Taskar Yanci

Taskar Yanci Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Taskar Yanci, News & Media Website, Dutse.

TASKAR YANCI jarida ce ta yaren Hausa da aka samar da ita domin samar da sahihan labarai kan abubuwan cigaban zamantakewa a fannin siyasa, ilimi, tattalin arziki, lafiya, da sauransu.

Amincin Allah Ya tabbata a gareku baki daya!!!Ina farincikin sanar da ku cewar mun samar muku da manhaja mai suna SUFIDA...
03/02/2024

Amincin Allah Ya tabbata a gareku baki daya!!!

Ina farincikin sanar da ku cewar mun samar muku da manhaja mai suna SUFIDATA da zaku na siyen data, airtime, units na lantarki, cable subscription da PIN na fitar da jarabawar NECO, WAEC, NABTEB da NBAIS cikin sauki, araha da kuma inganci.

Zaku iya ziyarar shafinmu na yanar gizo a kan www.sufidata.ng ko ku ziyarci Google Play Store ku sauke manhajarmu mai suna SUFIDATA https://play.google.com/store/apps/details?id=co.median.android.objkld

Buy Cheap Internet Data Plan and Airtime Recharge for Airtel, 9mobile, GLO, MTN, Pay DSTV, GOTV, PHCN.

Katafariyar Kasuwar Zamani Ta Shoprite Ta Sanya Ranar Barin KanoKamfanin Kasuwar Shoprite ya yanke shawarar bin kamfanin...
16/12/2023

Katafariyar Kasuwar Zamani Ta Shoprite Ta Sanya Ranar Barin Kano

Kamfanin Kasuwar Shoprite ya yanke shawarar bin kamfanin Procter & Gamble da sauran manyan kamfanonin ƙasa da ƙasa na dakatar da kasuwanci a reshensa na Kano daga ranar 14 ga watan Janairu mai k**awa.

A sanarwar da kamfanin Shoprite ya saki ranar Alhamis, ya ɗora laifin barin Kanon ne kan wahalhalun kuɗaɗe da tsadar samar da kayayyaki da kamfanonin kasuwanci ke fuskanta a Najeriya.

Wannan na zuwa ne bayan sanarawar da kamfanin Jumia Food ya fitar ta dakatar da aiyukansa a Najeriya a ƙarshen wannan watan saboda yawaitar matsalolin tattalin arziƙin da ake fuskanta a ƙasar.

Kamfanin Shoprite ya sanar da takaicin bayar da sanarwar dakatar da aiyukansa a Kano, inda ya bayyana hakan a matsayin mataki na dole, ya kuma ce aikin da ma’aikatan kasuwar suke yi zai zo ƙarshe da zarar an dakatar da kasuwar.

Baya da Shoprite, kamfanoni irinsu Procter & Gamble da GlaxoSmithKline Consumer Nigeria Plc sun sanar da dakatar da aiyukansu saboda matsin tattalin arziƙin da ake fama da shi a ƙasa.

Da take magantuwa kan lamarin, Ƙungiyar Masu Samar da Kayayyaki ta Najeriya, MAN, ta bayyana cewar kamfanoni da dama zasu bar Najeriya saboda matsin tattalin arziƙin da ake fama da shi a Najeriya.

Gwamnatin Jigawa Ta Dakatar Da Biyan Ƴan J-Teach, Ta Kuma Gano Malaman Bogi 240 Da Masu Takardun Ƙarya 255Gwamnatin Jiha...
16/12/2023

Gwamnatin Jigawa Ta Dakatar Da Biyan Ƴan J-Teach, Ta Kuma Gano Malaman Bogi 240 Da Masu Takardun Ƙarya 255

Gwamnatin Jihar Jigawa ƙarƙashin jagorancin Gwamna Umar Namadi ta sanar da dakatar da biyan dukkan malaman da suke koyarwa a makarantun jihar ƙarƙashin shirin J-Teach.

Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Sagir Musa ne ya bayyana hakan ga ƴanjaridu yayin da yake jawabi kan sak**akon tattaunawar Majalissar Zartarwar Jihar.

Dakatar da albashin ƴan J-Teach ɗin ya biyo bayan karɓar rahoton kwamitin da aka ɗorawa alhakin duba yanda za a mayar da malaman na dindindin.

Kwamishinan ya ce, rahoton ya gabatar da bayanan da aka miƙawa tsohon gwamnan jihar, Muhammad Badaru Abubakar a ranar 9 ga watan Mayu, 2023 wanda yai nuni da bankaɗo malaman bogi 240 a cikin ƴan J-Teach da kuma wasu 255 masu takardun bogi, da ma wasu 72 da ba su da takardar komai.

Sagir Musa ya ƙara da cewa, an samu maimaituwar sunayen wasu ƴan J-Teach ɗin da kuma canja nagartattun ƴan J-Teach da waɗanda ba su da nagarta.

Ya kuma ce an gano cewar wasu ƴan J-Teach ɗin kwata-kwata ba sa zaman Jihar Jigawa, yayin da wasu s**a ɗau hayar wasu suna riƙe musu aikin.

Ya bayyana cewar waɗannan matsaloli sun jawo ruguje jarabawar da aka yi wa ƴan J-Teach ɗin kafin a ɗauke su aikin.

Ya ce, an dakatar da biyan ƴan J-Teach ɗin albashin ne har sai sabon kwamitin da aka naɗa kan lamarin ya kawo rahotonsa nan da sati huɗu masu zuwa, inda za a biya bashi ga duk waɗanda ba a samu da matsala ba.

Gwamonin Arewa 19 Sun Ziyarci Kaduna, Sun Bayar Da Gudunmawar Kuɗi Ga Mutanen Tudun BiriGwamonin Arewa 19 sun haɗu jiya ...
16/12/2023

Gwamonin Arewa 19 Sun Ziyarci Kaduna, Sun Bayar Da Gudunmawar Kuɗi Ga Mutanen Tudun Biri

Gwamonin Arewa 19 sun haɗu jiya Juma’a a Kaduna domin tattaunawa kan yanda za a magance matsalar tsaro, bunƙasa noma, haƙo mai a yankin Arewa da kuma jajantawa Gwamnan Kaduna Uba Sani kan iftila’in da ya jawo asarar rayuka da dama a Tudun Biri na Ƙaramar Hukumar Igabi da ke jihar.

Taron gwamnonin wanda Gwamna Uba Sani ya sauƙa, shine na farko da s**a gabatar tun bayan rantsuwar k**a aiki da s**a yi a ranar 29 ga watan Mayu na 2023.

Gwamnonin da s**a sami halartar zaman sun haɗa da Gwamnan Jihar Gombe, Muhammad Yahaya; Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Radda; mataimakan gwamnonin jihohin Jigawa, Bauchi, Kano, Yobe da Kwara waɗanda s**a wakilci gwamnoninsu.

Da yake jawabi ga sauran ƴan’uwansa, Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Muhammad Yahaya, ya yi allawadai da hatsarin da ya faru a Tudun Biri, inda ya jaddada cewar akwai buƙatar gwamnonin su sa ƙaimi wajen ganin an kawo ƙarshen matsalar tsaron da ta addabi yankin.

Gwamna Yahaya ya kuma yabawa Gwamnatin Tarayya kan ƙoƙarin da take na magance matsalar tsaro, inda ya ƙara da cewa, akwai buƙatar ƙara ƙaimi daga ɓangaren gwamnonin yankin Arewa domin ganin an kawo ƙarshen garkuwa da mutane, hare-haren ƴanbindiga, rigingimun ƙabilanci da ta’addancin da ya addabi Arewa.

Ya kuma yi alƙawarin ganin cewar ba ai watsi da abun da ya faru a Tudun Biri ba, zasu tabbatar da an yi bincike kuma an biyya diyyar waɗanda abun ya rutsa da su an kuma kare faruwar haka a gaba.

Haka kuma, gwamonin sun bayar da gudunmawar naira miliyan 180 ga waɗanda hatsarin ya rutsa da su, inda s**a gabatar da hoton cakin kuɗin ga Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani.

Najeriya Na Neman Sabon Bashin Naira Tiriliyan 1.2 Da Wasu Basuss**an Daga Bankin DuniyaA yanzu haka Gwamnatin Tarayya n...
01/10/2023

Najeriya Na Neman Sabon Bashin Naira Tiriliyan 1.2 Da Wasu Basuss**an Daga Bankin Duniya

A yanzu haka Gwamnatin Tarayya na tattaunawa da Bankin Duniya kan sabon bashin da ya kai dalar Amurka biliyan 1.5 daidai da naira Tiriliyan 1.2, k**ar yanda jaridar PUNCH ta gano.

Gwamnatin na neman bashin ne da a kai wa take da HOPE domin ‘Shirin Bunƙasa Cigaban Ɗan’adam Wajen Samun Damarmaki da Aiyukan Yi’ k**ar yanda shafin yanar gizo na Bankin Duniya ya nuna.

Manufar bashin da ake sa ran zai fara aiki a shekarar 2024 bayan samun amincewar bankin ita ce, a bunƙasa harkar samar da ilimi a matakin farko da kuma lafiya a matakin farko ga jihohin da zasu shiga tsarin.

Jaridar ta kuma gano cewar akwai wani sabon bashin da Najeriya ke shirin ciyowa wanda ba a bayyana yawansa ba domin sake fasalin harkokin manyan kuɗaɗe don bunƙasa tattalin arziƙi.

Haka kuma akwai sabbin basuss**an guda biyar da Najeriya ke tattaunawa domin samunsu, waɗanda s**a haɗa da naira biliyan 231.1 domin shirin samar da mafita ga ƴan gudun hijira da masu masauƙansu.

Sauran sun haɗa da naira biliyan 285.2 domin shirin bunƙasa harkar hada-hadar kasuwancin kayan gona ga mutanen karkara, naira biliyan 577.9 domin shirin bunƙasa samar da mak**ashi ta sabbin hanyoyin zamani, naira biliyan 539.3 domin shirin samar da wutar lantarki da bunƙasa harkokin noman rani da kuma naira biliyan 285.2 domin shirin bunƙasa samar da abubuwan da ake buƙata don samun ci gaba.

Tun a farko dai, cikin watanni huɗun farko na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Najeriya ta ciyo bashin da yawansa ya kai naira tiriliyan 1.5 daga Bankin Duniya.

Bankin Duniya dai shine kan gaba wajen bai wa Najeriya bashi, inda yake bin Najeriya kusan naira tiriliyan 12 k**ar yanda alƙaluma s**a nuna a ranar 30 ga watan Yuni, 2023.

A ƴan kwanakin baya kaɗan dai, Ofishin Kula da Bashi, DMO, ya ce bashin da ake bin Najeriya yanzu haka ya kai naira tiriliyan 87.38 a ƙarshen watan Yunin, 2023.

Bashin ya haɗa da wanda Najeriya ta ci daga cikin gida da yawansa ya kai naira tiriliyan 54.13 da kuma wanda ta ciyo daga wajen da ya kai naira tiriliyan 33.25.

Tinubu Ya Sanar Da Ƙarawa Ƙananan Ma’aikata Naira Dubu 25 A Tsawon Watanni 6Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce, a wat...
01/10/2023

Tinubu Ya Sanar Da Ƙarawa Ƙananan Ma’aikata Naira Dubu 25 A Tsawon Watanni 6

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce, a watanni shida masu zuwa, ƙananan ma’aikata za su sami ƙarin naira dubu ashirin da biyar a duk wata.

Shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne a jawabinsa na murnar cikar Najeriya shekarun 63 da samun ƴancin kai.

Tinubu ya ce, bisa la’akari da tattaunawar da ake da ƙungiyar ƙwadago, gwamnati ta zo da ƙarin albashi da zai ƙarawa mafi ƙarancin albashi yawa ba tare da an samu hauhawar farashi ba.

Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake bayani kan abubuwan da aka tanada ga ƴan ƙasa domin rage raɗaɗin janyen tallafin mai da kuma daidaita canjin kuɗaɗen ƙasashen waje.

Tinubu ya ce, gwamnatinsa na yin duk mai yiwuwa wajen ganin ta samar da sauƙi da bunƙasa tattalin arziƙi da kuma magance hauhawar farashi da ma bunƙasa samar da kayayyaki da tsaron rayukan al’umma da dukiyoyinsu.

Kira Ga Gwamna Ɗanmoɗi Kan Gyaran Matsalar APC A Birnin KuduDaga: Abubakar Ibrahim Ayuba (Habu Maja)Ba abu ne ɓoyayye ba...
04/09/2023

Kira Ga Gwamna Ɗanmoɗi Kan Gyaran Matsalar APC A Birnin Kudu

Daga: Abubakar Ibrahim Ayuba (Habu Maja)

Ba abu ne ɓoyayye ba cewar akwai gagarumar matsala a jam’iyyarmu ta APC a Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu. Za a iya tabbatar da haka idan aka yi la’akari da irin ƙarfin da muke da shi lokacin da muka shiga zaɓe a zaɓuɓbukan da s**a gabata, amma rashin haɗin kan shugabanninmu ya sa muka kasa kai wa ga nasara.

Tun kafin zaɓen 2023, APC tana da matuƙar ƙarfi a Birnin Kudu, muna da manya masu riƙe da muƙaman siyasa a ƙaramar hukuma, jiha da ƙasa. Muna da Sanata mai ci a wancan lokaci ɗan Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu. Muna da Ɗan Majalissar Wakilai mai ci a wancan lokacin ɗan Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu. Muna da Sakataren Gwamnatin Jiha, Ɗan Majalissar jiha da Kwamishinan Yaɗa Labarai da na Shari’a duk ƴan Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu. Shugaban Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu da mataimakinsa da kuma kansiloli 10 cikin 11 duk na jam’iyyarmu ne, uwa uba kuma al’umma sun yarda da jam’iyyarmu amma duk da haka rarrabuwar kan da ke tsakanin manyanmu ta hana mu kai wa ga nasara.

Babu haɗin kai tsakanin yaran Faruku da na Nakudu. Babu haɗin kai tsakanin yaran Nakudu da na Engr. Magaji Da’u. Babu haɗin kai tsakanin yaran SSG na yanzu da na sauran gidaje kowa ya sa gabansa daban da na sauran. Kowa ya ware yana harkarsa daban tare da yaƙar ɗan jam’iyyarsa da ke wani gidan da ba nasa ba. Haka aka yi ta yi, kuma wannan ce ta sa muka faɗi zaɓe.

Abin takaicin har yanzu shine, duk da mun faɗi a takara, kuma an kafa sabuwar gwamnati a jiha, har yanzu dai shugabanninmu ba su gane Annabi ya faku ba, sun ƙi su dawo su haɗa kansu. A yanzu haka babu haɗin kai tsakanin gidan SSG Bala Mamser da sauran gidaje irin na su Faruku, Engr. Dau da sauransu. Kuma har bayyana rashin haɗin kan yaran gidajen su ke yi ƙarara a social media da kafafen sadarwa.

Tabbas akwai tsananin buƙatar Mai Girma Gwamna Malam Umar Namadi Danmodi ka shigo sabgar APC kicin-kicin a Birnin Kudu domin ka gyarata. Idan har muka ci gaba da tafiya a haka to babu inda zamu je kuma jam’iyyar za ta ƙara wargajewa a Birnin Kudu.

Haka kuma Mai Girma Gwamna, ina kira gareka da ka bayar da takarar Shugaban Ƙaramar Hukuma nan gaba a Birnin Kudu ga haziƙin matashi, ƙwararre a kan al’amuran ci gaban al’umma kuma wanda al’umma ta yarda da shi. Yin hakan zai matuƙar temakawa wajen farfaɗo da kimar jam’iyyarmu da kuma samarwa Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu ci gaba.

Ina yi maka fatan alkhairi da addu’ar Allah Yai maka jagora Ya kuma ba ka nasara kan ƙudire-ƙudirenka na alkhairi ga al’ummar jiharmu Jigawa.

Daga ɗanka, Abubakar Ibrahim Ayuba (Habu Maja), Birnin Kudu

PDP Ta Cika Shekaru 25 Da Kafuwa, Ta Ce Shekarunta Na Mulki Ne Gwalagwalai Ga NajeriyaA jiya Alhamis ne, jam’iyyar Peopl...
01/09/2023

PDP Ta Cika Shekaru 25 Da Kafuwa, Ta Ce Shekarunta Na Mulki Ne Gwalagwalai Ga Najeriya

A jiya Alhamis ne, jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP, ta cika shekaru 25 da kafuwa, inda ta bayyana shekarunta 16 na mulkin Najeriya a matsayin shekarun da s**a zama gwalagwalai ga Najeriya da ƴan Najeriya.

A wani jawabi da yai Abuja kan cikar jam’iyyar shekaru 25, Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na PDP, Debo Ologunagba ya ce, jam’iyyar ta yanke hukuncin yin ƙananan bukukuwa saboda babu wani abin murna a wannan lokaci saboda, a cewarsa, jam’iyyar All Progressives Congress, APC ta wargaza duk ci gaban da PDP ta kawo a tsawon shekaru 16 cikin shekaru 8 kacal.

Ya ce, PDP na murna dagewar ƴan Najeriya kan mulkin demokaraɗiyya, musamman ma waɗanda s**a assasa lamarin da kuma mambobin jam’iyyarsu ta PDP, bisa sadaukarwarsu da gudunmawar da s**a bayar wajen dawowar mulkin demokaraɗiyya da samun dorewarta a Najeriya.

Ya ce, yana kan gaba-gaba a tsarin PDP na cewar mulki na al’umma ne, wannan ta sa jam’iyyar yin biyayya ga tsarin dokoki, da tsarin damawa da kowa da kuma bai wa kowa ƴanci, da tabbatar da ƴancin ƴanjaridu da gudanar da ingantaccen zaɓe.

Ya ƙara da cewar, jam’iyyar PDP ta samar da bunƙasuwar tattalin arziƙi, samar da ci gaban ababen more rayuwa, ɗaukar ma’aikata da samar da damarmakin kasuwanci da sauran abubuwan alkhairi, abin da ya sanya shekarun PDP a matsayin shekarun da Najeriya ta fi samun ci gaba a tarihinta.

Debo Ologunagba ya ƙara da cewar jam’iyyar PDP ta bunƙasa harkokin sa ka hannun jari daga ƴan ƙasa da kuma baƙi ƴan ƙasashen waje a dukkan fannoni har sai da ta kai kasuwanci a Najeriya na cikin mafiya samun riba a duniya.

Ya ce, amma abin baƙin ciki, dukkan nasarorin da PDP ta samarwa Najeriya, jam’iyyar APC ta durƙusar da su, abin da ya sa cikin shekaru takwas kacal, tattalin arziƙi ya lalace har ƙasar ta zama cibiyar talauci ta duniya da tarun marassa aikin yi da yawansu ya kai kaso 35 cikin 100.

Ya kuma ce, APC ta jawo tsananin yunwa ga ƴan Najeriya da ƙyale ɓullar baƙin cututtuka da haifar da yawaitar mutuwar ƴan ƙasa.

Ologunagba ya ce, a ƙarƙashin gwamnatin APC, manyan kamfanonin duniya na barin Najeriya; yayin da darajar naira tai matuƙar faɗuwa daga naira 197 a dala ɗaya zuwa sama da naira 900 a dala ɗaya; man fetur da ake siyar da shi a naira 87 duk lita kafin zuwan APC, yanzu ya koma sama da naira 600.

Ya ce baya da waɗannan ma akwai ƙare ƙaren wahala ta haraji kala-kala da tsadar biyan kuɗaɗen abubuwa da cirewa mutane kuɗaɗe waɗanda jam’iyyar ta APC ta ƙaƙabawa ƴan Najeriya.

Ya ƙara da cewar, rayuwa a Najeriya ta yi matuƙar wahala, ta yanda a yanzu ƴan Najeriya na siyar da rayuwarsu da miƙa kansu cikin bauta a ƙasashen waje domin su samu sauƙi.

Ya kuma ce, jam’iyyar APC ta yaudari mutane wajen karɓar mulki ta hanyar amfani da ƙarerayi, sannan kuma tana amfani da ƙarfi da cin zarafi da maguɗi wajen ganin ta ci gaba kasancewa a karagar mulki.

Sakataren Yaɗa Labaran na PDP, Ologunagba ya kuma ce, jam’iyyar PDP na kira ga ƴan Najeriya da kar su bari guiwarsu ta sare a kan Najeriya, inda ya ƙara da cewar, jam’iyyarsu ta PDP za ta ci gaba da kasancewa tare da su a duk inda ci gabansu ya ke.

Jigawa Za Ta Siyo Buhun Shinkafa Dubu 42, Za Ta Biya Wa Ɗaliban Jami’a Kuɗin MakarantaGwamnatin Jihar Jigawa ta amince d...
31/08/2023

Jigawa Za Ta Siyo Buhun Shinkafa Dubu 42, Za Ta Biya Wa Ɗaliban Jami’a Kuɗin Makaranta

Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da samar da kayan tallafin rage raɗaɗin janye tallafin man fetur, biyawa ɗaliban jihar kuɗin karatu a jami’o’i da kuma siyo taraktocin noma guda 54 domin manoman jihar.

Gwamnatin ta amince da aiwatar da waɗannan aiyuka ne a jiya Laraba, yayin gudanar da zaman Majalissar Zartarwar Jihar Jigawa da ya gudana ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar, Malam Umar Namadi.

Sanarwar bayan taron da Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar, Sagir Musa Ahmad ya fitar ta nuna cewar, gwamnatin ta amince da siyo tirela saba’in ta shinkafa, kimanin buhu dubu 42,000, domin rabawa ƴan jihar.

Ƙari a kan hakan, gwamnatin ta amince da siyo buhun gero 32,400 (tirela 54), da katan ɗin taliya dubu ɗaya domin rabawa a matsayin tallafin rage raɗaɗin janye tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi.

Sagir Musa ya bayyana cewar za a raba waɗannan kayayyaki ne ƙarƙashin kulawar Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar, SEMA, sannan ya ce, adadin kuɗaɗen da za kashe domin siyo waɗannan kayayyaki ya kai naira biliyan uku da miliyan ɗari takwas da dubu arba’in da takwas (N3,848,000,000.00).

Biya Wa Ɗalibai Kuɗin Makaranta
Haka kuma, a zaman Majalissar Zartarwar, gwamnatin Jihar Jigawan ta amince da biya wa ɗaliban jihar da ke karatu a Jami’ar Gwamnatin Tarayya ta Dutse, FUD; Jami’ar Bayero da ke Kano, BUK; Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, KUST; da kuma Jami'ar Maiduguri, UNIMAID.

A kan wannan, gwamnatin ta ware naira miliyan ɗari da sittin da bakwai, da dubu ashirin da huɗu da ɗari tara da hamsin (N167,024,950.00).

Gwamnatin ta bayyana cewar ta yi hakan ne domin ragewa iyaye nauyin biyan kuɗaɗen karatun da su ke biya wa ƴaƴansu duba da yanayin da ake ciki.

Siyo Taraktoci 54 Don Manoma

Majalissar Zartarwar ta Jihar Jigawa ta kuma amince da siyo taraktocin noma guda 54 a kan kuɗi naira biliyan 1.

Gwamnati za ta siyo waɗannan taraktoci ne ta hannun Kamfanin Siye da Siyarwar Kayan Aikin Gona ta Jiha, JASCO.

NNPC Ya Musanta Raɗeraɗin Ƙarin Kuɗin Man Fetur Da Ake Ta Yi
15/08/2023

NNPC Ya Musanta Raɗeraɗin Ƙarin Kuɗin Man Fetur Da Ake Ta Yi

Ana Matsawa Najeriya Kan Ta Amince Da Auren JinsiCocin Angalican ta Najeriya ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta bijir...
15/08/2023

Ana Matsawa Najeriya Kan Ta Amince Da Auren Jinsi

Cocin Angalican ta Najeriya ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta bijirewa kiraye-kirayen da Turawan Yamma ke mata na ta sake matsayinta kan auren jinsi a Najeriya.

Wannan dai na a cikin jawabin bayan taron da cocin ta saki bayan kammala taro na 12 na shugabannin cocin na faɗin Najeriya wanda aka gudanar a Abuja.

Takardar bayan taron, wadda Dr. Abraham Yisa da Babban Lauyan Najeriya, Odein Ajumogobia s**a sanyawa hannu ta bayyana cewar, Najeriya na fuskantar matsi daga masu kare haƙƙin masu auren jinsi a duniya da kuma ƙasashen waje wajen ganin an halatta auren jinsi a ƙasar.

Takardar ta kuma yi kira ga mabiya addinin Kirista da su tabbata kan aikin imani da biyayya ga Ubangiji ta hanyar yin rayuwa wadda a cikinta a kwai gaskiya da mutunci sannan kuma ta yi kira ga cocuna da su yi riƙo da addinin gaskiya.

Takardar jawabin bayan taron ta kuma yi kira ga ƴan Najeriya da su koma ga Allah domin neman ɗauki kan al’amuran ƙasa, inda tai nuni da cewar Allah yana tare da ƴan Najeriya a ko da yaushe.

Haka kuma ta yi kira ga gwamnatoci a dukkanin matakai, da su koma ga Allah tare da watsi da dukkan abubuwan ƙi domin a samu ingantaccen ci gaba a ƙasa.

14/08/2023

Hajiya Najaatu Muhammad kan Yaki da Nijar

29/07/2023

Dalilin da ya sa sojoji s**a kifar da Bazoum a Nijar.

03/07/2023

Wajibi Ne Gwaman Namadi Ya Karbe Da Yin Bincike Kan Kassarawa Da Mallakarwa Kai Dajikan Jigawa

Daga: Ahmed Ilallah

Adalcin shugabanci shine, yin abu dai daidai domin zaman lafiyar al'ummar su. Hadama da babakere da tara dukiya ta kowane hali, ba suffa ba ce ta adalin shugaba. Adalcin shugaba shine ne bawa kowa hakkin sa, kare mutuncin sa da lafiyar sa.

Tabbas a kwai abin takaici da tausayii da ban haushi, ganin yadda Shugabannin wannan zamani suke ganganci da jahiltar mulki da jagorancin al'ummah. Wai in da duk wanda Allah ya bawa mulki watanda suke da kayan talaka, da ku Shugabannin yau za ku samu wani abu da ya rage?

A wannan karnin a kwai abin mamaki yadda Shugabannin Kananan Hukumomin mu, s**a maida jejinan jahar Jigawa tamkar kayan gadon su, sun sare dajukan suna rabawa kan su da mutanen su, ba tare da dogon tunani ba a kan muhiman cin wannan dajujjuka.

Duk da cewa a na rade radin cewa, Maigirma Gwamna ya dau matakin soke rabon filaye da gonakan da a kayi ba bisa ka'ida ba.

Bisa wannan dalilai muna kira da Maigirma Gwamna da soke duk wani rabon fili a shekara biyar baya da kafa kwamitin, mutane masu kishi da gaskiya su bincika wannan badakala..

KAWO KARSHEN RIGIMAR MAKIYAYA

Ya k**ata kulum muna tinanin abubuwan da suke haddasa rigingimu, musamman tsaka on manoma da Makiyaya, gudun kadda irin wannan matsala ta girma, ya zama dole mu dau darasin abubuwan da ke faruwa a wasu wurare. Allah ya sau waka.

KO KUWA DA KWARAROWAR HAMADA

Ya zama dole mu tunawa kan mu gaskiya game da yadda muke cikin hadarin kwararowar hamada. Ya k**ata a ce gwamantin Jigawa hankalin ta ya tashi ganin yadda mutane ke saran bishiyoyi ba bisa ka'ida ba, amma wannan halayar, ba ta dami Shugabannin mu ba.

Abin takai cin, shine a na kukan targade sai kuma ga karaya, karayar ma ta ganganci. Sai ga shi Shugabannin Kananan Hukumomin mu sun k**a shiga dajukan mu, suna rabawa kayukan su da wasu tsirarun mutane. Zai yi kyau, Maigirma Gwamna ya yi duba na adalci, don maida kowane al'amari yadda yake.

Allah ya taimaki Jahar Jigawa.

[email protected]

TASKAR YANCI jarida ce ta yaren Hausa da aka samar da ita domin samar da sahihan labarai kan abubuwa

20/04/2023
Amfanin Zogale Ga Fatar Dan AdamWani lokaci abubuwa masu girma s**anzo a karamar suffa, k**ar dai zogale, da ya kasance ...
11/04/2023

Amfanin Zogale Ga Fatar Dan Adam

Wani lokaci abubuwa masu girma s**anzo a karamar suffa, k**ar dai zogale, da ya kasance ƙananan ganye mai tarin albarka da kara lafiya. Kazalika ba kadai ganyen bane mai amfani, kowanne ɓangare na wannan tsiro, tun daga iri, furanni, tushensa, har ma da sassakensa, an san su wajen adana phytonutrients, amino acid, minerals, antioxidants, wanda ke taimakawa wajen rigakafin, kumburi, da rage yawan s**arin jini da matakan cholesterol.

Zogale na daga cikin abincin da ake ta’ammali da su sosai, ana yawan amfani dashi a matsayin wani bangare na girkin yau da kullum, a wasu lokutan ma akan busar da shi a mai dashi hoda domin barbadashi a girki don karin dandano.

Amma sai dai kash har yanzu mutane ba su gama gano amfanin wannan tsiro mai dinbin mamakiba. Wannan amfanin kuwa shine fitar da mai daga cikin ‘ya’yanta, wanda ke da ɗimbin amfani ga fata.

“Man zogale ko man ben, yana da hormones na shuka da ake kira cytokines waɗanda ke taimakawa girman cellular da kuma hana lalacewar tissues din fata," in ji masanin abinci mai gina jiki, kuma ƙwararre a ilimin aromatherapy Janice Rosenthal, wanda ya kirkiri Garden of Essences.

Ga kadan daga cikin amfanin wannan Mai na zogale a fatar mutum:

Vitamin C na man zogale yana ƙarfafa collagen, yana taimakawa wajen rage yamutsewar fata. Man zogale mai cike da bitamin da sinadirai masu yawa yana samar da ingantattun sinadaran kula da fata, godiya ga abubuwan da ya kunsa irin su antioxidants, antibacterial, da abubuwan gina jikin sa. “Ben oil” ya taimakawa man zogale wajen zama babban makami dan gujewa tsufan fata, kuma gashi da fa'ida ga gashin kan mutum.

Amfanin bai tsaya iya nan ba. Rosenthal ya kara da cewa, amfani da man da aka fitar daga zogale yana kuma taimakawa wajen kawar da kananan matsalolin fata k**ar su kurajen fuska da kuma rage duhun fata, kuma an san magungunansa da taimakawa wajen kauda kumburin ciki da waje.

Yanzu da kuka kara sanin amfanin wannan tsiro, lokaci ya yi da zaku ga fa'idodin zogale da kanku masu ban mamaki.

• Erno Laszlo, (Man Cleansing): Wannan man ba iya cire dattin fuska yake ba, yana kuma saka laushin fata da Hanata bushewa.
• HUM Nutrition Raw Beauty (Koriyar Hoda): Shan kofi daya na Wannan hoda na kawarda abubuwan dake lalata, kuzari, da haɓaka kyan fata har guda 39.
• Decleor Hydra Floral Anti-Pollution Hydrating Gel-Cream: Kare fata daga gurɓacewa, wannan gel-cream din wato man shafawa yana kauda bushewar fata.

Baya ga tarin sinadirai marasa iyaka, Shin kun san cewa zogale tushen bitamin A ne, wanda ke inganta lafiyar gani. Shin ko kun san cewa binciken kimiyya na baya-bayan nan yana ganin zogale a matsayin hanyar magance ciwon s**ari, kuma an tabbatar da cewa yana rage yawan glucose a cikin jini?

Shin kun san cewa daya daga cikin mafi kyawun fa'idodin zogale shine yana haɓaka ƙarfin garkuwar jiki?
Shin ko kun san cewa an gudanar da bincike da dama akan yuwuwar zogale ya kasance a matsayin maganin cutar daji?

A ƙarshe, ina ganin zogale yana daya daga cikin manyan tsirrai da amfaninsu bazai Taba misaltuwa ba. Ku Gwada ƙara shi a cikin abincin ku, ku kuma yarda da ganyen, don ganin abubuwan al'ajabi.

Manufata Ga Jihar Jigawa (10) – Mustapha Sule LamidoDaga: Mustapha Sule LamidoZan fara da godiya da jinjina ga ƴan uwana...
08/03/2023

Manufata Ga Jihar Jigawa (10) – Mustapha Sule Lamido
Daga: Mustapha Sule Lamido
Zan fara da godiya da jinjina ga ƴan uwana mutanen Jihar Jigawa bisa fitowa da s**a yi domin kaɗa ƙuri’unsu a zaɓen shugaban Ƙasa da na ƴan Majalisun Tarayya. Duk da irin ƙalubalen da aka fuskanta, mutane sun nuna haƙuri wajen bin layi don zaɓo waɗanda zasu jagoranci ƙasarmu. To amma duk da haka, ina ganin akwai buƙatar mu ƙara himma wajen fitowa a zaɓuka masu zuwa. A cikin mutane masu rajistar zaɓe miliyan 2.35 da muke dasu a Jigawa, ƙasa da miliyan ɗaya ne kaɗai s**a kaɗa ƙuri’a a zaɓen Ranar Asabar da ta gabata wanda hakan bai fi 40% ba.
Zan yi amfani da wannan dama don taya murna ga ƴan takarkarin Jam’iyyar PDP na Jiharmu da na sauran sassan ƙasarnan waɗanda s**a samu nasarar lashe zaɓe a matsayin sanatoci da ƴan majalisu. Ina kira garesu da su mayar da hankali kan manufofi da tsare-tsaren da zasu taimaki jama’a waɗanda aka san jam’iyyar PDP da su. Muna kira ga Hukumar INEC da jami’an tsaro su yi gyare-gyare da ƙara shiri don ɗinke ɓaraka da magance kura-kuren da s**a haddasa maguɗin da ya sa Jam’iyyarmu ta rasa wasu kujerun ƴan majalisu a Jihar Jigawa da sauran gurare a saasan ƙasarnan.
Game da zaɓen shugaban Ƙasa, mutane da yawa sun tofa albarkacin bakinsu a kan wasu muhimman al’amura masu alaƙa da doka da shari’a. Na san cewa shugabanni da jagororin Jam’iyyarmu na ƙasa sun yi nazari sosai a kan abubuwan domin ɗaukar matakin doka da ya dace. Ni daga ɓangarena, ina kira ga jama’a su zauna lafiya, su zama masu bin doka kuma su sanya idanu sosai tare da kyautata zaton gyaruwar al’amura. Kada mu karaya, mu ci gaba da jajircewa da yin aiki don samun ƙasa ta gari a 2023 da kuma gaba.
Ina miƙa godiya ta ga dukkan masu ruwa da tsakin Jam’iyyar PDP na Jihar Jigawa bisa aiki tuƙuru da s**a yi a zaɓen shugaban Ƙasa da kuma rashin nuna gajiyawa wajen bada gudunmawa a tsawon watanni shida da s**a wuce. Ba shakka, kun nuna sadaukarwa, jajircewa da amana. Irin wannan jajircewar taku ce ta taimaka wa PDP wajen cimma nasarorin aiwatar da daki-barin aiyyuka a shekarun 2007-2015 da har yanzu ba a k**anta irinsu ba a Jihar Jigawa. Zamu ci gaba da dogaro kan gudunmawarku don tabbatar da samun nasara a zaɓen Gwamna da ƴan majalisun jiha.
Kasancewar mun kewaya dukkan ƙananan hukumomi 27 domin gabatar da manufofinmu ga jama’ar Jihar Jigawa, bana jin akwai buƙatar sake maimata tsare tsarenmu a yanzu. Mun riga mun fitar da kundin manufofinmu tun watan Nuwamba wanda muke ci gaba da karɓar shawarwarinku game da shi. Zamu yi masa gyaran fuskar da ya dace da muradunku inda buƙata kuma zamu yi iya bakin ƙoƙarinmu wajen aiwatar da shi idan kuka bamu dama Insha Allah. Muna kira da mata, matasa da dattawa su bamu goyon bayan da muke buƙata.
Yau ina so na maida hankali kan yin cikakken bayani a kan abubuwa guda uku masu matuƙar muhimmanci kafin zaɓe. Na farko, ina shaida wa kowa cewa ina fatan zama gwamna kuma hadimin haɗaɗɗiyar Jihar Jigawa, bai wai gwamnan wani ɓangare ko wasu wararrun mutane ba. Na sha faɗa cewa, haɗin kan Jigawa shi ne abu na farko a cikin manufofinmu, a taƙaice ma dai shi ne babban dalilin da yasa na shiga wannan takara. Idan na zama gwamna, zan yi wa kowa adalci Insha Allahu. Don haka ina kira ga dukkan masu ɗabbaka siyasar ɓangaranci da niyyar taimakonmu ko cutar damu, su daina. Jihar Jigawa ba zata taɓa kai wa inda take so ba a matakin ci gaba da rarrabuwar kai. Don haka, ya zama dole mu fahimci mummunan tasirin waɗannan abubuwan da muke yi.
Na biyu, ina jaddada cewa na shirya wa wannan aiki. Idan ina tunanin ba zan iya ba, ba zan shiga wannan takara ba. Mun riga mun tsara dukkan abubuwan da muke so mu cimma tun daga ranar farko, kuma Insha Allahu ba zamu yi wasa ba. Zamu ɗauki kowacce rana a gwamnatinmu da matuƙar muhimmanci. Mun riga mun samar da abokan aiki da haɗin guiwa da muke buƙata. Ina tabbatar muku, ba zamu baku kunya ba idan kuka bamu dama. Zamu saurareku kuma zamu yi aiki don inganta rayuwarku. Muna da yaƙinin ba zaku yi nadamar zaɓarmu ba Insha Allah.
Na uku, ina kira ga jama’ar Jihar Jigawa su fita wajen kaɗa kuria a ranar zaɓen gwamna da kishin Jiharmu a ransu. Mu sanya jiharmu a farko. Mun bawa APC shekaru 8 kuma mun ga iya abin da zasu iya. Sun yi alƙawarin ɗorawa daga inda s**a tsaya wanda hakan bai wadatar ba. Mu kuma mun yi alƙawarin kawo tsare tsaren da zasu ɗaukaka jiharmu fiye da yadda take a yanzu. Mu sa hikima wajen kaɗa ƙuri’unmu.
Mun fahimci cewa Jam’iyya mai mulki burinta shi ne maguɗin zaɓe. Muna ta karɓar rahotanni masu tada hankali kan yadda suke da niyyar yin amfani da hanyoyi daban daban domin juya sak**akon abin da mutane s**a zaɓa. Wannan abin takaici ne duba da cewa masu yin hakan sune s**a fi kowa cin moriyar ingantaccen zaɓe a baya. Da ana mana dariya ana ganin bamu isa ba, an manta cewa girma da ɗaukaka a hannun Allah suke, yanzu kuma so ake a turmushemu da ƙarfin tsiya. Ina kira a garemu mu tashi mu kare ƙuri’inmu kuma mu hanasu cimma mummunan ƙudurinsu. Mu yi watsi da duk wata barazana da zasu yi mana.
Duk wanda ya yi ƙoƙarin sayen ƙuri’unku da kuɗi ko kayan abinci, to ya nuna ƙololuwar rashin girmamawa gareku. Kawai yana ganinku a matsayin waɗanda zai iya amfani dasu a lokacin da ya ga dama. Ƙuri’unmu sun fi ƙarfin duk wani farashi. Kamata ya yi a ce mutanen da s**a yi shekaru takwas suna mulki su burgeku da aiyukan raya ƙasa ba wai kyautar kayan abinci da kuɗin da baza su magance muku matsalolin da s**a saka ku a ciki a shekaru huɗu masu zuwa ba.
Alhamdulillah, wannan doguwar tafiya tamu ta zo da ƙalubale iri iri. Amma dai ko sau ɗaya ban taɓa nadamar shiga siyasa ko tsayawa takara ba. Ina da yaƙinin cewar ba wani abin da zaka iya canzawa ba tare da ka shiga an dama da kai ba. Babu wasu kalamai da zan iya amfani da su wajen gode muku. kan irin soyayya, goyon baya da karɓuwa da kuka nuna mana. Zan yi alfahari da wannan har ƙarshen rayuwa ta. Ko yanzu mun kafa tarihi, domin mun gudanar da kamfen mai manufa wanda ya zama abin misali a tarihin siyasar Jihar Jigawa. Sannan kuma da goyon bayanku, zamu kafa wani tarihin Ranar Asabar, 11 ga watan Maris, 2023. Insha Allah.
Gobe ta Allah ce!
©Santurakin Dutse.

Santuraki Zai Samarwa Ma’aikatan Jigawa Rancen Noma Da Kiwo Marar Kudin RuwaDan takarar gwamnan Jihar Jigawa karkashin t...
07/03/2023

Santuraki Zai Samarwa Ma’aikatan Jigawa Rancen Noma Da Kiwo Marar Kudin Ruwa

Dan takarar gwamnan Jihar Jigawa karkashin tutar Jam’iyyar PDP, Alhaji Mustapha Sule Lamido, Santurakin Dutse, ya yi alkawarin karawa ma’aikatan gwamnati da ke jihar karfin guiwa wajen shiga harkar sana’ar noma da kiwo domin bunkasa tattalin arzikinsu.

Dan takarar ya yi wannan bayani ne a shafinsa na Facebook, a cikin jerin irin aiyukan da yake alkawarin yiwa al’ummar Jihar Jigawa idan har sun zabe shi a ranar Asabar mai zuwa.

Santurakin Dutsen ya ce, “Ya k**ata a samar da wani ƙuduri na ƙarfafa guiwar ma’aikatan gwamnati da kamfanoni su shiga harkar noma a matsayin ƙarin sana’a.

“Gwamnati ta duba yiwuwar ware wasu kuɗaɗe don bada rancen yin noma ga ma’aikata ba tare da kuɗin ruwa ba wanda za a dinga cirewa daga albashinsu a tsawon wani lokaci.”

Dan takarar gwamnan na jam’iyyar PDP ya kara da cewa, za a tabbatar da cewa iya waɗanda aka tabbatar suna kan tsarin noman ne kaɗai za a ba wannan rance.

Ana yawan kallon ma’aikatan gwamnati a Jihar Jigawa a matsayin masu dogara da iya albashinsu, abin da ke hana wadatar arziki da walwala a jihar a lokuta da dama.
A baya dai ma’aikatan gwamnatin jihar na samun wasu tagomashi daga tsohuwar gwamnatin jihar, abubuwan da gwamnati mai ci ta sossoke saboda matsin tattalin arziki in ji ta.

Address

Dutse

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskar Yanci posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Taskar Yanci:

Videos

Share


Other Dutse media companies

Show All

You may also like