MEDIA Tudun-iya

MEDIA Tudun-iya Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from MEDIA Tudun-iya, Media/News Company, Funtua.

KO KUN SANGangamin   Ke Gudana Yanzu Haka A Banex Plaza Wuse Abuja.Matasa ne dauke da hotunan Sheikh Zakzaky damai dakin...
25/04/2022

KO KUN SAN

Gangamin Ke Gudana Yanzu Haka A Banex Plaza Wuse Abuja.

Matasa ne dauke da hotunan Sheikh Zakzaky damai dakinsa Malama Zeenah tare da hotuna masu dauke da rubuce rubucen , Allow Zakzaky To Travel Now!!! Masu gangamin na gabatar da taken kira ga azzalumar Gwamnatin Buhari ta APC kan ta gaggauta sakin Passport din Sheikh Zakzaky da Matarsa Malama Zeenah. Ga kadan daga hotunan gangamin dake gudana yanzu haka.

— Asperger
25/April/202

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIMYan uwa amajiran Sayyid Zakzaky (h) na garin Tudun-iya Funtua suna farin cikin gayyatar al'umm...
23/03/2022

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Yan uwa amajiran Sayyid Zakzaky (h) na garin Tudun-iya Funtua suna farin cikin gayyatar al'umma zuwa wajen bikin ranar haihuwar IMAM MAHADI (AF) da SAYYID ZAKZAKY (H)

Wanda zai gudana k**ar haka:
Ranar juma'a 25/03/2022

Muzahara bayan sallame sallar juma'a wadda za'a tayar da ita bakin Fudiyya

Wurin khatama: Filin makarantar tsakiya a nan cikin garin Tudun-iya

Akwai wasanni kala kala gami da fareti wanda matasa zasu gabatar a wurin tare da jawabin babban bako

Sanarwa daga kwamitin shirye shirye qarashin DA'IRAR TUDUN-IYA

Allah ya bada ikon zuwa amin

Media T/iya
23032022

ABS CHANNEL TVShafin harka islamiyyah karkashin Sayyid Zakzaky (h) don jin jawabin jagora kai tsaye. Kira na ga 'yan uwa...
24/02/2022

ABS CHANNEL TV
Shafin harka islamiyyah karkashin Sayyid Zakzaky (h) don jin jawabin jagora kai tsaye.

Kira na ga 'yan uwa ya k**ata mu yawaita shiga wannan shafi muna sauraron jawabin jagora (h) sannan mu Rika yin likes da subscribes don kara wa shafin armashi.

Yawan yan uwa da suke ta'ammuli da social media ya k**ata mu cika wannan shafin don samun abinda zai tsiratar damu duniya da lahira.adadin da na gani na likes da subscribes bai kai ko kusan abinda ya k**ata a gani ba.

12/02/2022

WATAN RAJAB:
FALALOLI NA AZUMOMIN WATAN RAJAB:

RANA TA (17)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai umurci Mala'iku su yi masa rakiya su na yi masa kirari har cikin Aljanna.

RANA TA (18)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai sa shi ya zamo na hannun daman Annabi Ibrahim (AS) a Aljanna.

RANA TA (19)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai gina masa gidan Bene na Lu'u lu'u da Yakutu a Aljanna.

RANA TA (20)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai ba shi lada k**ar ya bauta masa na tsawon shekaru Ashirin.

RANA TA (21)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai cece shi daga wuta a ranar Alkiyama.

RANA TA (22)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai sanya shi cikin waliyansa.

RANA TA (23)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai umurci Mala'iku su yi masa Albishir da Aljanna.

RANA TA (24)
Wanda ya yi a Azumi a wannan rana. Allah zai zo masa a kyakyawan Sifa.

RANA TA (25)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai zamo kaffarar shekara dari na zunubansa.

RANA TA (26)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai shiga Inuwar Al-arshi ranar da ba wata inuwa sai ita.

RANA TA (27)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah za ba shi ladar wanda ya yi Azumin wata sittin.

RANA TA (28)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. zai zamo kaffarar zunubin shekaru Saba'in a gare shi.

RANA TA (29)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai gafarta masa zunubansa.

RANA TA (30)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana duk abin da ya roki Allah a wannan shekara to zai ba shi. muddin ba halaka ba ne a gareshi.

A TAKAICE:
Wanda ba zai iya ribatar duk wadannan ranaku da Azumi ba. to akalla ya Azumci ranar farko. sai ranakun 13. 14. 15. wato fararen ranaku. Sai kuma ranar (27) da kuma ranar karshen watan. Wadannan ranaku su na da falala da daraja sosai. rashin yin Azumi a cikinsu Babbar asara ce. Don sanin cikakken falala na azumin kowace rana a watan Rajab. duba littafi "IKBAL FILA'AMAL" na Sayyid Ibn Dawus. 👏👏👏

YUSUF DAHIRU MUDARIS

12/02/2022

WATAN RAJAB:
FALALOLI NA AZUMOMIN WATAN RAJAB:

RANA TA (1)
Manzon Allah (S) ya ce "Wanda ya yi Azumi a ranar farko na watan Rajab Aljanna ta wajaba a gare shi"

RANA TA (2)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. zai samu ceton Annabawa a ranar Alkiyama.

RANA TA (3)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai sanya Hijabi na tsawon tafiyar shekaru (70) tsakaninsa da wuta.

RANA TA (4)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai kiyaye shi daga dukkanin bala'o'in shekarar.

RANA TA (5)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai tashe shi a filin Alkiyama fuskarsa ta na haske k**ar farin wata.

RANA TA (6)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai katange shi daga cutar da mahaifansa. da yanke zumunci ga 'yan'uwansa.

RANA TA (7)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai rufe masa kofofin wutar Jahannama guda bakwai. wato ba zai shige ta ba.

RANA TA (8)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai bude masa kofofin Aljanna guda (8) ya shiga ta inda yake so.

RANA TA (9)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai tashe shi a kabarinsa ya na kalmar Shahada. kuma zai shiga Aljanna ba tare da hisabi ba.

RANA TA (10)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai rubuta masa lada k**ar ya bauta masa na tsawon shekaru dubu.

RANA TA (11)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai fifita daraja da matsayin sa a ranar Alkiyama.

RANA TA SHA (12)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai tufatar da shi da wani tufafi a ranar Alkiyama wanda haskensa ya fi na rana

RANA TA (13)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai ciyar da shi launin abinci har kala dubu Saba'in a ranar Alkiyama.

RANA TA (14)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai ba shi wata kyauta wadda ido bai taba gainin irin ta ba.

RANA TA (15)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai tsayar da shi a wurin tsayawar Amintattun bayinsa a filin Alkiyama.

RANA TA (16)
Wanda ya yi Azumi a wannan rana. Allah zai dora shi akan wani abin hawa mai haske ya kai shi gidan Aljanna.

*KADAN  DAGA  FA'IDOJIN  YAWAN  SAURARON  ZANTUKAN  JAGORA (H).**1,  Za  ka  fahimci  manufar  kiran  Jagora  (H)  da  i...
12/02/2022

*KADAN DAGA FA'IDOJIN YAWAN SAURARON ZANTUKAN JAGORA (H).*

*1, Za ka fahimci manufar kiran Jagora (H) da inda Harkar tasa gaba.*

*2, Za kayi saurin fahimtar mataki da matsayar Jagora a al'amura masu rikirkitarwa.*

*3, A lokacin jarrabawa za kayi saurin fahimtar jarabawar da matakan dauka don cin jarabawar.*

*4, Ayayin Fitina zaka gane tudun muntsira, mafakar kaucewa duk Fitina.*

*5, Zaka samu kyakyawan Damfaruwa da Jagoran HARKA a fikra , ta yadda baza a iya maka kutsen fikirar da ta sabawa hadafin Gwagwarmaya ba.*

*Allah ya tabbatar damu bisa sahihiyar fikirar Jagora, Allamah Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).*

11/06/2021

SAYYIDA MA’ASUMA ‘YAR IMAM MUSAL KAZEEM (AS)

— Saifullahi M. Kabir

Ranar 1 ga watan Zulka’ada, rana ce ta farin ciki da murna ga muminai, saboda a cikinta ne aka haifi Karima, Jalila, Sayyida Fatima Ma’asuma ‘yar Imam Musal Kazeem (AS).

Wannan baiwar Allah mai girma, wacce a cikin ziyararta ake mata kirari da cewa: “’Yar waliyiyar Allah, ‘yar uwar waliyin Allah kuma innar Waliyin Allah.” Ta kasance ‘yar uwa shakikiya (wacce suke uwa daya uba daya) ga Imam Aliyu bin Musar Ridha (AS).

An haifeta ne a garin Madina, a shekara ta 173 bayan Hijira. Ta kasance mafificiya a cikin dukkan ‘ya’yan da Imam Kazeem ya Haifa baya ga Imam Ridha (AS). Ta taso a gidan Imamanci da Wulaya, ta rayu a tsakankanin Limaman shiriya tsarkaka. Kakanninta A’imma, Mahaifinta Imam, Wanta Imam, kuma ta zama Innar Imamai (AS).

Ta kasance daga cikin matan da s**a tsarkake Imaninsu. Tsarkakakkiya, ta taso ne bisa kulawar yayanta Imam Ridha (AS), sak**akon kulle mahaifinta Imam Musal Kazeem da azzalumin sarkin Banul Abbas mai suna Harun ya yi, wanda ya kai ga Shahadantar da shi a cikin wannan Kurkuku din.

Cikin lakubba da ake kiran Sayyida Fatima Ma’asuma, akwai Muhaddasa, Mubaraka, Abida da kuma Karimatu Ahlulbait (AS). Dabi’un wannan tsarkakakkiyar baiwar Allah din ya yi k**a sak da na kakarta Sayyida Fatima Azzahra (SA).

Wannan baiwar Allah din ta kasance wacce ta mori suna, a yayin da aka saka mata sunan Sayyida Zahara (S). Imamanmu masu girma sun muhimmantar da saka suna ‘Fatima’ ga ‘ya’yan da s**a haifa (mata), saboda suna ne na uwarsu, Sayyida Fatima ‘yar Manzon Allah (S).

Kulaini, ya kawo ruwaya a cikin Alkafiy, daga Salmanul Ja’afariy, yace; Na ji Baban Hasan (AS) yana cewa: “Talauci bata shiga gidan da a cikinsa akwai mai suna Muhammad ko Ahmad ko Ali ko Hasan ko Husaini ko Ja’afar ko Dalib ko Abdullahi, ko kuma sunan Fatima a cikin mata.” Dan haka lallai sunan Fatima a wajen iyalan Fatima da masoyanta, suna ne mai girman daraja. Kuma duk wacce Allah ya azurta da sunan abar girma

01/06/2021

Robbers enter a house, asks for all the money and valuables.
After they collect what they can, they give the man of the house a gun with instructions to shoot his wife or else he be shot himself. The man gets the gun, points it at his wife and hesitates.

He is thinking of what he has gone through in life with his wife and how she has suffered and sacrificed for him. He hands back the gun and says, “I am sorry I can’t do this…

“The boss of the robbers silently grabs the gun from him and passes it on to the wife with the same instruction. The wife gets the gun and without any single hesitation points to her husband’s head and pulls the trigger. But at last, the gun had no bullets in it. The robbers get their gun and walk out of the house laughing.

QUESTIONS FOR DISCUSSION

1. If you were the man in that house how would you react towards your wife?

2. If you were the wife, what explanation can you give to your husband!

3. If you were invited to bring peace between this couples, what advice would you give?

Drop your Comments & this should really be an interesting topic to discuss as counsellors.

SHARE THIS POST ON YOUR WALL & SEE THE KIND OF ANSWERS YOUR FRIENDS WILL BE DROPPING, YOU WILL BE SURPRISED..

19/05/2021

-Wake Bukatar Ganin Imam Ali (as) a Darensa Na Farko da aka Sanya shi a Cikin Kabari?.

-Ga Wata Sallah Sassauka da ake yi Duk Wanda Yayi Wannan Sallah Allah Yayi Alqawarin Cewa a Daren Farko da Mutum Ya shiga Qabarinsa Imam Ali (as) zai Kawo Masa Ziyara...:

Ga Yanda Sallar take:

-Mutum Zai yi Niyyar Wannan Sallah ne a Matsayin Amana tsakaninsa da Allah ta'ala Sai Ya Fara Sallar,

-Kuma Sallar Raka'a biyu ce, a Raka'ar Farko Fatiha da Inna'a'adaina kal kausar, Raka'a ta biyu Kuwa Fatiha da Izazulzilati idan Mutum Yazo Yin Qunuti Sai Ya Karanta inna'a'adaina a Matsayin Quntinka, Sai ka Kammala Sallar ka Shikkenan ka gama.

-Allah Yayi Alqawarin Duk Wanda Yayi Sallar Nan zai sa Imam Ali (as) Ya ziyarce shi a daren da Yaje Qabarinsa.

Muhammad Jiddah Nguru

24/04/2021

WURIDIN SURAR “INNA ANZALNAHU FI LAILATIL QADAR”
Don neman arziki da wadata

(1) Wuridi na farko shi ne a lizimci karatun surar kafa goma a kullum bayan an idar da sallar asubahi. Za a ga abin mamaki, daga Allah mai iko akan dukkan komi.
(2) Wuridi na biyu, shi ne a karanci surar kafa 360, domin neman biyan kowace irin bukata. Za a sami biyan bukatar da gaggawa.
(3) Amma domin neman yankewar talauci cikin gaggawa, ko biyan bashi, ko wani matsayi ko arziki da wadata, sai a karanci surar kafa 304. Da izinin Allah za a sami biyan bukata a cikin hamzari.An ruwaito daga Imam Ja’afar Assadiq (AS), ya ce: Duk wanda ya lizimci karatun surar, Allah zai buda masa kofofin arziki da wadata ta inda ya tsammata da ma ta inda bai tsammata ba.

05/12/2020

*LABARAN-LIBERTY NA YAU ALHAMIS 03/12/2020*

DOLE YASA SHUGABAN KASA ZAIJE MAJALISA

1)Shugaban Najeriya Buhari Ya Amsa Gayyata Da Majalisan kasa Tayi Mashi Dole Yazo Yayi Mata Bayani Akan Matsalan Tsaro:

2)) Gwamnoni Sunce Sojoji Bazasu Iya Kawo Tsaro A Najeriya Ba Dole A Kawo Sojojin Haya Daga Wata Kasa:

3))) Hanyan kaduna Abuja Ko Jiya Cikin Dare Yan Bindiga Dadi Sun Budewa Motocin Jama,a Wuta Sun Harharbi Jama,a:

4)))) Yan Najeriya Suna Cikin Mawuyacin hali Shugaban Najeriya Buhari Ya Yabawa Yan Najeriya Wajan Juriya Da Mawuyacin hali Da S**a Tsinci Kawukansu A Ciki:

5)))) Majalisan Jadtawa Sun Mikawa Buhari Bukatansu Guda Bakwa Ciki Kuwa Dole Buhari Ya Bincike Sojoji Akan Makudan Kudaden Da Ake Tura Masu Musamman Burutai Da Manyan Abokan Aikinsa:

6))))) Gwamnatin Buhari Batada Tausayi Inji Hajiya Naja,ana Kano Tace Saidai Akayi Mata Tsirara Akan Buhari Saboda Goyan Bayan Da Take Nunamashi Kafin Yaci Zabe:

7)))))) Yan Bindiga Sun Shiga Kasuwanin A Jahar Niger Sun Kashe Mutun Biyu:

8))))))) Gwamnatin Najeriya Tabukacin Temakon Sojoji Daga Kasan Sin-Chaina Domin Temakawa Sojojin Najeriya Wajan Yaki Da Ta,addancin A Najeriya:

9)))))))) Shugaban Sojojin Najeriya Yusuf Burutai Yace Harkan Ta,addancin A Najeriya Sai Yakai Shekara Ashirin(20) Masu Zuwa Ba,a Daina Yin Ta,addancin Ba A Najeriya:

10)))))))) Wasu Yan Bindiga Sunyi Garkuwa Da Wani Kansila A Jahar Ido Suna Neman Kudin Fansa Naira Miliyoyi Kafin Yasamu Yanci:

11))))))))))) Coronavirus Mutun Ashin Da Bakwa (27) A Jiya Laraba S**a Kamu Da Cutar Coronavirus A Fadin Najeriya:

12))))))))))) Wata Tsohun Minista Tabukacin Da Dole Abincika Kwakwalwar Shugaban Najeriya Buhari Domin Tana Ganin Kaman Yana Da Ciwan Kwakwalwa:

13)))))))))))) Yan Uwa Musulmai Almajiran Mallam Zakzaky-h- Sun Bukaci Da Gwamnatin Tarayya Najeriya Ta Girmama Umurni Da Babban Kotun Abuja Tabayar Na Sakin Mallam Zakzaky-h- Kotun Taba Da Umurni Biyan Su Diyya Da Kuma Ginamasu Sabon Gida A Dukkan Inda Shehin Malamin Yake Da Bukatan Zama:

14)))))))))))))) Mabiya Mallam Zakzaky-h- A Fadin Najeriya Ciki Kuwa Har Da Babban Birnin Tarayyan Najeriya Abuja Sun cigaba Da Gudanar Jerin Gwano Suna Kira Da Gwamnatin Tarayya Da Saki Shehin Malamin Domin Cigaba Tsare Shehin Malamin Zalinci Ne, Mabiyan Sunce Zasu Cigaba Da Gudanar Da Jerin Gwano Suna Cigaba Da Kira Da Asaki Shehin Malamin A Nan Birnin Tarayyan Najeriya Abuja

*_Baban hydar zariya_*
_*Liberty Media Action reporter Abuja-Nigeria*_

AN SABUNTA KIRAN A SAKI SHEIKH ZAKZAKY A DA'IRAR KADUNA...Kaduna Press0011 A yau 23/11/2020 misalin 3:00pm, daruruwa yan...
23/11/2020

AN SABUNTA KIRAN A SAKI SHEIKH ZAKZAKY A DA'IRAR KADUNA...

Kaduna Press0011

A yau 23/11/2020 misalin 3:00pm,
daruruwa yan'uwa Almajiran Sheikh Zakzaky, sun fitowa kan titin Ahmadu bello way domin cigaba da yin kira ga gwamnatin Buhari da ta gaggauta sakin jagoran harkar musulunci a najeriya Sheikh Ibraheem Zakzaky da mai dakin sa, wanda da take cigaba da tsarewa tun bayan harin da sojojin Najeriya su ka kai a a garin zaria a shekar 2015, ba tare da laifin komai ba.

Almajiran Sheikh Zakzaky sun tafi cikin tsari tare da rera wake, da kiraye kiraye a sake shi. In da a kayi tafiya mai tsawo Sannan a ka kashe muzahran.

Yanzu haka dai Sheikh Zakzaky (H) yana gidan kurku a nan garin Kaduna, tare da iyalansa, duniya na ta Kira da a sakeshi, amma wannan gwamnatin tana nuna halin ko in kula.

Anyi Muzaharar lafiya an tashi lafiya.

Kaduna Press0011

WANI ABU DA BAKU SANI BA GAME DA RAYUWAR MUTANE A ZAMFARA.Aliyu Samba Na ziyarci wani kauye dake karamar hukumar Anka ta...
23/11/2020

WANI ABU DA BAKU SANI BA GAME DA RAYUWAR MUTANE A ZAMFARA.

Aliyu Samba

Na ziyarci wani kauye dake karamar hukumar Anka ta jihar Zamfara da ake kira Bagega, kauye ne da yake da adadi mai yawa na yara kanana da tsofaffi masu shekaru. A tattaunawar mu da sashen mazauna garin, sun bayyana mana irin matsanancin hali da suke ciki sak**akon yan bindiga da suke makotaka dasu, s**an shigo kusan kullum su dauki mutane mazan su da matan su suyi daji dasu. Mafi munin lamarin shine, idan s**a tafi da su ba kudi suke nema ba, fyade suke wa mazan su da matansu. Idan wani ko wata yayi gardama sai su kashe su.

Yaran su kanana suna fama da wata iriyar cuta da take sauya musu halitta, kuma binciken mu ya nuna cewa hakan ya faru ne sak**akon abinda ake cewa "Lead Poison" wanda yake kassara sassa jikin dan adam har yayi silar mutuwar sa. A kauyen har ka fita bazaka samu jami'i guda daya ba na tsaro, bazaka samu wani abu na cigaba ba daga "social amenities", babu ruwa, babu hanya, babu asibiti babu makarantu.

Gwamnatin Zamfara da gwamnatin tarayya sun gaza matuka akan al'ummar wannan yanki, sun gaza wajen tsare rayukansu da lafiyarsu. Akwai tsohuwa da ta doshi shekaru 60, a bayanan ta take cewa sanda aka sace su aka kaisu, yan bindigar suna zabar matan da zasu yiwa fyade, wani yaro da bai wuce 25 ba yace shi ita yake so, harda cewa wai tsohuwa tafi ****. Cikin kwalla take sheda mana wannan, bayan ita akwai wata da aka harba a mazaunan ta saboda taki yarda ta kusance wanda yake nufin hakan akanta. Lamarin yayi tsanani yayi tsamari, har takai ba kowa zaka cewa zaka je Bagega ba ya yarda kaje, don sunan wajen dead zone kawai a takaice.

Shin babu abinda za a yi kenan dan cetan rayukan mutanen wannan kauye, babu abinda gwamnati zatayi dan gyara wannan barna?


©Aliyu Samba
23rd November 2020

بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صلى على محمد وآل محمد وعجل فرجهم
25/09/2020

بسم الله الرحمن الرحيم
اللهم صلى على محمد وآل محمد وعجل فرجهم

Address

Funtua

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MEDIA Tudun-iya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share


Other Media/News Companies in Funtua

Show All