MAZAN JIYA

MAZAN JIYA Tarihin ma gabatanmun a Najeriya

Takaitaccen tarihin Janar Sani AbachaAn haifi janar Sani Abacha ranar 20 ga watan Satumbar shekarar 1943 a cikin garin K...
15/06/2023

Takaitaccen tarihin Janar Sani Abacha
An haifi janar Sani Abacha ranar 20 ga watan Satumbar shekarar 1943 a cikin garin Kano.

Ya yi makarantar Firamari ta City Senior Primary School, Kano, Government College, Kano, 1957-1962, Kwalejin horas da sojoji ta Kaduna Najeriya, 1962-1963.

Sannan ya wuce kwalejin Horas da Sojoji ta Aldershot dake Ingila, 1963, Kwalejin horas da dakarun kasa ta Warminster, ta Birtaniya 1966, 1971 Kwalejin sojoji ta Jaji dake Kaduna Najeriya, 1976, Kwalejin nazarin manufofi da tsara dabarun mulki ta Kuru, Jos, 1981, ya yi kuma wasu kwasa-kwasai da s**a shafi harkar tsaro a Canada, Amurka a shekarar 1982.

Tun daga juyin mulki na farko a Najeriya a shekarar 1966 janar Sani Abacha ke taka rawar gani sai wanda aka yiwa Shagari da na Babangida da kuma wanda yaiwa Cif Ernest Shenakon.

Allah ya yiwa janar Sani Abacha rasuwa ranar 8 ga watan Yuni shekarar 1998 yana da shekaru 54 da haihuwa sakamakon ciwon zuciya.

Ya mutu ya bar mata daya Hajiya Maryam Abacha da 'ya 'ya tara mata uku da maza shida.

ASSALAMU ALAIKUMBarka kan da wannan lokacin mai albarka, ayau ma mun kara bunci ko muku tarihin daya  daga cikin Magaba ...
04/06/2023

ASSALAMU ALAIKUM
Barka kan da wannan lokacin mai albarka, ayau ma mun kara bunci ko muku tarihin daya daga cikin Magaba tanmu wanda shima yayi gwagwarmaya a wannnan kasar mu ta Nigeria
Wato Sa'adu Zungur.
TAKAITACCEN TARIHIN MALAM SA'ADU ZUNGUR
AN haife shi a shekara ta 1915 - ya mutu a shekara ta 1958) shi ne mutumin da ya fara kafa jam'iyyar siyasa a Arewacin Najeriya. Shi ma mawaƙi ne kuma Bahaushe Mahaifinsa shine limamin Bauchi. Yayi makarantar firamare elemantery school garin Bauchi sanna ya tafi higher college ta garin Katsina bayan ya kammala yatafi yaba technical college(1934). Sannan bayan yabar lagas yakoyar a jihar Kano a (1940) sannan ya dawo Zaria inda yazama shugaba a makarantar magunguna a(1941) haka dai ya ƙirƙirar kungiyar hadin kan al'umma da abota a garin Zaria inda alaqarshi da marigayi Malam Aminu Kano takara bunkasa

DA ƊUMI-ƊUMI: Nan da Mako biyu za a buɗe sabuwar matatar Man Fetur na shahararren mai kuɗin Afrika, Aliko Ɗangote da ke ...
14/05/2023

DA ƊUMI-ƊUMI: Nan da Mako biyu za a buɗe sabuwar matatar Man Fetur na shahararren mai kuɗin Afrika, Aliko Ɗangote da ke jihar Legas. Mutane dubu 40 za su samu aiki a matatar Mai ɗin na Dangote da za a buɗe.

I've just reached 1K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏🤗...
09/05/2023

I've just reached 1K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏🤗🎉

TAKAITACCEN TARIHIN IBRAHIM BADAMASI BABANGIDA An haifi BABANGIDA a watan Agusta na shekarar 1941 a garin Minna na jahar...
08/05/2023

TAKAITACCEN TARIHIN IBRAHIM BADAMASI BABANGIDA
An haifi BABANGIDA a watan Agusta na shekarar 1941 a garin Minna na jahar Neja.

Ya yi karatu a makarantar soji ta India a shekarar 1964, makarantar horas da sojoji ta Royal Armoured Centre ta Ingila daga 1966, kwalejin sojoji ta Jaji a shekarar 1977 da kuma makarantar sojin ruwa ta Amurka a shekarar 1980.

A shekarar 1962 ya shiga aikin soji inda yai aiki a gwamnatin sojin janar Obasanjo. Ya taka rawar gani a juyin mulkin 1976.

Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya yi aure ranar 6 ga watan Satumbar 1969 ga Maryam wadda Allah ya yiwa rasuwa ranar 27 ga watan Disambar 2009. Janar Babangida na da 'ya'ya 4 biyu maza biyu mata.

TAKAITACCEN TARIHIN ALHAJI ALIYU MAI BORNOAn haifi Mallam Aliyu Mai Bornu ne a shekarar 1919 sannan ya fara makaranta fi...
29/04/2023

TAKAITACCEN TARIHIN ALHAJI ALIYU MAI BORNO
An haifi Mallam Aliyu Mai Bornu ne a shekarar 1919 sannan ya fara makaranta firamari a shekarar ta 1932. Daga baya aka koma da shi makarantar sakandare ta Yola daga nan ya tafi kwalejin Kaduna a shekarar ta 1938 sannan ya kamala karatun sa a shekara ta 1942 bayan ya cancanci ya zama Malami Mai koyar da Ingilishi.

Mallam Mai Bornu ya koyar da Ingilishi a makarantar, Yola Middle School daga shekara ta 1942 zuwa 1946 sannan ya koma zuwa Kwalejin Kaduna inda yaci gaba da koyarwa a shekara ta 1954, sannan kuma ya yi aiki a matsayin Mai Kula da Gidan Makaranta a Veterinary School kafin nan ya tafi zuwa Jami’ar Bristol duk dai a shekara ta 1954, don nazarin tattalin arziki (Economics).

Bayan kammala karatunsa a shekarar 1957, ya dawo Najeriya ya kuma yi aiki tare da ma’aikatar kula da jama’a ta Arewacin Najeriya a matsayin Babban Jami’in Gudanarwa inda ya rike mukamai daban-daban kafin nan yasamu zuwa Babban Bankin Najeriya a 1959 a matsayin Mataimakin Sakatare a CBN.

17/04/2023

Amina (Queen of Zazzau)

Amina (also Aminatu; died 1610) was a Hausa Muslim historical figure in the city-state Zazzau (now city of Zaria in Kaduna State), in what is now in the north-west region of Nigeria. She might have ruled in the mid-sixteenth century. A controversial figure whose existence has been questioned by some historians, her real biography has been somewhat obscured by subsequent legends and folk tales.

Amina was born in the middle of the sixteenth century CE to King Nikatau, the 22nd ruler of Zazzau, and Queen Bakwa Turunku (r. 1536–c. 1566). She had a younger sister named Zaria for whom the modern city of Zaria (Kaduna State) was renamed by the British in the early twentieth century. According to oral legends collected by anthropologist David E. Jones, Amina grew up in her grandfather's court and was favored by him. He carried her around court and instructed her carefully in political and military matters.

At age sixteen, Amina was named Magajiya (heir apparent), and was given forty female slaves (kuyanga). From an early age, Amina had a number of suitors attempt to marry her. Attempts to gain her hand included "a daily offer of ten slaves" from Makama and "fifty male slaves and fifty female slaves as well as fifty bags of white and blue cloth" from the Sarkin Kano.

After the death of her parents in or around 1566, Amina's brother became king of Zazzau. At this point, Amina had distinguished herself as a "leading warrior in her brother's cavalry" and gained notoriety for her military skills. She is still celebrated today in traditional Hausa praise songs as "Amina daughter of Nikatau, a woman as capable as a man that was able to lead men to war."

The exact circumstances of Amina's death are not known. The nineteenth-century Muslim scholar Dan Tafa says that "She died in a place called Attaagar. It was for this reason that the kingdom of Zazzau was the most extensive among the kingdoms of Hausa, since Bauchi included many regions." Drawing on Tafa's account, Sidney John Hogben reports that "Amina died in Atagara, near present day Idah, for at that time Amina had pushed the frontiers of Zazzau south of the Niger-Benue confluence. But there are many contradictions surrounding her death; many authors in their books cited that she died in Vom Jos while other historian said she died in Atagara, the present day Idah."
jiya

I have reached 900 followers! Thank you for your continued support. I could not have done it without each of you. 🙏🤗🎉
16/04/2023

I have reached 900 followers! Thank you for your continued support. I could not have done it without each of you. 🙏🤗🎉

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJI'UNA irin wannan ranace ta 06-02-2023 Al,ummar masarautar jama'are s**a kasance cikin al...
06/02/2023

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJI'UN

A irin wannan ranace ta 06-02-2023 Al,ummar masarautar jama'are s**a kasance cikin alheni, kaduwa, da kuma jimami na rashin jigo, jagora abin koyi, uba ga daukacin Al,ummar wannan masarautar jama'are HRH. Alhaji Dr. Ahmadu Muhammadu Wabi III, OON.

Tabbass tarihin marigayi uban kasa mai martaba sarkin jama'are zai cigaba da kasancewa a zukatan Al,ummar masarautar jama'are wajen koyar dasu kaunar juna da kuma wanzar da zaman lafiya.

Marigayi mai martaba sarkin jama'are HRH Alhaji Dr. Ahmadu Muhammadu Wabi, III OON ya kasance mutum nagari abin koyi, ga kyawawan halayensa masu kyau kamar su. Hakuri, dattaku, sarki ne maison Al,ummar karamci, adalci, kawaici, taimako, yakana, sanin yakamata, son Al,ummarsa girmama Al,umma, kaunar zaman lafiya, dadai sauran su.

A wannan ranace mukasan bango ya fadi a masarautar jama'are.

A wannan ranace mukasan jigo ya tafi yabar mu a masarautar jama'are

A wannan ranace zuciyar ta shiga cikin tashin hankali a masarautar jama'are

A wannan ranace al,ummar ta shiga cikin maraici

A wannan ranace idanuwan mu s**a zubar da kwalla marar misaltuwa.

Muna addu,a ya allah ya jaddada rahama ga bawan ka , ya ubangiji ka yafe masa kurakuransa ka bashi aljannah mafi Girma kasa idan tamu tazo mu ciki da kyakkyawar karshe.

Chief media to the jama'are emirate council. Engr Mahmood Ibrahim Jama'are [06-02-2023]

Allah yayiwa mai martaba sarkin Dutse rasuwa, Alh Dr Muhammadu Nuhu Sanusi, Kwamishinan ayyuka na musamman Alh Danladi s...
01/02/2023

Allah yayiwa mai martaba sarkin Dutse rasuwa, Alh Dr Muhammadu Nuhu Sanusi, Kwamishinan ayyuka na musamman Alh Danladi sankara ya sanar da haka cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a birnin Dutse,Yace za'ayi Jana'izar sa Gobe laraba idan Allah ya kaimu.
Allah ya jikan mai martaba🙏🙏

19/01/2023

NASIHA KYAUTA-:

1. WASA
idan yayi yawa yana kawo
SHAGALA.

2. SURUTU
idan yayi yawa yana kawo
KARYA

3. WAYEWA
idan tayi yawa tana kawo
KAUYANCHI

4. JAYAYYA
idan tayi yawa tana kawo
GABA.

5. SON DUKIYA
Idan yayi yawa yana kawo.
CHIN HARAM

6. WAYO
idan yayi yawa yana kawo.
ZALUNCHI.

7. KARFI
idan yayi yawa yana kawo
MUGUNTA.

8. ROKO
idan yayi yawa yana kawo
WULAKANCHI.

9. TUNANI
idan yayi yawa yana kawo
DAMUWA.

10. FUSHI
idan yayi yawa yana kawo
DANASANI.

11. JAHILCHI
idan yayi yawa yana kawo
KAFIRCHI.

12. RAGWANCHI
idan yayi yawa yana kawo
TALAUCHI.

13. SON MULKI
idan yayi yawa yana kawo
GIRMAN KAI.

14. SABON ALLAH
idan yayi yawa yana kawo
MUMUNAN KARSHE.

Allah yasa mu dace Duniya da Lahira-:

A yau ne Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto ya cika shekara 57 da rasuwa. 😭An kashe shi ne a ranar 15 ga watan Janairun ...
16/01/2023

A yau ne Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto ya cika shekara 57 da rasuwa. 😭
An kashe shi ne a ranar 15 ga watan Janairun shekarar 1966 a Kaduna.
Wane darasi ne kuke ganin shugabannin zamanin nan ya kamata su koya daga marigayin?

.    Takaitaccen tarihin Abubakar Tafawa BalewaAn haifi Sir Abubakar Tafawa Balewa a garin Tafawa Balewa dake jihar Bauc...
15/01/2023

.
Takaitaccen tarihin Abubakar Tafawa Balewa
An haifi Sir Abubakar Tafawa Balewa a garin Tafawa Balewa dake jihar Bauchi a Arewa maso Gabashin Najeriya a shekarar 1912.

Ya kasance mutum mai da'a da kuma asali kasancewar mahaifinsa ma'aikaci ne ga hakimin garin.

Yayi karatu a makarantar horon malamai ta Katsina daga ( 1928 zuwa 1933), sannan ya zamo malami, kuma shugaban makarantar Bauchi Middle School.

Yayi karatu a makarantar horas da malamai ta London daga ( 1945 zuwa 1946), inda ya samu shaidar malanta.

A lokacin yakin duniya na biyu ya nuna sha'awarsa ta shiga harkokin siyasa, inda ya kafa zauren tattaunawa na Bauchi Discussion Circle.

Sannan daga bisani ya shiga siyasar malamai inda aka zabe shi mataimakin shugaban kungiyar malaman Arewa.

A shekarar 1952 ya zamo ministan ayyuka na Najeriya, ministan sufuri a 1954, sannan ya zamo jagoran jam'iyyar NPC a majalisar wakilai ta kasa.

Ya zamo Fira Ministan farko na Najeriya bayan da kasar ta samu 'yancin kai a shekarar 1960.

A shekarar 1966, wasu sojoji s**a yi kokarin juyin mulki inda anan ne aka sace shi kafin daga bisani aka kashe marigayi Sir Abubakar Tafawa Balewa.
Allah ya jikan kan mazan jiya, Allah yasa shugaban bannin mu na yanxu suyi koyi da irin halin ka amin

I've just reached 100 followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏...
15/01/2023

I've just reached 100 followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏🤗🎉

YANZU-YANZU: Kotun Alkali Sarki Yola   ta yankéwa Sheíkh Abduljabbar Sheíkh Nasíru Kabara hukuncín kísa ta hanyar rataya...
15/12/2022

YANZU-YANZU: Kotun Alkali Sarki Yola ta yankéwa Sheíkh Abduljabbar Sheíkh Nasíru Kabara hukuncín kísa ta hanyar rataya.

Bisa laifin kalamun batanci ga Annabi MUHAMMADU (S A W) Allah ya karawa annabi amin.

08/12/2022

Assalamu Alaikum warahamatulhi wa barakatuh ina mai farin ciki sanar da ku mun bude wanna shafi(page) domin kawo muku tarihin ma gabatanmun wato shugaban gasar mu dakuma sarakunan Kasar mu

Address

BAUCHI
Jama'are
740102

Telephone

+2348109916929

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MAZAN JIYA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to MAZAN JIYA:

Videos

Share


Other News & Media Websites in Jama'are

Show All