14/06/2021
Dr. Mansur Sokoto
,
Bala'i ya tashi zai yi tafiya, sai ya nemi abokin tafiya.
Ciwo ya ce zan bi ka. Bala'i ya ce ban yarda da kai ba. Domin kai da an sha magani sai ka bace, kuma wanda duk ka shafe shi, zai samu lada.
,
Gobara tazo ta ce za ta bi shi, sai ya ce, ban aminta da ke ba. Domin ke idan kin gama aiki sai a sake share wuri aci gaba da rayuwa.
,
Sai ga Bashi ya iso yana yi wa kansa kirari: Ni ke hana mutum barci, in hana shi zuwa masallaci, in sakar masa ciwo marar dalili, in sa shi karya da saba alkawari, in jefa shi gidan kaso, in ya mutu in gaji gidansa da iyalinsa, sannan ba zan barshi ba sai na tsaya da shi wurin hisabi a gaban Allah.,
Nan take Bala'i ya ce zo mu tafi tare, tabbas kai ne abokin tafiyata. Babu abokin tafiya in ba kai ba.
,
Ya Allahu Ya Ar-razzaku Ya Al-wahhabu ka raba mu da musibar bashi.