Yin karya ga Allah da ManzonSa da A’imma Ma’asumai (AS) a bisa Ihtiyadi na Wajibi.

6- Hadiye qura mai kauri, ko shan taba a bisa Ihtiyadi na Wajibi.

7- Nitsar da dukkan Kai a cikin ruwa a bisa Ihtiyadi na Wajibi.

8- Yin Allurar ruwa ko da kuwa saboda rashin lafiya ne, amma babu laifi da busasshe (kamar wanda ake turawa a dubura ko a gaba)

9- Yin Amai da gangan, ko da saboda lalura ne, amma yin Amai ba bisa rafkanuwa, ko kuma ba tare da zabin mutum ba, baya bata Azumi.

10- Ganganta zama cikin Janaba ko Haila ko Nifasi har Alfijir ya keto.”

MAS’ALOLI DANGANE DA ABUBUWAN DA SUKE KARYA AZUMI

Mas’ala ta 668:
“Abubuwan da suke bata azumi, wadanda aka lissafo su a Mas’alar ta da gabata, suna bata azumi ne kawai idan aka yi su da gangan, amma idan bisa mantuwa ne, ko bisa rafkanuwa, to ba su bata azumi, in banda Janaba. Da mutum zai Ci wani abu, ko ya Sha wani abu saboda ya manta cewa yana Azumi, to Azuminsa bai baci ba, duk daya ne kuma, azumin ya kasance na Wajibi ne ko kuma na Mustahabi.”

Wato in dai bisa mantuwa mutum ya aikata daya daga abubuwa goma din can da aka ambata, to azuminsa bai karye ba. In banda Jima’i, shi ko bisa mantuwa ko rafkanuwa aka yi shi yana iya bata azumi, kamar yadda bayanin hakan zai zo a rarrabe a nan gaba. Amma don mutum ya ci abinci ya koshi da rana, bisa mantuwar cewa yana azumi, to azuminsa bai baci ba, zai cigaba da abinsa, kuma ba sai ya sake azumin ba. Sai dai wajibi ne ya tofar da abin da ke bakinsa da zaran ya tuna a sadda yake kan ci.

Mas’ala ta 669:
“Idan mai Azumi ya aikata daya daga abubuwan da suke karya azumi bisa rafkanuwa, sannan ya sake aikata (abin da ke karya azumin) a karo na biyu (da gangan) bisa tunanin cewa ai dama Azuminsa ya riga ya baci tun farko, to (yanzu) Azuminsa ya baci.”

Ma’ana, na farko ya yi da mantuwa, bai san cewa hakan bai bata azuminsa ba, sai ya dauka cewa ai azuminsa ya riga ya baci tunda ya ci abu bisa mantuwa, don haka sai ya kara cin wani abu kawai a zimmar tunda azuminsa ya riga ya baci, to yanzu cigaba da aikata abin a karo na gaba ne ya bata azuminsa ba wai yin aikin a karo na farko bisa mantuwa ba.

Mas’ala ta 670:
“Idan mai Azumi ya fara kokonto (shakka) a kan shin ya aikata wani abu da ke bata azumi, ko bai aikata ba? Kamar da zai yi shakka akan shin ya hadiye wani abu daga ruwan da ya saka a bakinsa, ko bai hadiye ba? To a nan Azuminsa na nan Ingantacce (tunda shakka yake yi, bashi da tabbaci).”

Mas’ala ta 671:
“Bai halatta a sha ruwa (ko a aikata wani abu daga abubuwan da suke karya azumi ba) kafin a samu tabbacin shigowar dare, da mutum zai sha ruwa a wannan halin, to ramako da Kaffara sun wajjaba a kansa, ko da bai samu yakinin wanzuwar rana ba.”

Wato in har mutum bai da yakinin cewa rana ta fada, dare ya fara, to bai halatta ya sha ruwa ba. In har ba tare da samun tabbaci ba ya sha ruwa a yayin da yake shakku (kokono) kan dare ya shiga ko har yanzu da sauran rana, to wajibi ne a kansa ya rama azumin ranar, ya kuma yi Kaffara. Wajibi ne mutum ya sha ruwa ne a lokacin da yake da yakinin faduwar rana da farawan dare.

Mas’ala ta 672:
“Idan Mukallafi yana shakka a kan ketowar Alfijir (wato yana kokonto akan Alfijir ya fito, ko bai fito ba), to ba wajibi ba ne a kansa ya bincika don ya tabbatar kafin ya ci ko ya yi abin da ke karya azumi ba, sai dai kuma idan ya Ci din ba tare da binciken ba, sai daga baya ta bayyana masa ashe lokacin (da ya cin) Alfijir ya riga ya keto, to ya zama wajibi a kansa ya kame bakinsa a tsawon wannan yinin, sannan kuma ya rama Azumin daga baya, amma babu Kaffara a kansa.”

Saboda dama yana kokonto ne, tunda kokonto ne, to ba wajibi ne sai ya tashi ya bincika ba, amma idan ya bincika din ya fi masa, saboda zai samu tabbaci sai ya yi aiki da tabbacin. Saboda haka idan da zai zama yana da tabbacin Alfijir ya keto sai ya aikata abin da ke bata azumi, to wannan wajibi ne ya kame bakinsa a take, sannan ya rama azumin ranar, ya kuma yi kaffara. Amma idan yana shakka ne, wanda Malaman Fiqihu sun ce, shakka shi ne rabin tunanin mutum eh ne, rabi kuma a’a ne. To sai bai bincika ba, sai ya ci abinci, in daga baya ya gano lokacin Alfijir bai riga ya keto ba, shikenan azuminsa ya inganta, idan kuwa daga baya ya gane cewa ashe lokacin Alfijir ya fito, to ba shi da azumin ranar, sai ya rama shi amma ba tare da Kaffara ba, kuma wajibi ne ya kame daga aikata duk wani abu da ke bata azumi a tsawon wannan yinin.

Mas’ala ta 673:
“Idan (Mukallafi) ya zama yana shakka a kan Alfijir ya fito ko bai fito ba, sai ya bincika, sai ya tabbatar da cewa bai riga ya fito ba, sai ya ci abinci, sai kuma daga baya sabanin haka ya bayyana masa (wato ya bayyana masa ashe Alfijir din ya keto a lokacin), to Azuminsa ya inganta. Amma wannan a Azumin watan Ramadan ne kawai, amma a sauran Azumomin da ba na watan Ramadan ba, to azumi ya baci idan aka ci (ko aka aikata wani abu da ke bata azumi) a kowane hali.”

Wato in dai a cikin watan Ramadan, mutum ya fara shakka a kan Alfijir ya keto ko bai keto ba, sai ya bincika, sai ya tabbatar bai keto ba, sai ya ci abincinsa, sai daga baya kuma ta bayyana masa ashe a lokacin da ya bincika din nan ya keto fa, binciken ne bai bashi daidai ba. To tunda dai ya bincika shikenan, azuminsa na ranar ya inganta, ba sai ya rama ba. Sabanin da ace bai bincika ba, wanda aka yi bayanin hukuncinsa a sama.

To amma idan ba a azumin watan Ramadan ba ne, to ko a wane hali in ta tabbata wa mutum cewa ya ci abinci bayan ketowar Alfijir, ko ya bincika, ko bai bincika ba, ko ya samu yakini ko bai samu ba, to wannan azumin nashi babu shi, ya baci, ya sha ruwansa kawai.

Mas’ala ta 674:
“Ya halatta ga mata su yi amfani da magungunan da za su hana su, ko su jinkirta musu zuwan Al’adarsu (menstrual cycle) a cikin watan Ramadan, domin su Azumci watan bakidayansa ba tare da yankewa ba, matukar hakan bai lizimta musu cutarwa abin dogaro.”

Wato, in har an aminta da cewa, shan wani magani, ko amfani da shi don ya jinkirta zuwan jinin Al’ada, ko ma don ya hana shi zuwa gabadaya, ba zai cutar da mace irin cutarwar da za a lissafa shi a matsayin cutuwa mai illa ba, to babu matsala a shari’a ta yi amfani da wannan maganin, don ya dakatar mata da zuwan jini a watan Ramadan don ta yi azuminta lafiya ba tare da ta sha ko daya ba, in tana bukatar hakan. Amma in aka san cewa zai haifar da wani lalura ko illa abin dogaro, to bai halatta ba, saboda duk wani abu da zai jawowa mutum cutuwa a kan kansa, shari’a na kokarin kiyaye shi daga fadawa cikinsa.

Mas’ala ta 675:
“Idan mai azumi ya nitsar da dukkan Kansa a cikin ruwa da gangan, to bisa Ihtiyadi na Wajibi Azuminsa ya baci, ya zama wajibi a kansa ya rama Azumin wannan ranar. Idan kuma ya yi shakka a kan shin dukkan Kaina ya nitse a cikin ruwan ko bai nitse ba? To a nan (tunda kokonto yake yi, bai da tabbaci), Azuminsa ya inganta.”

Mas’ala ta 676:
“Idan mai azumi ya fada cikin ruwa ba tare da zabinsa ba (kamar idan wani ya tura shi a ciki, ko ya zame ya fada), sai kansa ya nitse a cikin ruwan, to azuminsa bai baci ba, sai dai kuma ya zama wajibi a gare shi ya gaggauta fitar da Kan. Irin wannan hukuncin ne ma yake a cikin cewa, da ace mutum zai manta yana Azumi, sai ya nitse a cikin ruwan (wato shima Azuminsa bai baci ba, tunda bisa mantuwa ne).”

Mas’ala ta 677:
“Ya zama wajibi a kan mai Azumi, a bisa Ihtiyadi na Wajibi, ya bar zukan Taba da dukkan nau’o’insa mabambanta, haka nan ma (ya bar) amfani da amfani da magunguna (Narcotics) wadanda ake amfani da su ta hanyar saka su a hanci ko wadanda ake saka su a karkashin harshe.”

Mas’ala ta 678:
“Idan mutum (mai azumi) ya yi gyatsa, sai abincin (da ke cikinsa) ya komo bakinsa, to bai halatta ya hadiye shi ba. Haka nan ma bai halatta (mai azumi) ya hadiye raguwan abincin da ke cikin bakinsa ba (kamar wanda ke jikin hakora), idan da zai hadiye shi ba tare da nufi ba, ba kuma tare da zabinsa ba, to Azuminsa bai baci ba, amma idan ya hadiye shi da gangan Azuminsa ya baci.”

Mas’ala ta 679:
“Idan mutum yana cikin cin abinci ya gano cewa Alfijir ya keto, ya zama masa wajibi ya fitar da ragowan abincin da ke cikin bakinsa, idan ya cigaba da ci, to Azuminsa ya baci.”

Wato in ya tofar da gaggawa, shikenan, sai ya kuskure baki ya cigaba da Azuminsa, kuma ya inganta. Amma idan yace tunda yana bakina, bari na karisa shi, to ya karya Azuminsa, kuma tunda da gangan ne ma ya yi hakan, to baya ga kame baki da zai yi na yinin, da ramako, sai ya kuma yi Kaffaran karya Azumin Ramadan da gangan.

* Akwai sauran Mas'aloli da suke bayani dangane da hukunce-hukuncen sauran abubuwan da ke karya azumi, wanda za mu cigaba a kansu insha Allah.

— Saifullahi M Kabir
25 Sha'aban 1445 (6/3/2024)
Whatsapp: 08062911212

Mutanen Zariya Na Caje Aljihun Gawarwakin Ƴan Shi'a Da Sojoji S**a Kashe Suna Kwashe Kuɗi, Waya Da Cire Wanduna Masu Kya...
05/03/2024

Mutanen Zariya Na Caje Aljihun Gawarwakin Ƴan Shi'a Da Sojoji S**a Kashe Suna Kwashe Kuɗi, Waya Da Cire Wanduna Masu Kyau A Gyallesu Gidan Sheikh Zakzaky!

—Bilya Hamza Dass

“Ku ji wannan shegen wai ruwa ya keso a bashi ya sha, to baza'a ba yar ba, ka jira Zakzaky yazo ya baka” kalmomin wani kenan yana bada amsa ga wani ɗan uwan da yake daf da barin wannan duniyar, sanadin harbin Sojojin Najeriya a gidan Sheikh Zakzaky, ranar da Sojojin s**a kawo harin ƙare dangi a watan Disambar shekarar 2015. Muhammad Sadik, daya halarci wajan kuma daga baya ya rayu da raunuka shi ne ya bani dukkan wannan labaran da na faɗa da kuma wanda zan faɗa nan gaba a rubutun! Sadik, yana cikin ƴan uwa musulmi Almajiran Sheikh Zakzaky da s**a tsira da munanan raunuka a harin Sojojin Najeriya a gidan Sheikh Zakzaky, kuma yana cikin ƴan uwan da s**a fara jinya a Asibitin Shika, wanda Sojoji su kaje su ƙarasa su amma Likitoci s**a hana faruwan hakan!

Dayawan wasu daga ƴan uwan mu da Sojojin Najeriya s**a kashe a gidan Sheikh Zakzaky wancan ranar a Gyallesu, wasu mutanen gari ko nace ƴan Iskan gari sune s**a ƙarasa su. Bayan Jami'an tsaron sunyi duk abinda za suyi cikin dare zuwa lokacin da gari ya waye sai kuma s**a gayyato Matasa, tantirai, ƴan Iska, ƴan shaye-shaye, kuma Musulmai, wasu cikin mu ba sa shaye-shaye amma suna da ra'ayin cewa Mallamai sunce musu ai ƴan Shi'a kafurai ne, domin akwai falala a kashe su! Da wannan fatawa ta miyagun Mallamai su kayi amfani su kayi abinda su kayi ga ƴan uwa na izigili da cutarwa! irin abubuwan da zan zayyana kaɗan a ciki yanzu.

Ku duba, ɗanuwan ka Musulmi ne a gaban ka lokacin da aka kashe, ko jinin jikin sa be gama bushewa ba, amma kana caje shi kana cire ƙudi, waya ko wando a jikin sa idan yana kyau ya cire domin ya siyar ya samu kuɗi! Wallahi irin wannan tsananin rashin Imani ban taɓa jin irin shi ba! Ko a film ko a littafi, in banda Labarin Karbala. Ko dabba aka yanka ba'a fara feɗe ta sai an tabbatar ta bar numfashi kafin! Duk mutumin da yayi wannan babu Imani ko kwayar zarra babu wallahi cikin zuciyar shi, kuma be cancanci a kira shi da sunan Musulmai ba b***e ace masa Musulmi me imani da Allah da Annabi Muhammadu ba. Wani abin mamaki sojojin da hukumomin da s**a sanya ayi abin suna kallo ana wannan rashin mutunci.

Suna bi kan dukkan gawar da ke wajan suna bincike ta su ɗauke waya, kudi, ko su cire mata Wando idan ya musu kyau, Sadik yace, wani yaga Singileti sabuwa jikin wani ɗan uwa da aka kashe, sai yake cewa, ku kalli Singiletin jikin wancan tayi kyau amma jini ya ɓata ta! sai wani cikin su yace, ka cire kaje ka wanke ta mana! Wani labari da naji daga wani wajan daban akace wani yaga wani Zobe a hannun wata gawa, yayi ta ƙoƙarin cirewa amma ya kasa sai kawai ya ɗauko wuka ya yanke yatsan ya cire zoben! Wani na roƙon su ba shi ruwa kada ya cika da kishin ruwa amma suna zagin shi suna hana shi!

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIN RAJI'UN!

Bari na tsaya haka! Labarin akwai tsayi akwai taɓa zuciya, na raba shi kaso 10 wannan fitar farko ne! Zanci gaba Insha Allah!

Bilya Hamza Dass
26/04/2021
..

AL'AMARIN SHAIKH ZAKZAKY AYA CE TA ALLAH TA'ALA DA YA KAMATA AL'UMMA TA FAHIMTA— Cibiyar Wallafa (www.cibiyarwallafa.org...
28/02/2024

AL'AMARIN SHAIKH ZAKZAKY AYA CE TA ALLAH TA'ALA DA YA KAMATA AL'UMMA TA FAHIMTA

— Cibiyar Wallafa (www.cibiyarwallafa.org)

Shekaru 9 da s**a shude, duniya ta shaidi mafi girman zalunci, irin wadda ba a taba ganin irinsa a kan wasu mutane a kaf fadin Nijeriya ba, inda sojojin da aka dauke su aiki domin kare al'ummar ƙasa, s**a dira a kan wasu gungun al'ummar ƙasar, fararen hula, kuma Musulmi da kisan kiyashi a Zariya.

Kisan-Kiyashin Zariya, wanda sojan Nijeriya s**a shafe kwanaki dare da yini suna kashe fararen hular Musulmi kusan mutum dubu, sannan gwamnatin Jihar Kaduna don ta rufawa sojin asiri, ta ba da fili a Mando, sojojin s**a haƙa s**a bizne duk ɗaruruwan mutanen da s**a kashe a ramin bai-ɗaya, ba a taɓa ganin irinsa ba a nahiyar Afirka ma bakidaya.

A nan ne s**a harbi Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) da mai dakinsa Malama Zeenah, s**a debe su jina-jina s**a tafi da su, bayan sun kashe musu 'ya'yan cikinsu uku a gaban idonsu, da almajiran Shaikh din kusan mutum dubu.

A tsakiyar watan Disamba 2015, 'yan kwanaki bayan sojojin sun yi wannan ta'addancin na kashe 'yan uwa Musulmi, sojin sun saki wasu hotuna da ke nuna Shaikh Zakzaky jina-jina, da fasasshen ido, jini ya lulluɓe farin gemunsa. Har ma s**a saki wani hoto da ke nuna shi a kan 'Wheel Barow' da nufin yi masa Izgili.

Al'ummar Arewa, musamman Hausawa, masu ra'ayin halascin kashe duk wanda ya saɓa da su a ra'ayi ko fahimtar addini, s**a rika murna da ganin wannan hoton, har ma s**a rika yaɗa shi, tare da nuna Shaikh Zakzaky baya raye. Tsawon watanni, kafin daga baya a watan Febrairun 2016 da 'yan uwan Shaikh din s**a bayar da tabbacin sun ganshi ido da ido, kuma s**a tabbatar da rayuwarsa, amma cikin jinya, a lokacin yana asibitin DSS da ke Abuja, wanda shi da matarsa s**a shafe watanni uku zuwa hudu a wajen.

Lokacin farko da jami'an tsaron DSS s**a fara bayyana Shaikh Zakzaky a 'Video' shi ne a watan Junairun 2018. A wannan lokacin, al'ummar duniya sun ganshi sanye da rawani, da Abaya, yana dogara sanda, a wuyansa akwai makarin da ke taimakawa wajen tallafa ma kansa.

Shehin Malamin, ya sha fadi tashin neman lafiya, duk da yana tsare, DSS bisa umurnin gwamnatin Buhari s**a rika wasa da lafiyarsa, har zuwa shekarar 2019, bayan sun baro da su daga Abuja sun kawo su Kaduna da nufin cigaba da tsarewa, sannan a wani lokaci da illar guban harsasan da ke jikin Shaikh Zakzaky s**a fara takura masa, a ranar 23/7/2019, DSS s**a yarda s**a kai Shaikh din asibitin National Ear Care Center, da ke Kaduna, don a yi gwaje-gwaje musamman akan harsasan da ke cikin kansa.

A wannan babban asibitin gwamnatin ne, s**a wa Shaikh Zakzaky hoton kansa, bayan lokaci, s**a fitar da rahoton hoton, inda s**a bayyana akwai Ɓaraguzan harsashi har guda 55 a jikin Shaikh Zakzaky a sassa daban-daban, kuma akwai kimanin 38 a kansa. Wanda hoton rahoton wannan binciken yana nan yana yawo a kafafen sadarwa har yanzu, da ma na 'scan' din. Hatta yadda aka yi 'scanning' din, daga farawa har aka gama, akwai 'Video' dinsa, wanda aka adana don tarihi.

Haka nan, lamarin idon Shaikh Zakzaky ma, bai buya wa al'ummar duniya ba, har ma wawayen al'ummar Hausawan Arewa, s**a riƙa yi masa izgili da cewa ya makance, ko mai ido daya. Saboda yadda bayan harbin da aka masa ido, kwayar idonsa ya fito, sai da aka mayar aka yi aiki, amma cikin ikon Allah ga kwarmin idon ana gani, amma idon baya aiki a wancan lokacin da suke izinin.

Yanzu bisa Hikima da Buwayar Allah Ta'ala, ya sa Shaikh Zakzaky ya kubuta daga hannun azzalumai, wanda wawayen Izgilallu sun rika izgilin cewa, ba zai fito ba har ya mutu. Bisa ikon Allah Ya sa Shaikh Zakzaky ya samu sauki daga cututtukan da suke damunsa, ciki kuma har da gubar 'lead' din da harsasan da aka harbe shi da su suke fitar masa a jiki. Allah Ta'ala Ya mayar masa da idonsa, da ganinsa, har ya zama in ka kalle shi kamar ba shi ne wannan da wawayen Arewa s**a rika ma izgilanci akan ido da lafiyar jikinsa ba.

To kuma duk wadannan abubuwan baiwa da Allah Ta'ala Ya wa Shaikh Zakzaky, bai taba nuna fariya da hakan ba, face tun bayan fitowarsa, komai yana cewa Allah Ta'ala ne Ya yi masa. Aikin Allah ne. Allah ne Ya ga damar Ya masa duk abin da ya masa. Allah ne Ya raya shi, Allah ne Ya dawo masa da lafiyarsa da ganinsa. Kuma Allah Mai iko ne akan komai.Da gaske ne, irin halin da Shaikh Zakzaky Ya shiga, in ba Ikon Allah ba, babu wanda zai shiga irin wannan halin kuma ya rayu. Amma tunda Allah Ta'ala ne mai raya wa, kuma ya ga damar ya raya shi, shikenan.

Ya ishi Aya gare mu, yadda sojojin nan s**a kashe mutum dubu a kokarinsu na su kai ga Shaikh Zakzaky, amma da s**a same shi, s**a bude masa wuta, s**a karya hannun hagunsa da kafar damansa da harsasai, s**a fasa idon hagunsa, da harsashi, s**a dauke shi jina-jina jini na zuba a jikinsa s**a tafi da shi, amma duk Allah bai nufi su kashe shi ba.

S**a tsare shi da tunanin ba ranar sakinsa, s**a rika kashe almajiransa da suke fitowa suna Muzaharar kira a sake shi, har s**a kashe kimamin mutum 200 daga magoya bayansa a tsakanin kwanakin tsare shi, amma a karshe Allah Ya kaddara fitowarsa da kubutarsa daga hannunsu suna kan mulkin ba tare da sun sauka ba. Sannan s**a hana shi samun isasshen kulawar likita, amma Allah Ya kaddara samun hakan bayan kubutarsa, ba tare da ya hallaka ko wani abu ya nakasa tare da shi ba.

Yana yin taron da ke tattaro dukkan almajiransa daga dukkan sassan ƙasar nan da ketare a cikin ƙaramar hukumar Zaria/Sabon Gari ta jihar Kaduna, abin da azzaluman mahukuntan ƙasar nan s**a masa ya zama kamar katin gayyata a gare shi na komawa babban birnin Tarayyar Nijeriya, wato Abuja, inda ya zama yanzu taron da ke hada duk almajiransa daga dukkan sassan ƙasar man da kewaye, a tsakiyar birnin Abuja yake gudanar da shi.

Duk wadannan wasu Ayoyi ne ababen lura ga masu hankali daga Allah Ta'ala, wadanda sun isa su nuna cewa lallai Allah Ta'ala yana tare da wannan bawan nasa, kuma yana dafa masa a cikin al'amuransa, kuma yana taimakonsa. Sannan kuma izgilin Izgilallu ba zai wa Da'awar da yake na kira zuwa ga komawa addini komai ba, kamar yadda bude wutan masu kisan kai, bai iya imma Da'awar ba.

Kiranmu ga 'yan uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) shi ne, kar a gajiya wajen yada Mazlumiyar Shaikh Zakzaky (H), kamar yadda Mazlumiyar Imam Husaini (AS) ta wanzu mana sakamakon kiyayeta da yada ta da aka rika yi a tsawon tarihi, wannan ma bai kamata mu yi sako-sako da kiyaye ta da yada ta ba. In kun lura tun yanzu makiya sun fara kokarin nuna kamar komai ma bai faru ba, kuma haka za su yi ta kokarin nunawa din har nan gaba; Azzalumai za su so su boye ɓarnar da s**a yi, tunda bai yi nasa ba, haka ma 'yan korensu za su yi kokarin zaluncin ya ɓace bat, saboda bai yi nasara ba, murnarsu ta koma ciki.

Muna rokon Allah Ta'ala Ya ƙara kariya da lafiya ga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), da iyalansa. Ya girmama matsayinsu Shahidanmu masu girma. Ya kara hakuri da juriya ga Iyalansu. Ya tsinewa makasansu albarka. Ya nuna mana lokacin tabbatar wannan addinin a wannan nahiyar karkashin Jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) Insha Allah.

— Cibiyar Wallafa Da Yada Ayyukan Shaikh Zakzaky (H)
17 Sha'aban 1445 (27/2/2024)
[email protected]

Address

GRA Layout
Katsina

Telephone

+2348036342932

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when VOICE of Sheikhs posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share


Other News & Media Websites in Katsina

Show All

You may also like