30/04/2024
ABIN ALHERI: Shugaban Karamar Hukuma Ya Gina Asibiti Mai Daukar Gadajen Majinyata 60 A Jihar Katsina
Hon. Dr. Habibu Abdulkadir Shugaban Karamar Hukumar Musawa Jihar Katsina, Ya Shimfida Karamin Asibiti Mai Daukar Gadajen Majinyata Sittin 60 A Garin 'Yar-'Kirgi Dake Karamar Hukumar Musawa, A Kokarinshi Na Ganin Ya Inganta Harkar Lapiya A Karamar Hukumarsa.
Kamar Yadda Wakilinmu Jaridar Karaduwa Post, Ya Gano Mana, Shugaban Karamar Hukumar Musawa, Yana Daya Daga Cikin, Shuwagabannin Da S**a Shimfida Ayyukan Alkhairi Raya Kasa Masu Tarin Yawa A Jagorancinshi Na Shekara Biyu,
Wakilin Mu Ya Labarta Mana Akwai Wasu Ayyukan Raya Kasa Masu Tarin Tawa Da Ya Aiwatar Kamar:-
(1) Ya Gina Asibiti A Yar Kirgi, Gingin Ward
(2) Ya Gyara Asibitin Yar-Awala Kurkujan (A) Ward
(3) Ya Gina Hanyar Ruwa Mai Tsayin Gaske A Marabar Musawa, Kurkujan (B) Ward
(4) Yayi Salaf Garin Kurkujan, Kukujan (A) Ward.
(5) Yayi Hanyar Ruwa Mai Tsayin Gaske A Garin Mangafi, Gingin Ward
(6) Yayi Hanyar Ruwa A Tabani/Yar-Raddau Ward
(7) Yayi Salaf A Unguwar Chakaro, Gingin Ward
(7) Yayi Salaf A Garin Kurkujan, Kurkujan (A) Ward
(8) Ya Gyara Kwata Dake A Kasuwar Garin Musawa, Musawa (A) Ward
Wadanan Kadan Kenan Daga Cikin Ayyukan Alkhairin Da Ya Shimfidawa Al'ummarsa Wadanda Maku Kawo Maku A Karon Farko, Zamu Kawo Maku Wasu Anan Gaba.
Dafatan Allah Yayi Mashi Jagora, Allah Yasaka Mashi Da Alkhairi Ameen
~Karaduwa Post