LDM Radio & Tv

LDM Radio & Tv LDM Source NG Hausa Sabuwar Gidan Jarida ce Dake Arewa Maso Gabas Dazata Dinga Kawo muku Sahihan La

♥️♥️♥️mr❤️❤️mss✊✊❤️♥️ today the best kannywood celebrities 💋💋 with Hausa 📷 🙏💋🙏💚 📷📸💪✌️🥑✍️😜💚💋💋💯🙏✊💯
27/01/2024

♥️♥️♥️mr❤️❤️mss✊✊❤️♥️ today the best kannywood celebrities 💋💋 with Hausa 📷 🙏💋🙏💚 📷📸💪✌️🥑✍️😜💚💋💋💯🙏✊💯

♥️♥️♥️mr❤️❤️mss✊✊❤️♥️ today the best kannywood celebrities 💋💋 with Hausa 📷 🙏💋🙏💚 📷📸💪✌️🥑✍️😜💚💋💋💯🙏✊💯
20/12/2023

♥️♥️♥️mr❤️❤️mss✊✊❤️♥️ today the best kannywood celebrities 💋💋 with Hausa 📷 🙏💋🙏💚 📷📸💪✌️🥑✍️😜💚💋💋💯🙏✊💯

Bayanin gaskiya game da batun rufe bankunan Online da s**a hada da; Opay, Palmpay, Moniepoint, Kuda, Wema da sauran su. ...
08/12/2023

Bayanin gaskiya game da batun rufe bankunan Online da s**a hada da; Opay, Palmpay, Moniepoint, Kuda, Wema da sauran su.

A makon da ya gabata babban bankin Najeriya ya bawa bankunan ajiyar kudi (DMBs) umurnin rufe duk wani asusun ajiyar kudi da ba shi da BVN da NIN daga farkon shekara mai zuwa.

Da yawan bankunan Online irin su Opay, Palmpay, da Kuda na ba mutane damar bude asusu ta hanyar amfani da lambar waya kawai, ba tare da sanya BVN ko NIN ba.

Sabanin bankuna na zahiri da sai kana da BVN da NIN, amma bankunan Online sun takaita shiga ko fitar kudi akan Naira dubu hamsin a asusu mai matakin tsaro na farko.

Sai dai CBN ya fitar da sanarwar da ke cewa: "Dole ne duk masu asusun ajiyar kudi da ke da matakin tsaro na farko ya makala BVN da NIN, kamar yadda yake dole masu mataki na biyu da uku su saka BVN da NIN, gaza hakan zai sa a rufe asusun."

Wannan sanarwa ta saka anata yada labari a kafofin sada zumunta cewa za'a rufe dukkannin Bankunan Online, duba da cewa suna bada damar ana bude asusu ba tare da an saka BVN ko NIN ba.

Wannan chakwakiyar ta shafi bankuna irin su Opay, Palmpay, Kuda da sauran bankunan Online masu yawan gaske, amma bata shafi bankunan Moniepoint da Wema Bank da sauran manyan bankunan zahiri ba.

A yanzu ya zama dole ga kowane bankin Online da ya bukaci BVN da NIN akan kowane asusun ajiyar da aka bude a cikin shi ko kuma a rufe shi.

Itama fadar shugaban kasa ta karyata labarin cewa, za'a rufe dukkannin Bankunan Online, sai dai tace kowane Banki dole yabi tsarin da Gwamnati ta kawo.

A yanzu haka cikin kwanakin nan, bankunan zahiri da dama sun daina nuna bankunan Online idan za'a tura kudi, wanda yake nuni da cewa suna kokarin katse alaka dasu.

Sannan akwai yiwuwar karawa Bankunan Online haraji, wanda hakan zaisa su fara cire Charges mai yawa ga masu ta'ammuli da bankunan.

✍️ Comr Abba Sani Pantami

Sarkin Roma Maximillian na 1 ya sa waɗannan safofin hannu masu sulke tun daga 1508 har zuwa mutuwarsaWadannan kyawawan s...
05/12/2023

Sarkin Roma Maximillian na 1 ya sa waɗannan safofin hannu masu sulke tun daga 1508 har zuwa mutuwarsa

Wadannan kyawawan safofin karfe da Maximilian na I Sarkin Roma ke sawa, wani nau'in safar hannu ne da sojoji da mayaka daga ko'ina cikin duniya ke sawa a tsakiyar zamanai.

Wadannan safofin hannu na karfe su na kare hannayen mutane da hannayen sojoji. Akwai nau'ikan Wadannan irin sarar da yawa, amna ba duka suke da da kyau kamar waɗannan ba.

Wasu daga cikin waɗannan “safofin hannu na yaƙi” an yi su ne da fata, wasu na ƙarfe ne, wasu kuma saƙar sarƙoƙi ne.

Ana tsammanin Maximilian I na sanye da safofin hannu har zuwa mutuwarsa a shekara ta 1519.

Innalillahi Wainnah Ilaihir raji'un 😭Allah yayiwa Shugaban Karamar Hukumar Gombe Rasuwa Alh Ali Usman Haruna (Ali Ashaka...
05/12/2023

Innalillahi Wainnah Ilaihir raji'un 😭

Allah yayiwa Shugaban Karamar Hukumar Gombe Rasuwa Alh Ali Usman Haruna (Ali Ashaka)

Allah Yajikansa yagafarta masa

✍️ Rabi'u B Goroo,

An Binne Mutum 80 Bayan Harin Jirgin Soji Kan Masu MauludiMutanen da s**a tsallake rijiya da baya a harin bom da jirin s...
05/12/2023

An Binne Mutum 80 Bayan Harin Jirgin Soji Kan Masu Mauludi

Mutanen da s**a tsallake rijiya da baya a harin bom da jirin sojin kasan Najeriya ya kai wa masu taron Mauludi sun tabbatar da yin jana’izar sama da mutum 80.

Wani mazaunin yankin mai suna Liman ya ce sun binne sama da mutum 90, wasu a cikin buhu.

Ya ce akwai wani magidanci da ya rasa matansa biyu da yaya, sai jariri daya da ya tsallake rijiya da baya a harin.

Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta dauki alhakin harin, wanda ta ce jirginta ne ya kai harin kan fararen hula bisa kuskure a lokacin da yake sintirin yaki da ’yan ta’adda.

Yankin Tudun Biri dai na kusa ne hanyar Birnin Gwari, a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya da ke fama da matsalar hare-haren da ke wa mutane kisan gilla da kuma garkuwa da su domin karbar kudin fansa.

Mutane 30 s**a mutu a harin jirgin sojin saman Najeriya kan masu Maulidi a KadunaMutane da dama ne ake fargabar sun rasa...
04/12/2023

Mutane 30 s**a mutu a harin jirgin sojin saman Najeriya kan masu Maulidi a Kaduna

Mutane da dama ne ake fargabar sun rasa ransu sakamakon fashewar wani bam, da ake zargin wani jirgin saman sojojin saman Najeriya ne ya jefa musu, a lokacin da suke gudanar da bukin Mauludi a unguwar Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.

Duk da cewar babu gamsassun bayanai kan lamarin, amma wasu mazauna garin sun ce mutane 30 sun mutu a hadarin daya faru da cikin daren jiya Lahadi.

“Mutane sun taru suna gudanar da Maulidi sai jirgin sama ya jefa musu bom, wanda yayi sanadiyar mutuwar sama da mutane 30 nan take.”

Sai dai wasu rahotanni na nuna cewar akwai yuwar adadin wadanda s**a rasa rayukansu ya zarce 50.

Bayan faruwar lamarin, wasu daga cikin mazauna garin sunyi gudun hijira zuwa makwabtansa, saboda tsoron kar wasu hare-hare su biyo bayansa.

Kawo yanzu dai gwamnatin jahar Kaduna da kuma rundunar sojojin saman Najeriya ba su ce komai kan lamarin ba, duk da dai wasu rahotanni na nuna cewar gwamnatin Jahar ta kira taron tsaro na gaggawa wanda mataimakiyar gwamnan Jahar Dr Hadiza Balarabe ke jagoranta.

Jama’a dan Allah a taimaka a tayamu sa ido, kuma ayi mana share duk inda akaga wannan motar yanzu ba’ayi awa daya da sac...
16/10/2023

Jama’a dan Allah a taimaka a tayamu sa ido, kuma ayi mana share duk inda akaga wannan motar yanzu ba’ayi awa daya da sace ta a kofar gida mu sabuwar mandawari layin ulumu number motar 06 A12 KN idan Allah yasa an ganta za'a iya tuntubar wannan number
0803 692 0304
08138221712

CIKIYYA!!! CIKIYYA!!! CIKIYYA!!Anacikiyar Wannan Yaro Dankimanin Shekara 7 maisuna Mujaheed Yabatane Anguwar Barunde Dak...
30/09/2023

CIKIYYA!!! CIKIYYA!!! CIKIYYA!!

Anacikiyar Wannan Yaro Dankimanin Shekara 7 maisuna Mujaheed Yabatane Anguwar Barunde Dake kwaryar Jahar Gombe da Yanmacin Jiya Juma'a Ana Rokon Duk Wadda Allah Yasa Yansa Yakhaishi Gidan Mai Anguwar Barunde kokuma Ofishin Yansanda Mafi kusa

Kokuma Ya Tuntumemu Akan Wannan Numbers kamar Haka:
08035997825
09137926008
08149675978
Don Allah Mutane Atayamu Da Shearing ko Allah zaisa Adace 😭
Allah Yasa Mudace 🙏

Ka Fara Bincikar Kanka, Ma'aikatanka Da Ministocinka Da Gwamnoni Na Buhari Kafin Kace Zaka Yi Wani Bincike; Cewar Gamayy...
19/05/2023

Ka Fara Bincikar Kanka, Ma'aikatanka Da Ministocinka Da Gwamnoni Na Buhari Kafin Kace Zaka Yi Wani Bincike; Cewar Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya
.... Ya zama dole ka fara titsiye kanka da ma'aikatanka tare da ministocin da ka baiwa mukamai har da gwamoninka.

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya, kamar yadda ta saba, ta bayyana damuwarta game da karuwar rashin tabbas da wasu masu tayar da kayar baya ke kokarin haifarwa a kasar yayin da ake kokarin mika mulki a watan Mayun 2023 zuwa sabuwar gwamnatin da aka zaba ta hanyar tsarin zabe na dimokiradiyya a watan Fabrairun 2023.

Mun lura da cewa wadannan abubuwan sun yi daban-daban daga aiyukan babbar kungiyar tsaro ta kasa, DSS, babban kwamandan sojoji da rundunar ‘yan sandan Najeriya ba tare da an samar da wasu matakan da za a dauka don dakile su ba.

Kungiyar ta CNG ta kuma damu da rahotannin da ke cewa wasu manyan jami’an gwamnatin mai barin gado na shirin barin kasar gabanin mika mulki, ko shakka babu a wani yunkuri na yin rufa-rufa a kan rashin da’ar da s**a yi a ofis da kuma gudun kada a gurfanar da su a gaban kuliya. Mun damu matuka da rahotannin da ke cewa Godwin Emefiele wanda ya rike daya daga cikin manyan ofisoshi a kasar nan a matsayin Gwamnan Babban Bankin Najeriya a tsawon shekarun da Najeriya ta yi fama da tabarbarewar tattalin arziki da tabarbarewar kudi, na cikin wadanda ke shirin yin gudun hijira zuwa kasashen waje.

INA GANIN BABU WANI ABIN KUSKURE IDAN MACE TA FARA CEWA TANA SON NAMIJI.Ni da kaina da wasu mutane kusan kaso Casa'in da...
11/05/2023

INA GANIN BABU WANI ABIN KUSKURE IDAN MACE TA FARA CEWA TANA SON NAMIJI.

Ni da kaina da wasu mutane kusan kaso Casa'in da Biyar bisa ɗari mun yarda namiji kaɗai ne ya dace idan yaga macen da yake so zai iya ya same ta ya faɗa mata babu laifi kuma ba abin kunya bane.

Lokaci da dama nauyin baki na ja ma mata da yawa su kasa samun namijin da suke so wasu har ƙarshen rayuwar su.

Yayin da mace ta ga wani salihi mutumin kirki ƙilan wurin aikin sune ko abokin Yayan ta ko Malamin ta ko wani abokin hulɗa namiji mutumin kirki sai ta ga kamar ci baya ne ta furta tana son sa bare tayi wani yunƙurin da zai sa ta mallake shi.

Saɓanin namiji da zai iya ƙoƙarin sa domin mallakar wacce yake so idan ba a dace ba zai ƙara gaba ya nemi wata, ke ma babu inda aka hana ki, kika sani ma ko kece da kan ki za ki yi yunƙurin samun abokin rayuwa na dindin, idan ke kika gan shi kika zaɓa za ki iya jurewa a yi ta rayuwar cikin rufin asiri.

Nana Khadija RA ita ta fara ganin Manzon Allah SAW tace tana son sa, s**a yi aure da tarin zuriya mai albarka, don me wani zai saƙa maki abinda ba haramun ba ya zama abin kunya, shi kaɗai ne zaki iya rayuwa da shi tal babu ƙari, idan kun haɗu ki faɗa masa kina son sa Allah zai shiga lamarin ki idan kin yi domin sa, ki duba cancanta ba laifi ba ne.

Kina ta doguwar addu'a kina neman miji nagari yana ta giftawa ta gaban ki me k**e jira ne? Sai yayi wuf da wata kina nan zaune.

- GOLDEN PEN

LABARI DA DUMI DUMI Rahotanni daga jihar Kebbi na cewa wasu yan bijilanti sun hallaka rikakken dan bindigar nan mai suna...
11/05/2023

LABARI DA DUMI DUMI

Rahotanni daga jihar Kebbi na cewa wasu yan bijilanti sun hallaka rikakken dan bindigar nan mai suna 'Yalo' a garin Wasigu da ke karamar hukumar Danko.

Majiya: DCL Hausa

Yadda Bola Ahmed Tinubu Ya Jajirce Wajen Ceto Al'umma Daga Faɗawa Wani Hali Akan Maganar Chanjin Kuɗi. Ko mutum ya yarda...
30/01/2023

Yadda Bola Ahmed Tinubu Ya Jajirce Wajen Ceto Al'umma Daga Faɗawa Wani Hali Akan Maganar Chanjin Kuɗi.

Ko mutum ya yarda ko bai so ba, jajircewa ce da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya nuna wanda a kullum shine ya ceci talakan Najeriya daga radadin wa'adin farko da gwamnatin tarayya ta gindaya na musanya sabon kudin da ba a so.

Kuma ta wannan matakin na musamman, Tinubu ya kuma ceci al’ummar kasar daga tashe-tashen hankula sakamakon zazzafar bacin ran da jama’a s**a yi da shi kafin karin kwanaki 10 da gwamnati tayi.

Tinubu, ya sake tabbatar da kansa a matsayin babban jigo, a cikin wani jawabin da ya yi a Abeokuta a yanzu, ya dauki kwakkwaran matakin da ya dace na fadakar da jama’a kan illolin da ke tattare da sabuwar manufar dake tattare da sauyin Naira, da lokacinta da kuma wa’adinta.

Da alama dai shugaban ya caccaki Asiwaju ya kuma gayyaci Asiwaju zuwa Daura inda mutumin ya tsaya tsayin daka yana mai jaddada cewa manufar ba lallai ba ne, ba ta da farin jini kuma za ta cutar da talaka ne kawai ta kuma haifar da rikici.

Wannan jajircewa da jagoranci da Asiwaju ya nuna ne ya tilastawa gwamnati komawa kan matakin da ta dauka a baya.

Lallai al'umma na yiwa Tinubu matuƙar godiya saboda shiga da yayi tare da yin kasada da komai don ceton wani yanayi mara kyau.

𝔹𝔸ℝ𝔸𝕎𝕆 𝔻𝔸 𝕊𝕌ℕ𝔸ℕ 𝕄𝔸𝕃𝕌ℕ𝕋𝔸 Daga Ismail Bn Tahir Abdullahi.Yan uwa wanna da kuke gani acikin wannan hoton BARAWO Muna ne man...
22/09/2022

𝔹𝔸ℝ𝔸𝕎𝕆 𝔻𝔸 𝕊𝕌ℕ𝔸ℕ 𝕄𝔸𝕃𝕌ℕ𝕋𝔸
Daga Ismail Bn Tahir Abdullahi.

Yan uwa wanna da kuke gani acikin wannan hoton BARAWO Muna ne manshi (Wanted).

Sunan shi: KABIRU MUSA NUHU

Yazo makarantar mu dasunan Yana neman aikin karantarwa, bayan an bashi aiki. Fara karantarwar shi keda wuya yace wa yaran SS3 gobe kowa yazo da waya ko ya aro waya Mai babban RAM zasuyi practical, bayan sun kawo wayoyi washe gari, sai ya karba ya fita dasu ya gudu batare da sani kowa ba .

Wanda kimanin kudin wayoyin yakai 400k plus.

Duk Wanda yasani shi pls Dan Allah yayi mana bayani inda zamu sameshi.

Dan haka muke baiwa masu makaranti shawari, karda su dauki malami batare da Wanda zai mashi grantor ba, Dan yanzu mutane sun canza.

Allah ya tuna asirin shi

07/09/2022

GWAJIN KAYAN AIKI

CIKIN SU WA ZAKU ZABA SHUGABANCIN NIGERIA1. Atiku2. Peter Obi3. Kwankwaso4. Tinibu Bari Muga Wanda yafi masoya ?
06/09/2022

CIKIN SU WA ZAKU ZABA SHUGABANCIN NIGERIA

1. Atiku
2. Peter Obi
3. Kwankwaso
4. Tinibu

Bari Muga Wanda yafi masoya ?

Zaku iya kallon shirin tumbin giwa kai tsaye a youtube channel din mu kuma zaku iya aika sakonninku kai tsaye a shafin a...
05/09/2022

Zaku iya kallon shirin tumbin giwa kai tsaye a youtube channel din mu kuma zaku iya aika sakonninku kai tsaye a shafin amana subscribing da like.

👇👇👇

This is official YouTube channel of the Progress Media Broadcasting services.

ALLAHU AKBAR! 😭Wannan gawar da kuke gani gawar wata baiwar Allah ce wadda Allah yayma rasuwa jiya garin Jos  a Gada-Biyu...
03/09/2022

ALLAHU AKBAR! 😭

Wannan gawar da kuke gani gawar wata baiwar Allah ce wadda Allah yayma rasuwa jiya garin Jos a Gada-Biyu

Matar takasance ita kadai ce musulma maiyin sallah aduk cikin duka dangin ta kuma a unguwar da take ma babu musulmai ko mutum daya da yake Rayuwa a yankin wajen

Kafin mutuwar ta tabar wasiyya ga yaranta Akan cewar inta mutu su dauki gawarta s**aita wajen musulmai dan suyi mata sutura d sallah, irin na addinin muslumci.

Yau Allah ya amshi rayuwar ta kuma bayan mutuwar ta yaranta s**aje office din JAMA'ATUL NASRIL ISLAM JOS wanda yake central mosque ta garin sai s**a sanar dasu wannan wasiyya data bari.

Alhamdullah cikin sauri da mutimtawa jama'atu ta tura yan agaji s**aje s**a dauko gawar tata aka suturta'ta dayi mata sallah kana kuma aka tara mutane s**a kaita makwanci kamar dai yanda addini musulinci ya tanadar.

Lallai Addinin musulinci na kowa ne

Ubangiji Allah yay mata rahama, Allah ya gafarta Mata, Allah yasa Annabi ya karbi bakoncinta.

Daga| It'z Kamalancy
3/9/2022

Yadda aikin rusau ke gudana a kasuwar Kantin Kwari bayan umarnin Gwamna Ganduje.📸
02/09/2022

Yadda aikin rusau ke gudana a kasuwar Kantin Kwari bayan umarnin Gwamna Ganduje.

📸

MAFARKINAko wani Dan Adam yana buri ta musamman da yakeson yaga ya cinma a rayuwarsa na duniya.Tun daga tashiwana Har zu...
31/08/2022

MAFARKINA

ko wani Dan Adam yana buri ta musamman da yakeson yaga ya cinma a rayuwarsa na duniya.
Tun daga tashiwana Har zuwa rana kamar yau burina ko ince mafarkina bai can a ba akan kudirina.

✍️Ayuba Yunusa Mai Kalamai

Rayuwata Ina ginata ne bisa tsarina sannan Ina tafiyar da ita dai-dai da tarbiyata hakkan yasa Bana tsawwala WA kaina ko wani na, domin Ina la'akari da abubuwa kamar haka. Mai nene asalina, kuma menene darajar asalina a gareni hakan yasa bana taba shiga wata garari dalili kuwa Ina tafiyar da komai yadda ubangiji ya tsarani akai.
Ni daga usulini masu rufin asari sannan tarbiyata alhamadullah, sannan abubuwa mafi girma da nake girmamawa a tattare da rayuwata sune iyayena, Yan uwana, al'umma, masoyana. Domin duk Sanda zan roki ubangiji wani abu suma Sai na roka masu abun.

Babban mafarkina shine taimakawa al'umma ta siga da dama Hakan yasa nake da wata buri ta mussaman Tun daga tasowa na har zuwa rana Mai kamar ta yau ta Gina GIDAUNIYA wacce zata shahara wajen taimakawa al'umma a fadin afrika gabaki bama nijeriya kadai ba.
Na fito da wannan mafarkina nawa ne domin kuyimun kyakyawar addu'a da kuma fatan wannan burin nawa ya cika.
Ina alfahari da al'umma Hakan yasa nake matukar sha'awar ganin nima na zamo sanadiyar murmushi da fafun cikin su.

Allah Ina rokonka da kyawawan sunayenka, da girman zatinka, darajar fiyayyen halitta muhammadu Rasulillah S. A. W ka cikamin wannan mafarkin nawa.

Amin🙏🙏🙏

DA DUMI-DUMIN SA: Gwamnatin Jihar Gombe Zata Daina Biyan Malaman Jami’ar Jihar Gombe Albashin Su Muddin Basu Koma Aiki B...
29/08/2022

DA DUMI-DUMIN SA: Gwamnatin Jihar Gombe Zata Daina Biyan Malaman Jami’ar Jihar Gombe Albashin Su Muddin Basu Koma Aiki Ba

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Mai girma Gwamnan jihar gombe ya bayyana cewa, tun daga lokacin da kungiyar ASUU, ta fara yajin-aiki ake biyan malaman jami'ar jihar gombe albashin su, ba tare da sun yi aiki ba.

Muhammadu Inuwa Yahaya yace, zai dakatar da albashin malaman jami’arsa idan s**a ki dawowa aiki.

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya Kara da cewa duk tsawon watanni shida malaman jami’ar jihar Gombe ta GSU suke yajin-aiki, kuma ana biyansu kudi.

An gagara shawo kan ASUU a GSU A cewarsa, an yi kokarin tattaunawa da shugabannin jami’ar ta GSU da kuma reshen kungiyar ASUU na malaman jami’ar GSU, amma an gaza samun mafita.

Idan har malaman sun ki bude jami’ar domin a cigaba da karantar da yara kamar yadda aka bada umarni, gwamnatin jihar Gombe za ta daina biyan su albashi.

Gwamnan ya bayyana yadda yake biyan ma’aikatan jihar da ‘yan fansho albashinsu duk ranar 25 da 27 na kowane wata tun da ya zama gwamna.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN 😭😍😭Matashin Injiniya Khalil M. Khalil Ya R@suAllah Ya Yi Wa Matashin Injiniya Dake Ai...
29/08/2022

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN 😭😍😭

Matashin Injiniya Khalil M. Khalil Ya R@su

Allah Ya Yi Wa Matashin Injiniya Dake Aiki A Kamfanin Mai Na Ƙasa (NNPC) R@suwa Sakamakon Hatsarin Mota Da Ya Yi Akan Hanyarsa Ta Katsina Zuwa Kaduna.

Allah Ya Jikansa Da Rahama!

DAGA Jamilu Dabawa, Katsina

Address

Pantami Near Water Board
Gombe
17100

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when LDM Radio & Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to LDM Radio & Tv:

Videos

Share


Other Broadcasting & media production in Gombe

Show All