NorthBlaze Hausa

NorthBlaze Hausa Labarai da rahotanni da dumi duminsu tare da sauran shirye shirye masu kayatarwa. Ku biyo shafinmu d

Dumi Dumi:Shugaban kasa Muhammad Buhari yakai ziyarar wucen gadi jihar katsina. Shugaban yayi tafiyar ne a jiya Juma'a W...
12/12/2020

Dumi Dumi:

Shugaban kasa Muhammad Buhari yakai ziyarar wucen gadi jihar katsina. Shugaban yayi tafiyar ne a jiya Juma'a Wanda rabonsa da Jihar nasa tun watar December shekarar 2019. Ana sa ran shugaban zaiyi akalla sati daya a Jihar tasa ta katsina.

An Hallaka Mutane 16 Akan Hanyar LegasKimanin mutane 16 wanda duk matasa ne s**a rasa rayukan su sak**akon harbin tayar ...
09/12/2020

An Hallaka Mutane 16 Akan Hanyar Legas

Kimanin mutane 16 wanda duk matasa ne s**a rasa rayukan su sak**akon harbin tayar motar su da akayi a hanyar su ta zuwa legas domin gudanarda sanaoin su.

Matasa da yan asalin karamar hukumar Danbata ne dake jahar Kano sun nufi legas dinne domin komawa bakin aikin su yayin da alamarin ya ritsa dasu.

Wannan bashi ne karon farko da irin wannan abu yake faruwa a manyan hanyoyi Najeriya ba. Don ko a makon da ya gabata irin wananan abu ya faru a kaduna da kuma hanyar Abuja , inda mutane da dama s**a rasa rayukan su. Amma dai har yanzu gwamnati bata dauki wani mataki maganin wannan bata garin masu tsare mutane suyi garkuwa dasu ba.

01/12/2020

BUƊAƊƊIYAR WASIƘA GA HON. PANTAMI

Saƙon mai sauƙin fahimta ne matuƙar ka kasance Malami na Allah, mai kuma tsoron Allahn.

Ba kuma tsayi ne da shi ba, don ba tashin-tashina zanyi maka ba kasancewar ƙarancin lokacin da wasu al'amuran ke tsimayin ɗaukina.

Kafin shigar ka cikin ƙunshin wannan Gwabnatin tun a wa'adi na farko, a baya ka kasance Malamin addinin musuluncin da ɗumbin musulmi ke tasirantuwa da lafuzanka, musamman waƴanda s**a jiɓinci s**ar Gwabnatin kan yawaitar salwantar rayukan al'umma. Wannan ina batu ne ba tare da na sanyo irin ƙaruwar da ake da kai ba ta hanyar sauraron karatuttukan ka a kafafen sadarwa. Dalilin kenan da yasa ka shahara har kayi sunan da nan da nan kowa ya sanka yake kuma iya shaida muryarka. Muryar da a yau ita ce ta zamanto abar zargi da munafunci a gurin mafi ɗumbin Musulman da suke da hankali.

Hon. (SHEIKH) Pantami, yana da kyau ace a matsayin ka na malami ka fi kowa sanin alamomin munafuki da s**a zo a cikin Hadisin Masoyin Mu (SAW).

A ranar da ta kasance ranar da majalisa za ta tantance ka, ka bayyanawa majalisa cewa kana da dabarun hanyoyin zamani bisa ma'aunin kimiyya da fasaha da za ta taimaka wajen ganin an bi sawun duk wani ɗan ta'adda, ko nace wasu Ƴan ta'adda. Amma har yanzu da kake kan kujerar MINISTA mun kasa ganin cikar wannan batun naka, wanda kai da kanka kan furta shi.

Baya ga haka, kai ka furta cewa za a rufe duk layukan wayar da akayi rijistarsu da sunan mutum ɗaya, matuƙar s**a haura guda uku. Amma a zahiri batu kuma mafi inganci har yanzu akwai irin waƴannan layukan da suke amfani, ba a rufe su ba. Ƙarawa ma, har gobe ana siyar da sabon layin waya mai rijista akansa.

Tun zamowarka MINISTA, ni dai ban ga wani sauyi da zai sanya a bambanta ka da sauran takwarorinka wajen ƙarya da yaudara ba. Domin dai har gobe ana samun matsalar Network. Kamfaninnikan waya suna satarwa jama'a kuɗin credit. Data har gobe akwai ta banza mara amfani, wacce za ka siya, amma har ta ƙare baka mori rabinta ba. Masu amfani da Glo shaida ne akan hakan.

A matsayinka na Malamin addini, dan Allah meye hukuncin mutum irin ka?

A baya kayi Kuka, kayi alƙunutu, ka sharce majina, duk don ana kashe mutane. Sai gashi kisan da ake na yanzu ya zarce na bayan, amma kuma ba muji gunjin ka ba.

Kai da kanka ka taɓa bayar da labarin irin yadda masu mulki da masu muƙamai ke sauka daga matsayin su yayin da duk s**a gaza gudanar da amanar al'umma. Amma sai ga shi ka tsinci kanka tsamo-tsamo cikin irin labaran naka, amma kuma kayi gum k**ar baka san me ke faruwa ba.

Na rantse da Allah, da waƴancan kalaman naka na baya akan Gwabnatin da ta gabata, wallahi baka da dalili na kusa ko na nesa, ko wata hujjar ci gaba da kasancewa cikin wannan Gwabnatin matuƙar da gaske kai na Allah ne ba mai fuska biyu ba.

Dan haka a shawarce cikin girmamawa, kawai ka ajiye muƙaminka na MINISTA saboda gazawarka ga cika alƙawarin da kai ka ɗauka da kanka. Muddin ba haka ba, wallahi girman ka da girman maluntarka duk sai ka rasa su. Kafin kuma kaje ka haɗu da Allah da Annabinsa Muhammadu (SAW).

Ƙaunarka nake, shi yasa na baka wannan shawarar.

©️ Na Ƴar Talla.

Rahotanni sun tabbatar wa majiyar mu cewa sanannen dan wasan kwallon kafa ta duniya wato Christiano Ronaldo ya kamu da c...
13/10/2020

Rahotanni sun tabbatar wa majiyar mu cewa sanannen dan wasan kwallon kafa ta duniya wato Christiano Ronaldo ya kamu da cutar corona virus wanda ake kira da Covid19

07/10/2020

Sabon Sarkin Zazzau Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli ya shiga fada inda yake kabar gaisuwar jamaa.

Da duminsa: Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli ya tabbata sabon Sarkin ZazzauGwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, ya...
07/10/2020

Da duminsa: Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli ya tabbata sabon Sarkin Zazzau

Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, ya bayyana sabon Sarkin Zazzau

K**ar yadda wallafarsa ta shafinsa na Twitter ya bayyana, Ahmed Nuhu Bamalli ne sabon Sarkin

- Ambasadan ya maye gurbin Marigayi Dakta Shehu Idris, wanda ya rasu a ranar 20 ga watan Satumba

Labari da duminsa da ke zuwa wa Legit.ng shine sanarwar gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai na sabon Sarkin Zazzau.

K**ar yadda Gwamnan jihar Kaduna ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya bayyana Ahmed Nuhu Bamalli a matsayin Sarkin Zazzau na 19.
Ya gaji marigayi mai martaba, Alhaji Dakta Shehu Idris wanda ya rasu a ranar Lahadi, 20 ga watan Satumban 2020 bayan kwashe shekaru 45 da yayi a karagar mulkin.

Yariman Zazzau Munir Ja'afaru ya yi martani game da naɗin sabon sarki Ahmed Nuhu BamalliMohammed Munir Ja'afaru, Yariman...
07/10/2020

Yariman Zazzau Munir Ja'afaru ya yi martani game da naɗin sabon sarki Ahmed Nuhu Bamalli

Mohammed Munir Ja'afaru, Yariman Zazzau ya taya sabon sarki Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli murna
Yariman na Zazzau da ke cikin masu neman sarautar yace ya amince da nadin Bamalli a matsayin ikon Allah

- Ya mika godiya ga magoya bayansa tare da addu'ar Allah SWT ya yi wa sabon sarki jagora

Yariman Zazzau Mohammed Munir Ja'afaru ya taya Ahmed Nuhu Bamalli murna bisa naɗin da aka masa matsayin sabon sarkin Zazzau.

A ranar Laraba 7 ga watan Oktoban 2020 ne Gwamna Nasiru El-Rufai ya amince da nadin Ahmed Bamalli a matsayin sabon sarki don maye gurbin Dr. Shehu Idris da ya rasu a ranar 20 ga watan Satumba.

Da ya ke martani kan naɗin cikin sanarwar da ya fitar a ranar Laraba, Yariman Zazzau wadda ke cikin masu neman sarautar Zazzau ya amince da naɗin Bamalli a matsayin ƙaɗdara ta Allah.

Yau Najeriya ta cika shekara 60 da samun yancin kai daga turawan mulki mallaka. Gidan jarida Northblaze media na yiwa da...
01/10/2020

Yau Najeriya ta cika shekara 60 da samun yancin kai daga turawan mulki mallaka. Gidan jarida Northblaze media na yiwa daukacin yan Najeriya murna zagayowar ranar yancin.

21/09/2020
Wani Hatsarin Mota Da Ya Afku Yau Yayi Sanadiya Mutuwar Mata Da Mijin Ta Da Yayan Su Guda UkuMiji wanda aka aiyana sunan...
21/09/2020

Wani Hatsarin Mota Da Ya Afku Yau Yayi Sanadiya Mutuwar Mata Da Mijin Ta Da Yayan Su Guda Uku

Miji wanda aka aiyana sunan da Abubakar Isa Birnin Kudu tare matar sa da yayansa uku sun gamu da ajalinsu ne sak**akon hadari motar dasu kayi.

Allah yayi musu rahama!

PDP Ta Lashe Zaben Gwamnan Jahar EdoSak**akon zaben gwamna daya gudana jiya a jihar Edo ya nuna cewa jamiyar PDP tare da...
20/09/2020

PDP Ta Lashe Zaben Gwamnan Jahar Edo

Sak**akon zaben gwamna daya gudana jiya a jihar Edo ya nuna cewa jamiyar PDP tare dantakarar ta Mista Godwin Obasaki ne s**a samu nasarar cinye zaben da rinjaye mai yawa.Hukumar zabe ce ta kasa ta aiyana hakan a garin Benin.

Dan takarar Jamiyar APC fasto Osagie ya samu kuriu 226,619 yayi da abokin karawar tasa na jamiyar PDP Godwin Obasaki ya samu kuriu 307,955.

Tuni dai hukumar zabe ta kasa INEC ta aiyana mista Godwin Obasaki a matsayin zabenbe Gwamnan jahar Edo a karo na biyu bisa ciki sharudan ta.

Allah yayiwa mai martaba sarki Zazzau Alhaji Shehu Idris rasuwa yau a garin Kaduna. Zaayi jana'izar sa da misalin karfe ...
20/09/2020

Allah yayiwa mai martaba sarki Zazzau Alhaji Shehu Idris rasuwa yau a garin Kaduna. Zaayi jana'izar sa da misalin karfe 5 na yamma a garin Zaria.

Yan Bindiga Sun Kai Hari Garin KagaraWasu yan bindiga daba a tabbatar da ko suwaye ba sun kai hari garin Kagara dake kar...
02/09/2020

Yan Bindiga Sun Kai Hari Garin Kagara

Wasu yan bindiga daba a tabbatar da ko suwaye ba sun kai hari garin Kagara dake karamar hukumar Rafi a jahar Neja.

Majiyar mu ta tabbatar da cewa maharan dai sun shiga garin ne aka babura kimani 30 tare da manya bindigogi a hannayen su.

lamarin daya faru ne yau da yamma inda s**a shiga cikin banki tare da kwashe kudade daba a san adadin su ba.

Sai dai yan bindigar sun samu tirjiya daga wasu mazauna garin amma saboda suna dauke da manyan mak**ai basu samu nasara ba.

An Sake Kara Kudin Man fetur A NajeriyaWata sanarwa data fito daga kafanin kasuwanci, dilancin da kyade farashin man fet...
02/09/2020

An Sake Kara Kudin Man fetur A Najeriya

Wata sanarwa data fito daga kafanin kasuwanci, dilancin da kyade farashin man fetur na kasa PPMC ta tabbatar da karin kudin man daga N148 zuwa N151 kowace lita.

Sanarwa mai dauke da sa hannun manajan deport din Ibadan mista D.O. Abalaka tace farashin zai fara aiki ne a yau 2 ga watan satumba.

27/08/2020

Tirkashi: 'Yan sandan Najeriya sun bankawa wani matashi harsashi kan ya yiwa wata karamar yarinya ciki

Yan sandan sun k**a shi da laifin yiwa wata yarinya cikin shege, inda s**a biyo shi har gidan mahaifinsa s**a harbe shi a kafa

- Daga baya 'yan sandan sun dauke shi cikin jini sun wuce da shi zuwa wani asibiti

Wani matashi mai suna, Ledisi Kote, yana kwance yana fama da kanshi a wani asibiti, bayan wasu jami'an 'yan sanda na jihar Ribas sun harbe shi a kafa sak**akon wata yarinya da ya yiwa cikin shege.

Majiuarmu ta ruwaito cewa wasu jami'an 'yan sanda dake aiki a Kpor cikin karamar hukumar Gokana a jihar, a ranar Juma'a 21 ga watan Agusta, 2020, sun shiga gidan mahaifin Ledisi dake K. Dere da misalin karfe 7 na safe, inda s**a bukaci ganin matashin dan shekara 19.

An ruwaito cewa 'yan sandan sun shiga dakin Ledisi, s**a fito dashi s**a harbe shi a kafa.

Wani mai kare hakkin dan Adam, Tuka Loanyie, wanda ya wallafa rubutu game da Ledisi a facebook, ya bayyana cewa 'yan sandan, wadanda s**a dauki yaron bayan sun harbe shi sun ajiye shi a wani asibiti a cikin yankin.

Loanyie, wanda ya bukaci abi hakkin matashin, ya bayyana cewa akwai yiwuwar sai an yiwa Ledisi aiki har kusan sau uku a kafa kafin ya samu ya cigaba da tafiya.

Gidan Jarida NorthBlaze Hausa Na Yiwa Daukacin Masu Saurarenmu A Duk Inda Suke A Fadin Duniya, Murna Bikin Ranar Hausa K...
26/08/2020

Gidan Jarida NorthBlaze Hausa Na Yiwa Daukacin Masu Saurarenmu A Duk Inda Suke A Fadin Duniya, Murna Bikin Ranar Hausa Karo Na Shida.

Ko shin masu Bibiyar Mu Zaku Iya Fada Mana Abun Da Yake Burge Ku A Yaren Hausa.

Yau Ce Ranar Hausa Ta DuniyaShekaru shida kenan da aiyyana wannan Rana ta 6 ga watan Agusta a matsayin ranar Hausa.Wanna...
26/08/2020

Yau Ce Ranar Hausa Ta Duniya

Shekaru shida kenan da aiyyana wannan Rana ta 6 ga watan Agusta a matsayin ranar Hausa.

Wannan rana an samar da ita ne domin tunawa tare da karfafa yaren hausa da al'adun sa a duniya bakin daya.

A shekarun bayan bikin ranar Hausa a na gudanar dashi ne a kafafen yada zumunta na zamani kafin bisani ya zamu gama gari.

Yanxu haka har takai a na shiriya taruruka domin Ranar a jahohi, makarantun da kuma kasashen da hausawa suke.

Wannan rana ta 6 ga watan Agusta tana da muhimmanci a gun kowanne bahaushe a duk in da yake a fadin duniyar nan.

Buhari Ya Nada Tsohon Dan Wasan Kwallo Kafa Ta Kasa Daniel Omokachi A Matsayin Mai Ba shi Shawara Akan Harkar Kwallon Ka...
20/08/2020

Buhari Ya Nada Tsohon Dan Wasan Kwallo Kafa Ta Kasa Daniel Omokachi A Matsayin Mai Ba shi Shawara Akan Harkar Kwallon Kafa.

Kimanin Mutum 30 Ne Aka K**a Da Yin Lalata Da Wata Yarinyar Yar Shekara 16 A Kasar Isra'ilaHukumar yan sandan isra'ila t...
20/08/2020

Kimanin Mutum 30 Ne Aka K**a Da Yin Lalata Da Wata Yarinyar Yar Shekara 16 A Kasar Isra'ila

Hukumar yan sandan isra'ila ta tabbatar da furuwar wannan lamarin, inda tace bincike ya tabbatar da cewa mutum 30 su kayi lalata da yarinyar yarin data bugu a wani otal.

Yan sandar kasar sun ce izuwa yanzu sun k**a mutane biyu da'ake zargin na daga cikin wanda s**a aikata wannan taasar.

Daya daga cikin wanda su kayi wannan aiki, ya tabbatar wa majiyar mu cewa yayi lalata da yarinyar amma bisa sahalewar ta. Yace ya wancin wanda su kayi wannan aiki basu san juna ba.

Hukumar otal din tace yarinyar bata daga cikin wanda suke k**a daki a wajen, sai dai tazo wajen ne ita da kawayeta don shakatawa.

Shugaban kasar israila Benjamin Natayahu yayi Allah wadai da wannan abin inda ya bukaci a zurfafa bincike don gano wanda s**a yi wannan aika aikar.

Ganduje Ya Aiyana Ranar Alhamis A Matsayin Ranar Hutun Sabuwar Shekarar Musulinci.Gwamnatin Kano ta bayyana gobe Alhamis...
19/08/2020

Ganduje Ya Aiyana Ranar Alhamis A Matsayin Ranar Hutun Sabuwar Shekarar Musulinci.

Gwamnatin Kano ta bayyana gobe Alhamis a matsayin ranar hutun sabuwar shekarar musulinci ta 1442 bayan hijirar Annabi Muhammad SWA daga Makka zuwa Madina.

Ganduje yayi kira ga allummar jihar da suyi amfani da wannan muhimmiyar ranar domin tunawa da aiyukan da s**a gabatar a shekarar da ake bakwana da ita, tare da yiwa jahar Kano da kasa baki daya adduar zaman lafiya da cigaba mai dorewa.

Bayan dukana, tsirara yake min a t**i - Matar aure mai bukatar sakiWata malamar makaranta mai suna Iyabo Amusan a ranar ...
07/08/2020

Bayan dukana, tsirara yake min a t**i - Matar aure mai bukatar saki

Wata malamar makaranta mai suna Iyabo Amusan a ranar Alhamis, ta garzaya gaban wata kotun gwargajiya da ke Mapo inda ta bukaci alkali da ya raba ta da mijinta saboda tsananin fushinsa.

Wata malamar makaranta mai suna Iyabo Amusan a ranar Alhamis, ta garzaya gaban wata kotun gwargajiya da ke Mapo inda ta bukaci alkali da ya raba ta da mijinta saboda tsananin fushinsa.

K**ar yadda Iyabo ta sanar, ta ce ta amince da barin 'ya'yan a hannun Joseph amma in har za ta rabu da shi tare da samun kariya a rayuwarta.

"Joseph ya saba bata min suna tare da kirana macuciya.

"Mai shari'a, ban san me yasa Joseph ya yanke hukuncin tozarta ni da ci min mutunci ba. A kowacce rana, rigima ta daban ce a gida na.

"Duk lokacin da ya dukeni, yana min tsirara. Yana zargina da mallakar kwalin bogi wanda na samu aiki da shi.

"Mummunan kudirin Joseph a kaina shine ganin bayana. Ya taba sassara ni da adda inda nayi doguwar jinya a asibiti.

"Duk da haka, baya bani abinci tare da 'ya'yana. Ina biyan haya da kaina," Iyabo tace.

Joseph, madakin mace, ya amince da bukatar sakin amma ya musanta dukkan zargin da ake masa.

07/08/2020

You can see how the North is beautiful with it culture.

Arewa gwanin ban sha'awa idan ba'a yada al'adu ba.

Yajin aikin da mu ka shiga zai fara daga ranar da aka bude jami'o'i' - NASU da SSANUWani kwamitin hadin gwuiwa (JAC) tsa...
07/08/2020

Yajin aikin da mu ka shiga zai fara daga ranar da aka bude jami'o'i' - NASU da SSANU

Wani kwamitin hadin gwuiwa (JAC) tsakanin kungiyar kananan ma'aikatan jami'o'i (NASU) da kungiyar manyan malaman jami'o'i (SSANU) ya sanar da shigarsu yajin aikin sai baba ta gani daga ranar da aka bude makarantu.

Shugaban kungiyar SSANU ta kasa, kwamred Samson Ugwoke, ne ya sanar da hakan yayin ganawa da manema labarai da yammacin ranar Alhamis bayan kammala taron JAC a Abuja.

Ya bayyana cewa NASU da SSANU sun yanke shawarar shiga yajin aiki sak**akon fuskantar matsin lamba daga wurin shugabannin kungiyoyin.

"Mun shiga yajin aiki sai baba ta gani wanda zai fara daga ranar da gwamnati ta amince a bude makarantu bayan janye dokar kulle da aka saka sak**akon barkewar annobar korona.



"Kungiyoyinmu sun kasance ma su juriya da hakuri da halayen gwamnati, ba za mu yi rigima da gwamnati ba duk da tura ta kai bango, a saboda haka mu ka yanke shawarar shiga yajin aiki.

"Idan ya kasance har an bude makarantu ba tare da biyan bukatunmu ba, babu sauran wani uzuri kuma babu abinda zai hana yajin aikinmu," a cewarsa.

Sannan ya cigaba da cewa; "an bamu tabbacin cewa za a saka mana dukkan alawus dinmu a cikin sabon tsarin biyan albashin ma'aikatan gwamnatin tarayya (IPPIS), amma har yanzu hakan ta gagara."

"Sakamu a cikin tsarin ya zama tamkar annoba, k**ar tsallen kwado daga cikin wuta zuwa kaskon suya. Biyan albashinmu da sauran hakkokinmu ya shiga mawuyacin hali."

The Nigerian government has announced another four weeks extension of the second phase of the eased COVID-19 lockdown Th...
06/08/2020

The Nigerian government has announced another four weeks extension of the second phase of the eased COVID-19 lockdown The announcement was made by the Secretary to the Government of the Federation (SGF), Boss Mustapha Mustapha urged Nigerians to act responsibly by taking steps to avoid contracting and spreading COVID-19.

23/07/2020

Ocean Ramsey swimming around the great white shark. Beautiful but a bit scary. Some people do have strong minds.

Entertaining you with people, issues, places and Events.From lifestyle to Liesure.Trailblazing and unique too!NB Current...
29/06/2020

Entertaining you with people, issues, places and Events.
From lifestyle to Liesure.
Trailblazing and unique too!
NB Currents Magazine....
Relax and let the currents take you around.

22/06/2020

Sabon shirin mu 'Ko Kun San' zai rinka zuwa muku a kullum a shafin tare da . Ku kasance tare da mu domin mu karu gaba daya.

 This is an oasis in the midst of a dessert in Yusufari Local Government Area of Yobe State, Nigeria.
21/06/2020


This is an oasis in the midst of a dessert in Yusufari Local Government Area of Yobe State, Nigeria.

21/06/2020

Gamji Dan Kwarai

Address

Kaduna

Telephone

+2348022299260

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NorthBlaze Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to NorthBlaze Hausa:

Share


Other Broadcasting & media production in Kaduna

Show All

You may also like