Matashin ɗan Badan wanda ake zargi da yi wa wani abokin faɗansa yankan Rago da Zarto a unguwar Ɗorayi da ke birnin Kano, ya ce lokacin da ya aikata kisan sai da imaninsa ya fita.
Tini dai rundunar Ƴansandan Kano ta kama matashin wanda ya yi yunƙurin tserewa zuwa ƙasar Nijar.
Bidiyo: Abdullahi Haruna Kiyawa/Facebook
Yadda al'ummar musulmai ke halartar tafsirin Alƙur'ani mai girma a fadar Sarki Kano tsawon kwanakin Azumin watan Ramadan.
Rukunin kamfanonin M.Abba Trading Company da M.Abba Gallery da kuma M.Abba Textiles, M.Abba Perfume Incense, suna yi muku barka da Azumin watan Ramadan da fatan za kammala lafiya, tare da yin idaba karɓarɓiya.
Abinda ya sa na yi waƙar "na samu fara, mulkin Tinubu"- Mawaƙi Usman.
Mawaƙin wanda ɗan asalin jihar Bauchi ne mazaunin birnin Kano mai suna Usman Ahmad Adam wanda aka fi sani da Usman A Faggo, ya ce, a cikin waƙar tasa akwai darasi.
Mawaƙin ya kuma ce, ba ya yin adawa da gwamnatin Bola Ahmad Tinubu shugaban ƙasar Najeriya, amma ya ce, akwai buƙatar al'ummar ƙasar su gyara halayensu.
Me za ku ce?
Murja Kunya Ta Yi Nadama, Ba Za Ta Bijirewa Sharuɗan Bayar Da Belinta Ba- Rahoto.
Ayyukan Da Manzon Tsira Annabi Muhammad S.A.W Ke Yi A Kwanaki Goman Ƙarshen Watan Ramadan- Saƙon Mai Azumi.
Ƴan Arewacin Najeriya Ba Sa Yin Amfani DA Social Media Yadda Ya Kamata- Kwararre.
Mujaheed Ibrahim wanda kwararren mai amfani da kafafen sada zumunta ne ya bayyana mana yadda ya kamata a yi amfani da su.
Ku kalli karin bayanin sa.
"Kasuwancin Zamani" sabon shiri ne za mu dinga kawo muku shi, zai dinga mayar da hankali kan kasuwanci da taltalin arziƙi na zamani.
Yau ta cikin shirin mun tabo batun yadda kudin Internet za su danne na takarda a duniya, sai kuma batun Kirfto.
Ku biyo mu cikin shirin.
Kaf jam'iyyar NNPP babu wanda ya yi aikin da Aliyu Sani Madaki ya yi, ko Gwamna bai kai shi aiki ba.- Aliyu Zangina.
Ƴa'ƴan Jam'iyyar NNPP Kwankwasiyya a ƙaramar hukumar Dala na ci gaba da kokawa kan karbar wasu tshoffin kansiloli da jagororin jam'iyyar APC da suka fice zuwa mai kaya marmari.
Aliyu Muhammad Zangina ya ce da sake a lamarin, ga abinda ya shedawa shirin siyasa na "Inda Ba Ƙasa".
Me za ku ce?
An samun ƙaruwar mabuƙata ya yin da ake ci gaba da fuskantar tsadar rayuwa a Najeriya.
Shugaban wata gidauniya a jihar Bauchi Malam Ibrahim Muhammad Inuwa, ne ya bayyana wa Martaba FM hakan a wata zantawa da shi.
Mai yin fushi ko harsala zai iya samun matsala a cikin Azuminsa.
Malam Aminu Adamu Muhammad, na'ibin limamin masallacin Juma'a na Alfurƙan da ke birnin Kano, ya yi mana karin bayani kan illar fushi ga mai Azumi.
Saƙon Mai Azumi
Yau ta cikin shirin Saƙon Mai Azumi Malam Umar Ɗahiru Soron Ɗinki, Ya Yi Mana Ƙarin Bayani Kan Karatun Alƙur'ani mai girma a lokacin Azumi.
Manufofinmu sun yi daidai na gwamnatin jihar Kano, za mu kawo sauyi ga yadda ake tafiyar da ƙaramar hukumar Dala- Aminu Mamman Yaro.
Aminu Mamman Yaro, shugaban ƙungiyar Kwankwasiyya Dubai kuma ɗan takarar shugaban ƙaramar hukumar Dala da ke jihar Kano a Jam'iyyar NNPP ya bayyana mana manufofinsa na fitowa takara.
Ku kalli cikakkiyar hirarsa da mu ta cikin shirin "Inda Ba Ƙasa".
Me za ku ce?
Malamin addinin Musuluncin wanda limamin masallacin Juma'a ne a Kano ya bayyana mana cewa akwai buƙatar a ƙara zage dantse wanjen ayyukan alkairi a wannan goma ta biyu da masu Azumi suka shiga.
La'akari da tsadar rayuwa da ake fama da shi a Najeriya, Dakta Yahaya Khamis Idiris, ya ce Zai yi kyau a ƙara matsawa da addu'a domin neman sauƙi.
Ko dai mulkin shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu, ya fara fusata `yan jam`iyyar APCn jihar Kano ne?
"Muna addu`ar Allah ya shiryi gwamnatin Tinubu"- Sadik Shazali Ali Dala.
Matashin dan siyasar a jihar Kano ya roki mawadata da su dinga taimakaon marasa karfi musamman a wannnan lokaci na Azumi.
`Ya`yan jam`iyyar APC a jihar Kano na ci gaba da bayyana rashin gamsuwarsu da yadda gwamnatin NNPP karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf ke tafiyar da gwamnatin jihar.
Auwal Ibrahim, wanda ake kira da Bakaki Mai Goro tsohon SSA ne a gwamnatin Ganduje ya bayyana wa shirin Inda Ba Kaca cewa da sake.
Me za ku ce?
Wata kungiya da ke fafuukar kare namun daji da shi kansa gandun dajin da kuma da muhalli a jihar Bauchi da ke Arewa maso Gabashin Najeriya.
Daya daga cikin manyan jami`an kungiyar Amina Shehu Gadiya, ta yi mana karin bayani kan ayyukan kungiyar tasu.
An yi saukar karatun Al`kur`ani 30 domin neman Allah ya kawo sauki kan tsadar rayuwa da matsin taltalin arziki da ke fama da su a Najeriya da kuma rashin tsaro da sauran matsaloli musamman a jihar Kano.
gidauniyar Kassim Umar Warure Islamic, mai ayyukan taimakamawa marayu da marasa galihu da kuma koyar da karatun Al`kur`ani mai girma ce, ta shirya a masallacin gidauniyar da ke unguwar Tudun Yola a birni Kano a karashin jagorancin shugabanta Alhaji Muhammad Kasim Umar.
Shugaban gidauniyar taimakawa marayu da marasa galihuta ta OVPC Amb. Khalifa Sani Abdullahi, ya bayyanawa Martaba FM wani sabon shirin su da zai taimaka wajen bunkasa lafiya da kuma imili a Najeriya wanda suka yi hadin gwiwa da INSO.