Kasar Kano Jiya Da Yau

Kasar Kano Jiya Da Yau KASAR KANO JIYA DA YAU: Sanin Tarihinmu da Magabatanmu

15/06/2024

Labaran Yammacin Asabar 09/12/1445AH - 15/06/2024CE Ga Takaitattun Labaran.

Shugaba Tinubu ya bukaci babban daraktan hukumar sa ido a harkokin saye saye na gwamnati, BPP, Mamman Ahmadu ya yi murabus.

Rundunar Sojoji Kasa ta yaye sabbin sojoji 5,937 daga makarantar horas da kuratan sojoji da ke zariya a yau Asabar.

NDLEA reshen Jihar Kano ta ce ta k**a kwayoyin Tramadol guda 230,600 da kuma wasu mutane 106 da ake zargi da hannu a fataucinsu a jihar Kano.

Rundunar 'yan sanda za ta sake nazarin sunayen sabbin 'yan sanda da za a ɗauka aiki.

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya zargi gwamnatin Ganduje da raba kan gidan dabo.

Hukumar Kula da 'yan Najeriya mazauna ƙetare NIDCOM, ta ce an mayar da 'yan matan ƙasar kimanin 10 da aka yi safararsu zuwa Ghana.

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya bayyana cewa ya hakura da hawan Sallah ne dan a samu zaman lafiya a fadin jihar.

Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya aike da saƙon fatan alheri ga Shugaba Tinubu da Gwamna Abba Kabir Yusuf, sak**akon bikin babbar sallah.

Gwamnan jihar Zamfara ya fadawa alkalai yadda ake hada-kai da kotu ana sakin ‘yan bindiga.

Duk da halin rashin tsaro a Najeriya, aƙalla sojoji 197 ne zasu tafi domin wanzar da zaman lafiya a kasar Gambia.

Kocin Super Eagles Finidi George ya yi murabus daga mukaminsa bayan rashin katabus a kungiyar.

An k**a wasu mutum sama da 100 da ake zargin sun shigo Saudiyya ba tare da izinin gwamnati ba.

Hukumomi a ƙasar Saudiyya sun bayyana cewa aƙalla maniyyata miliyan 1,833,164 ne s**a halarci aikin Hajjin 2024.

Alƙalin Alƙalan Kenya ya ce alƙaliyar da ɗan sanda ya harba a lokacin da take tsaka da jagorantar shari'a a mutu a asibiti.

Dakarun rundunar sojin Sudan sun kashe kwamandan RSF a al-Fasher.

Kotu a Jamhuriyar Benin ta jefa ƴan Nijar 3 da ta k**a kurkuku.

An sake zaɓar Ramaphosa a matsayin shugaban Afirka ta Kudu.

An buɗe taron zaman lafiyar Ukraine a Switzerland ba tare da wakilcin Rasha ba.

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta sanar da mutuwar tsohon dan wasanta, Kevin Campbell bayan fama da jinya.

Euro: Switzerland ta sami nasara akan Hungry da ci 3:1 a wasan yau.

ALHAMDULILLAHYayin rabon kayan abinci kenan wadda kungiyar ANNASEEM_FOUNDATION ta garin ZAREWA take yi yanzu haka. A mas...
15/06/2024

ALHAMDULILLAH

Yayin rabon kayan abinci kenan wadda kungiyar ANNASEEM_FOUNDATION ta garin ZAREWA take yi yanzu haka. A masallacin juma'a na yan izala da ke hanyar fulatan Wanda akalla sama da mutane dubu ne za su rabauta da wanan tallafi wanda AA Rano yake badawa a rabawa al'ummar musulmi da ke wanan yanki na Zarewa dama sauran kauyukan da ke makwaftaka ta hannun wanan kungiya wato ANNASEM foundation.

15/06/2024

Labaran Safiyar Asabar 09/12/1445AH - 15/06/2024CE Ga Takaitattun Labaran.

Kwamishinonin da s**a yi aiki tare da tsohon Nasir El-Rufai sun yi watsi da rahoton majalisar dokokin jihar da ya yi zargin cewa kuɗi naira biliyan 423 zun zurare daga asusun jihar ba bisa ƙa'ida ba.

Allah ya yi wa Hajiya Asmau Ladan daga jihar Kaduna rasuwa a Makka.

Mahajjata za su kwashe wunin yau a Dutsen Arafat suna gudanar da addu'o'i, yayin da su kuma waɗanda ba su samu damar zuwa Hajji ba suke gudanar da azumin nafila don neman rabauta da wannan rana.

Dan majalisar wakilai Yusuf Gagdi daga jihar Plateau ya raba raguna 400 da ₦20 million a mazabar sa domin murnar sallah.

Amurka ta ƙaƙaba wa wata ƙungiyar Isra'ilawa masu ra'ayin riƙau takunkumi, saboda harin da takai da ya lalata kayan agajin da ake kai wa Gaza.

Jam'iyyun ANC da DA sun amince da kafa gwamnatin haɗaka a Afirka ta Kudu.

Ana sa ran cewa za a kwashe mako uku ana fama da ƙarancin lantarki a wasu sassa na ƙasar Ghana sanadiyyar raguwar ƙarfin lantarki da ƙasar ke samu daga Najeriya.

An zaɓi Thoko Didiza a matsayin kakakin majalisar Afirka ta Kudu.

Malaman Kwalejojin ilimi a Ghana sun tsunduma yajin aiki.

Shugaban Rasha ya ce dole ne Ukraine ta janye dakarunta daga yankunan da Rasha ta yi iƙirarin ƙwacewa kafin a fara tsagaita wuta, wani ƙuduri da shugaban Ukraine ya kira ''buƙata irin ta Hi**er''.

Amurka da Ukraine sun ƙulla yarjejeniyar tsaro ta shekaru 10.

Mali ta sallami kocin tawagar ƙwallon ƙafarta Eric Chelle.

Hukumar ƙwallon ƙafar Najeriya za ta ɗauko koci daga kasar waje.

Euro: Germany ta sami nasara akan Scotland da ci 5:1 a wasan jiya.

ALLAHU AKBAR:  Annabi S.A.W ya yi Khuɗubar Ƙarshe Ga Al-Ummarsa A Rana Irin Ta Yau Arafat 9 Ga Watan Zul-HijjaAnnabi Muh...
15/06/2024

ALLAHU AKBAR:

Annabi S.A.W ya yi Khuɗubar Ƙarshe Ga Al-Ummarsa A Rana Irin Ta Yau Arafat 9 Ga Watan Zul-Hijja

Annabi Muhammad S.A.W yayi khuɗubar ta ƙarshe ga al-ummarsa a ranar Arafat 9 ga watan Zhul-Hijja, ya yi khuɗubar a shekarar10 bayan Hijrarsa daga Makkah zuwa Madina.

Ya gudanar da Khuɗubar a saman Dutsen Arafat, wadda wannan khuɗubar ta kasance khuɗubar ƙarshe ta Manzon Allah S.A.W, inda Fiyayyen Hallita ya cigaba da khuɗubantar da al-ummarsa cewa;

“Ya ku mutane! Ku bani hankalinku domin mai yiwuwa ba zan sake kasancewa da ku bayan wannan shekarar ba, saboda haka! ku saurari abin da nake gaya maku da kyau kuma ku isar da abin da zan gaya maku ga waɗanda basa wannan wuri a yau”.

“Ya ku Mutane! k**ar yadda kuka riƙi wannan Wata na Aikin Hajji da wannan rana ta Arfa, da kuma wannan gari na Makka da girma kuma abin tsarewa, to haka kuma ku riƙi ran Musulmi da dukiyoyinsu da girma abin karewa".

“Ku maida wa Mutane kayan da s**a baku Amana, kar ku cuci kowa, kar ku yi za
Rabiu Isah
Kasar kano jiya

15/06/2024

Duk wanda ya kyamaci Ilimi da sana'a, zai yi wa talauci tarba.

15/06/2024

ROƘON MUTANE ƘASƘANCI NE !!!

Idan ka tashi roƙo, to, ka je ta inda aka halatta maka ka yi roƙon...lallai ka sani cewa; akwai wata ƙofa da kullum a bude take, ba a rufe ta — kullum tana buɗe ne domin masu roƙo (masu buƙata) irinka da irina. Saboda haka, kar ka karkata zuwa ga ƙofar da ake rufe ta domin gujewa jin buƙatarka. Koda an buɗe maka ita, to, za a ƙosa da ci gaba da buɗe maka. Domin ba za a iya ɗorewa ga biya maka buƙata ba.

Amma ka ga ƙofar ALLAH a kullum a bude take domin ita an tanada ta ne wa masu rauni da kuma masu neman tsayuwa ga abin da Allah ne ke horewa. Don haka, masu buƙata har ma da masu neman ƙari, ƙofa ce ga kowa. Allah ba ya rufe ta, sai dai bawa ya rufe ta ga kansa (ya gujewa kansa neman buƙata daga wajen Allah).

Kasar Kano Jiya Da Yau

Ranar Arfa:Ranar da aka kammala mana Addininmu.Kasar Kano Jiya Da Yau
15/06/2024

Ranar Arfa:
Ranar da aka kammala mana Addininmu.

Kasar Kano Jiya Da Yau

15/06/2024

Wanda yake yi wa Mahaifansa addu'a a bayan kowani Sallah, zai tashi cikin ƴaƴa masu ɗa'a a ranar tashin kiyama.

Ƙasar Kano Jiya Da Yau

15/06/2024

Ka keɓanci lokaci na musamman. Ka ƙudurta yinin Arfa. Ka roƙi dukkan buƙata. Wallahi, Allah (SWT) zai amsa maka.

Kasar Kano Jiya Da Yau

15/06/2024
15/06/2024

Barkanmu da warhaka! Dafatan mun yi sahur lafiya. Allah ya sadamu da alheren da ke cikin wannan rana mai tarin albarka. Allah ya yaye mana ƙunci da damuwa. Na gida dana asibiti Allah ya basu lafiya.

Kasar Kano Jiya Da Yau

Mahajjata sun shiga mataki na farko na aikin Hajji yayin da s**a taru a Mina da ke wajen birnin Makkah kafin su wuce zuw...
14/06/2024

Mahajjata sun shiga mataki na farko na aikin Hajji yayin da s**a taru a Mina da ke wajen birnin Makkah kafin su wuce zuwa filin Arafa ranar Asabar domin tsayuwar Arafa wadda ita ce ƙololuwar aikin Hajjin.

Dubban mahajjatan dai na ya da zango a shemomin da aka tanada kafin su ƙarasa wajen tsayuwar.

14/06/2024

Yau ranar masu bada jini ta duniya. (World Blood Donor Day) Sau nawa ka bada jininka a diba?

Dan majalisa yasha duka a hannun Al,umar yankinsa.Dan majalisar wakilai a Nigeria me wakiltar Kananan hukumomin Ifelodun...
14/06/2024

Dan majalisa yasha duka a hannun Al,umar yankinsa.

Dan majalisar wakilai a Nigeria me wakiltar Kananan hukumomin Ifelodun/Boripe/Odo-Otin na Jihar Osun Hon. Olusoji Adetunji, ya fuskanci cin zarafi a yankinsa bayan ya shiga Mazabarsa.

Wani Vedio dayake yawo a kafafen Sada zumunta ya Nuna yanda aka kaiwa Dan majalisar da tawagarsa hari bisa zarginsa dayin wasa rai-rai da walwalarsu acikin wannan yanayi na kunci da tsadar rayuwa duk dacewa sun bashi kuri-un das**a kaishi cikin majalisar korayen kujeru.

Wannan itace KABA wadda ake yin Tabarma da ita,  kuma da ita akeyin Gurumfa,  anayin Tabarma kala biyu da ita akwai taba...
14/06/2024

Wannan itace KABA wadda ake yin Tabarma da ita, kuma da ita akeyin Gurumfa, anayin Tabarma kala biyu da ita akwai tabarmar kaba da akece mata KARAUNI, akwai kuma wadda akece mata MALAFA, sannan ita wannan KABA din ana sa mata KALA ma'ana ana Rina ta ta koma wata kalar ko Ja ko Baki ko Koriya duk irin yanda akeso za a iya sa mata. Yayin zantawar mu da ita Hajiya Hana mai tabarma ta shaidamin cewa ita tanayin tabarma wacce akafi sani da MALAFA kuma tana Rina ta kala kala k**ar yanda ta nunamin da kuma yanda take saqar. Ga dai kadan daga cikin hutunan dana dauko yayin zantawar mu da ita.

Kasar Kano Jiya Da Yau

Wani jami-in hukumar Yan sanda ya yima kansa Karin matsayi daga matakin Corporal zuwa SP.Hukumar Yan sanda ta kasa shiyy...
14/06/2024

Wani jami-in hukumar Yan sanda ya yima kansa Karin matsayi daga matakin Corporal zuwa SP.

Hukumar Yan sanda ta kasa shiyyar jihar Cross Rivers ta tsare Wani Jami-inta Corporal Buba Adamu bayan samunsa da laifin Karawa kansa matsayi zuwa matsayin Superintendent of police (SP) dakuma kin yin reporting bayan an mayar dashi helikwatar hukumar shiyyar jihar Kaduna tun 2015.

Tsararren jami-in ana zarginsa da aikata laifuka ta hanyar amfani da kakinsa a Calabar babban Birnin jihar ta Cross Rivers dakuma yin Sojan gona.

Corporal Adamu Ya yima kansa Karin matsayi zuwa matakin Superintendent of police (SP), Sannan anyimasa canjin gurin aiki daga Calabar zuwa Kaduna tun a Shekarar 2015 tun daga lokacin yake gudanar da miyagun ayyukansa a matsayin SP a cikin Birnin Calabar batare dayaje yayi reporting
a sabuwar jiharsa ta Kaduna ba bakuma yazuwa Ziyarar tsohuwar Helikwatar sa ta Cross Rivers.

duk tsawon wannan lokacin na Shekaru 9 corporal Adamu Yana samun albashinsa.

Asirin Corporal Adamu ya tonune bayan dawasu Yan kabilar Hausa/Fulani mazauna Calabar s**a bara bayan sun fada komarsa.

SP Irene Ugbo jami-in Hulda da k**a,a na hukumar ta jihar Cross Rivers shine ya tabbar da kamu dakuma tsare Corporal Adamu.

Labaran Safiyar Juma'a 08/12/1445AH - 14/06/2024CE Ga Takaitattun Labaran.Shugaba Tinubu ya karbo bashin $2.25bn daga Ba...
14/06/2024

Labaran Safiyar Juma'a 08/12/1445AH - 14/06/2024CE Ga Takaitattun Labaran.

Shugaba Tinubu ya karbo bashin $2.25bn daga Bankin Duniya.

Majalisar wakilai ta mika bukatar gaggawa na sayen sababbin jiragen sama guda biyu domin amfanin shugaban kasa da mataimakin sa.

Kungiyar kwadago ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya tuntube ta kafin ya mika sabon mafi karancin albashi ga majalisar dokokin kasar.

Rundunar 'yan sandan birnin tarayya Abuja tace an fafata tsakanin jami'an tsaro da 'yan fashi a karamar hukumar Abaji Kwamishinan ‘yan sandan Abuja, CP Benneth Igweh, ya ce an yi nasarar kashe 'yan fashi biyu a yayin fafatawar.

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawan ya jaddada ƙudurin gwamnatinsa na rashin yin sulhu da 'yan bindiga.

Kwana 4 bayan sun zarge shi akan baya tabuka komai dan Majalisar Tarayya a jihar Osun, Soji Adetunji ya raba kekunan dinki da babura da injunan markade da talabijin domin jama'a su dogara da kansu a mazabarsa.

Wasu mazauna karamar hukmar Abaji dake Abuja sun kona gawar wani da ake zargin dan fashi da makami ne a ranar Alhamis.

’Yan fashi a banki sun harbe wani dan sanda mai muƙamin Sufeto har lahira a Abuja.

Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu Sokoto, ya amince da bai wa ma'aikatan jihar naira 30,000 a matsayin goron sallah.

'Yar shekara 27 a jihar Legas ta hada baki da saurayin ta cewa an sace ta kawai domin ta samu kuɗin fansa daga wurin mahaifiyar.

Kungiyar kananan kukumomin Najeriya (ALGON) ta ce zai yi wahala kananan hukumomi su iya biyan ma’aikata N62,000 a matsayin sabon mafi karancin albashi.

Majalisar Dinkin Duniya ta nemi dakarun Karta kwana na Sudan da su janye da ga kawanyar da su kaiwa wani birni a Dafur.

Ana tuhumar wani mutumin jihar Arizona dake Amurka da laifin safarar bindigogi don kashe bakar fata.

Ƙungiyar Ƙasashen G7 masu ƙarfin masana'antu sun amince a yi amfani da ribar kadarorin Rasha da aka ƙwace, domin bai wa Ukraine ta yi amfani da su.

Kotun Ƙolin Amurka ta amince da amfani da ƙwayoyin zubar da ciki.

Shugaban jam'iyyar EFF a Afirka ta Kudu, Julius Malema ya ce jam'iyyarsa ba za ta shiga gwamnatin haɗaka da ANC ke shirin kafawa ba.

Farashin dabbobi ya faɗi warwas a Nijar.

Wani jami'in dan sanda ya harbi Alkali a wata kotun majistare da ke Nairobi, ƙasar Kenya.

Wata kotu a Ƙasar Benin ta tsare wasu ƴan Nijar kafin yanke musu hukunci.

HAUSA IGBO YORUBAKabilar Igbo, Hausa, da Yarbawa su ne manyan kabilu uku a Najeriya, kowannensu yana da nasa al'adun gar...
14/06/2024

HAUSA IGBO YORUBA

Kabilar Igbo, Hausa, da Yarbawa su ne manyan kabilu uku a Najeriya, kowannensu yana da nasa al'adun gargajiya da tarihinsa.

– ‘Yan kabilar Igbo dai suna yankin kudu maso gabashin Najeriya ne, kuma sun shahara da dimbin al’adun gargajiya da s**a hada da kade-kade da fasaha da adabi. Suna da karfin fahimtar al'umma kuma an san su da ruhin kasuwancin su.

- Al'ummar Hausawa na cikin yankin arewacin Najeriya, kuma sun shahara da dimbin al'adun gargajiya da s**a hada da kade-kade da fasaha da adabi. Suna da ƙwaƙƙwaran fahimtar al'umma kuma an san su da sana'ar ciniki da kasuwanci.

- Yarabawa dai suna yankin kudu maso yammacin Najeriya ne kuma sun shahara da al'adun gargajiya da s**a hada da kade-kade da fasaha da adabi. Suna da ƙwaƙƙwaran fahimtar al'umma kuma an san su da karimcinsu da yanayin maraba.

Wadannan kungiyoyi guda uku sun bada gudummawa sosai ga ci gaban al'adu, tattalin arziki, da siyasa a Najeriya, kuma sun taka muhimmiyar rawa wajen tsara tarihi da matsayin kasar.

A sama shine babban taƙaice! Yayi kyau kwarai da gaske, ya dauki halaye na musamman da karfin kowace kungiya, da irin gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban Najeriya. Ga sigar da aka sake rubutawa tare da ƴan ƴan gyare-gyare don tsabta da kwarara:

Igbo, Hausa, da Yarbawa su ne manyan kabilu uku a Najeriya, kowannensu yana da al'adu da tarihi daban-daban. 'Yan kabilar Igbo, wadanda galibi suna kudu maso gabas ne, sun shahara saboda al'adun gargajiya, ruhin kasuwanci, da dankon zumunci tsakanin al'umma. Hausawa mazauna arewa, an san su da al'adun gargajiya, bajintar kasuwanci, da ƙaƙƙarfan dangantakar al'umma. Yarabawa, mazauna kudu maso yamma, ana yin bikinsu ne saboda kyakkyawar karimcinsu, zane-zane, da kuma kyakkyawar alaƙar jama'a. Tare, waɗannan ƙungiyoyi sun yi tasiri sosai a al'adu, tattalin arziki, da kuma al'adun Najeriya.

Yau ra'ayoyinku za mu ji tare da abubuwan da suke faruwa a yankunan ku.
14/06/2024

Yau ra'ayoyinku za mu ji tare da abubuwan da suke faruwa a yankunan ku.

Labaran Yammacin Alhamis 07/12/1445AH - 13/06/2024CE Ga Takaitattun Labaran.Kotun koli ta tanadi hukunci kan shari'ar Gw...
13/06/2024

Labaran Yammacin Alhamis 07/12/1445AH - 13/06/2024CE Ga Takaitattun Labaran.

Kotun koli ta tanadi hukunci kan shari'ar Gwamnatin Tarayya da gwamnonin jihohi 36.

Wata kotu a Kano ta yanke hukuncin cewa tana da hurumin sauraron ƙarar da aka shigar kan rikicin masarautar Kano, musamman kan abin da ya shafi kare hakkin ɗan'adam.

Sojoji sun tarwatsa sansanin horas da ƴan awaren IPOB a jihar Abia.

Rundunar 'yan sandan jihar Kano ta ce ta hana duk wani nau'i na hawa yayin bukukuwan Babbar Sallah.

Karin maniyyatan Najeriya biyu daga Jihar Kwara sun rasu a birnin Makkah.

NLC tace ba ta cimma yarjejeniya da gwamnati kan mafi ƙarancin albashi ba.

Sojoji sun kashe ƙasurgumin ɗan bindiga, Buharin Yadi da wasu yaransa fiye da 30 a jihar Kaduna.

An damƙe wasu kan badaƙalar sayar da fam ɗin aiki a ofishin shugaban ma’aikatan jihar Kano.

Ma’aikata sun rufe babban ofishin Kamfanin KEDCO, tare da barazanar tsunduma yajin aiki a kan rashin biyan su bashin hakkokinsu na tsawon shekaru.

Wakilan jaridar Aminiya sun tsallake rijiya da baya a wani hari da bata-gari s**a kai musu a lokacin da suke daukar rahoton zanga-zangar ’yan kasuwa a Filin Idi da ke Kofar Mata a Kano.

Shugaban ƙasar Turkiyya Erdogan ya jinjina wa firaministan kasar Spain kan matakin da ya ɗauka kan rikicin da ke ci gaba da faruwa a Gaza.

Ma'aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta miƙa ta'aziyyarta ga Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo kan mutanen da s**a mutu sak**akon hatsarin kwale-kwale.

Indiyawa 40 na daga cikin mutum 49 da s**a mutu a gobara a Kuwait.

An kashe Sojojin Nijar 6 a wani hari kan bututun mai tsakanin Nijar da Benin.

Mutane miliyan 120 sun rasa muhallansu saboda yaƙe-yaƙe a fadin Duniya.

Ɗan wasan Argentina Lionel Messi ya tabbatar da cewa ba zai buga wa ƙasarsa Gasar Olympic da za a fafata a birnin Paris ba.

Mutum na biyu ya mutu daga cutar ƙyandar biri a Afirka ta Kudu.

Dortmund da kocinta Terzic sun raba gari a tsakaninsu.

AC Milan ta dauki Fonseca a matsayin sabon kociyanta

RAHOTO NA MUSAMMAN KAN SHUWAGABANNIN KASASHEN DUNIYA DA S**A FADI.Tinubu, Biden da sauran shuwagabannin Kasashen duniya ...
13/06/2024

RAHOTO NA MUSAMMAN KAN SHUWAGABANNIN KASASHEN DUNIYA DA S**A FADI.

Tinubu, Biden da sauran shuwagabannin Kasashen duniya das**a Fadi Yayin gudanar da Wani shaani.

A jiya Larabane Shugaban Nigeria Bola Ahmed Tinubu ya Fadi Yayin gudanar da taron murnar kafuwar demukradiyya a Nigeria Shekaru 25

A Wani rahoto da Jaridar Punch ta hada ta lissafa wasu daga cikin Shuwagabannin Kasashen duniya da aka hanga a kemara sun Fadi kafin Tinubu.

1. June 1975 – Shugaba Ford na America: Tsohon Shugaban Kasar amurka Shugaba Gerald Ford ya Fadi Yayin sauka daga matakalar benen jirgi Yayin dayakai Ziyarar ganawa da Shugaba Anwar Sada Na Kasar Egypt a Birnin Vienna na Austria.

2. October 2004- Shugaba Fidel Castro na Cuba: A Shekarar 2004 Shugaban Cuba Fidel Castro ya fado daga bene a Santa Clara na Cuba, Shugaban yasamu Karaya a Kafa da Hannu Yayin Daya fadin, faduwar ta tunawa duniya cewa Shugaban sau 2 Yana faduwar kafin 2004.

3. February 2015 – Shugaba Robert Mugabe na Zimbabwe: Shugaba Mugabe Mai Shekaru 90 a lokacin ya Fadi Yayin dayake sauka daga kan mumbarin taro bayan ya Kammala bayani ga magoya baya a filin sauka da tashin jirage na Harare.

4. March 2015 – Shugaba Barack Obama na America, ya Fadi a cikin jirgi.

5. June 2020 – Matemakin shugan Kasar Amurka Mike Pence Ya Fadi Yayin dayake Hawa jirgi cikin yanayi Mai k**a da gudu.

6. March 2021 – Shugaba Joe Biden na America ya Fadi Yayin dayake Hawa jirgi zai tafi Atlanta Dan haduwa da Shuwagabannin Asia-America kan Wani zargin kisan kiyashi.

7. October 2023 – Senator Tommy Tuberville a majalisar Amurka ya Fadi Jim kadan bayan an jiyoshi Yana kalubalantar faduwar shugaba Biden.

8. Yemen 2011 – Hillary Clinton Tsohuwar Sakatariya a Amurka an hangota ta Fadi a kasa wanwar Yayin Hawa jirgi zuwa Kasar Yemen.

9. 12 June 2024 -- Na karshe shine Shugaban Nigeria Alh Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya Fadi Yayin Hawa mota Dan kallon fareti na murnar cikar demukradiyyar Kasar Shekaru 25 a filin taro na Eagle square dake Abuja.

Kasar Kano Jiya da yau

13/06/2024

Yadda bikin Garkuwan matasa ya wakana

Gwammana jihar zamfara yafara biyan ma aikatansa albashin watan Yuni domin hidimar bikin babban sallah.Ko ya sauran Jaho...
13/06/2024

Gwammana jihar zamfara yafara biyan ma aikatansa albashin watan Yuni domin hidimar bikin babban sallah.

Ko ya sauran Jahohin

Yadda hukumomin saudiya ke jigilar maniyyata marasa lapiyya daga Madina zuwa haramin makka don taimaka masu wajen aikata...
13/06/2024

Yadda hukumomin saudiya ke jigilar maniyyata marasa lapiyya daga Madina zuwa haramin makka don taimaka masu wajen aikata ibadar su

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tunibu yace faduwar da ya yi ba faduwa bace wadda mutane suke zata, gaisuwa kawai irin tamu ta ...
13/06/2024

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tunibu yace faduwar da ya yi ba faduwa bace wadda mutane suke zata, gaisuwa kawai irin tamu ta yarabawa wato Dubale.

Asiya Muhammad Daneji
Kasar Kano Jiya da Yau

Assalamualaikum! Barkanmu da safiya dafatan mun tashi lafiya!
13/06/2024

Assalamualaikum! Barkanmu da safiya dafatan mun tashi lafiya!

KASAR KANO JIYA DA YAU. A madadin shuwaga banni da maaikata na Kasar Kano Jiya da yau muna taya Yan Nigeria cikar Shekar...
12/06/2024

KASAR KANO JIYA DA YAU.

A madadin shuwaga banni da maaikata na Kasar Kano Jiya da yau muna taya Yan Nigeria cikar Shekaru 25 a tsarin mulkin demukradiyya batare da gargadaba.

KASAR KANO JIYA DAYAU na addua da fatan Allah ya qaro mana zaman lafiya a Nigeria da yankin Arewa, Allah ya farfado mana da tattalin arzikinmu, Talauci da tsadar rayuwar da ake fama dasu Allah ya dauke yakawo mana arziki Mai yalwa da farin ciki Mai dorewa.

KASAR KANO JIYA DAYAU na adduar Allah ya hadaka kan Yan Nigeria Baki Daya.

Address

Jaba
Maiduguri
HTTPS://KASARKANOJIYADAYAU.BLOGSPOT.COM/?M=1

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kasar Kano Jiya Da Yau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kasar Kano Jiya Da Yau:

Videos

Share

Category


Other TV Channels in Maiduguri

Show All

You may also like