03/01/2024
Wata mata ta kwanta da kayan barci masu k**a da fatar maciji
Cikin magagin barci, mijin yadauka maciji ne, wajen kokarin kashe macijin ya karya mata kafa, Yanzu dai tana asibiti
Kafar yada labarai mai samar da ingantattu kuma sahihan bayanai akan abubuwan dake faruwa a Najeriya Public Enlightenment
Wata mata ta kwanta da kayan barci masu k**a da fatar maciji
Cikin magagin barci, mijin yadauka maciji ne, wajen kokarin kashe macijin ya karya mata kafa, Yanzu dai tana asibiti
Ana cigiyar wannan matashin
Muna ci giyar bacewar wannan matashin Mai suna Salisu Hassan ( Abba) ya bar gidan su dake Kwarun Badarawa Kaduna, kwana biyu ba a sake jin duriyarsa ba.
Saboda haka duk Wanda Allah yasa ya ganshi ko kuma yaji duriyarsa ya kira wannan Lambar 08038896861 ko kuma wata Hukuma Mafi kusa, Allah ya sa mu da ce.
Ikon Allah!
Hukumar Hisbah ta Karamar Hukumar Sabon Gari Zaria ta samu nasarar ceto wata budurwa mai suna Rabi'ah Salisu ƴar kimanin shekaru 22 da wani saurayi mai suna Joe Abdulmumin ɗan kimanin shekaru 30 ya ɓoyeta kimanin shekaru 7 da s**a wuce a gidan su dake unguwar Dogarawa a karamar Hukumar sabon Gari,kuma har ta haifa masa yara guda uku(3) biyu2 mata ɗaya 1 namiji a yau 28/12/2023 da misalin karfe 1:30pm.(na Rana).
A hirar mu da mahaifinsa wanda yake makaho ne ya shaida mana cewa yayi yayi ɗan nasa ya mayar da yarinyar amma abin yafi karfin sa.
Mahaifin ya shaida mana cewa a salinsa ɗan garin Madobi ne dake Jihar Kano Amma kuma shi ba musulmi bane Kirista ne.
Har ila yau munyi hira da ƴaƴan Rabi'ah Malam Abdullahi Salisu kuma yace mana shekaru bakwai kenan suna neman ƙanwarta su da ta baro gida daga gidan su a unguwar jaba daga nan basu ƙara jin ɗuriyar ta ba sunyi adduah daga baya s**a mayar da komai zuwa ga mahaliccin su.
Tuni dai muka mika shi ga Jimi'an tsaron ƴan sanda domin cigaba da bincike da kuma gurfanar dashi gaban ƙulliya domin ya girbi sak**akon wannan mummunan aikin da ya aika ta.
Allah Ya ƙara mana Nasara ya kuma kare mu daga sharrin bin son zuciya.
'YAN DAMFARA SUN SHIGO DA SALO IRI IRI
Yanzu Yanzu wani dan damfara yazo shagon dake kallon gidana dake unguwar kofar Halliru Gashua, da niyya sayan kaya. Bayan sun kammala ciniki da mai shagon sai ya nemi a bashi number Account, bayan an bashi number Account sai yace ya tura kuɗin mai shago yace kuɗi bai shigo ba fa.
Dan damfarar yazo da wadannan kwalaye da kuke gani guda biyar makare da kaya harda bacco bacco sabbi a cike da kaya. Sai yace wa mai shagon ga kayan sa zai koma kasuwa ya dawo Amma mai shagon ya bashi kuɗi #30,000 kafin ya dawo ga kayan sa nan.
Mai shago dai yaki bada kuɗi, sai Dan damfara yace to yana zuwa a jire masa kayan sa. Haryanzu dai bai dawo ba tin da safe, mai shago yace bari muga menene a ciki kar ya dawo yayi mana sharri.
Ya kira mu mukazo a matsayin shedu muna budewa sai mukaga kwalaye cike da yayi da duwatsu, kasa da sauran tarkace.
Ya jama'a mu kara kula sosai da irin wannan damfara da yan damfara ke yi a cikin Al'umma.
Allah ya raba mu da dukkan sharrin masu sharri.
Shehu A.A Gashua
Janye tallafin mai farashin Burkutu yayi tashin gwaron zabo
Me zakuce
Allah ne kadai zai yiwa wannan budurwa sakayya da hisabi tsakanin ta da wayanda s**a mata mummunar zato wajen chanza ma'anar fassaran wannan suna data rubuta a bayan rigan ta *RABAKAYA*
*RABAKAYA* Ba kalmar iskanci bane k**ar yanda mutane suke tunani suke ta yada hoton wannan baiwar Allah suna daukar alhakin ta
*RABAKAYA* babban family ne a jigawa wanda suna da nasaba da Masarautar Hadejia kuma wannan suna family name dinsu ne k**ar yanda kowa suke da nasu family name din su
Na tabbata duk iskancin yarinya ba zata taba rubuta wannan sunan a bayan rigan ta da niyyar iskanci ba saboda tasan dole wannan hoton zai zagaye duniya daka karshe har iyayen ta su gani
Kamar yanda aka chanza fassaran kalmar KUNU haka aka chanzawa wannan budurwa ma'anar sunan data rubuta, duk wanda yasan ya mata mummunan fassara yayi gaggawa ya neme ta domin yafiya. Muna mata fatan alkhairi mu kuma Allah ya shirya mu da ita baki daya
Copied
A Gaskiya Iya Abinda Na Sani Tsakanin Nafi'u Da Chuchu Matsananciyar Soyayya Ce, Céwar Jarumar Kannywood Suddeenly
Ku Saurara Kuji Daga Bakin Ta....
Ministar Buhari Saadiya Umar Farouk Ta Shiga hannu, EFCC Ta Lalubo Satar Naira Biliyan 37 a Gwamnatin Baya.
Hukumar magance cin hanci da rashawa ta ƙasa, wato EFCC ta lalubo badaƙalar kuɗi har biliyan 37 sannan ta cika hannu da tsohuwar ministar walwala da jin ƙai na Nijeriya lokacin mulkin Buhari, Sadiya Umar Farooq.
Wannan sanarwar mun sameta ne daga Gidan Jaridar Punch Newspapers a shafinsu na Twitter, sannan kuma Shugaban Gidan Jaridar Liberty, Ahmad Tijjani Ramalan ya wallafa a shafin sa.
Jama'a miye ra'ayin ku game da wannan batu.?
Ni nakai takarda Da iznin sheikh Dahiru Bauchi
Takardama kan takardar aka aikema kotun koli wanda daya dagacin yayansa ya musanta
Ya kuke kallon wannan zanga zangar
Wane suna zaku basu ?
Hon Husseni Kero Dan majalisar dake wakiltar kaduna ta kudu a Abuja ya kai ziyarar bazata domin duba yadda aikin wadanda ya dauki nauyin duba lafiyar idanunsu ke gudana
NAFI'U SAURAYIN HAFSAT NE: Ga yadda bincike ya tabbatar min kan labarin Nafi'u da Hafsat...
Nafi'u saurayin Hafsat ne da jumawa bayan Hafsat tayi aure shine s**a ha'da Kai s**a fara kasuwanci (Business) tare da Nafi'u Kuma Allah ya basu sa'a s**a samu ku'di masu yawa har ita Hafsa ta bu'de Shago a zoo road, Hafsat da mijinta Dayyabu suna zama a wani karamin gida sai Allah ya bu'dewa mijin ya samu ya Gina Babban gida kafin domin su koma can da zama tare da matarsa, kafin nan ita Hafsat ta Riga ta ha'da mijin nata da Nafi'u sun saba harya zama k**ar dan Uwa suna harkoki tare ba tare da mijin yasan abinda dake tsakanin matarsa da Nafi'u ba.
A lokacin da su Hafsat za su tare a sabon gidan su shine tace dole sai dai a koma Sabon gidan tare da Nafi'u haka Kuma akayi dole mijin ya amince ance Yana tsoronta kasancewar ta fishi ku'di.
Ana haka ne Nafi'u bashi da lafiya Kuma Already ya Fa'dawa Iyayensa cewa Yana da Ubangida a Kano ko da Iyayen Nafi'u s**a zo Kano daga bauchi sai Nafi'un ya gabatar da Iyayen nasa ga Dayyabu mijin Hafsat amatsayin maigidan sa ne na kasuwanci, ba kowa yasan cewa Nafi'u saurayin Hafsat bane sai abokan Nafi'un da Kawayenta na kusa, ana zargin Yaron da Hafsat ta Haifa Dan Nafi'u ne domin suna k**a sossai.
Ance ko Ina Hafsat za ta tafi tare suke tafiya da Nafi'u har Umrah Kuma mijin Yana kallo ba tare da yace komai ba.
Dalilin wannan rigima da ya sa Hafsat ta Kai kashe Nafi'u shine Nafi'un ne ya Fa'dawa Hafsat cewa zai yi aure ya samu wata matar aure tun lokacin shine ba a sake zaman lafiya ba tsakanin Hafsat da Nafi'u.
Allah ne ya taimakawa mijin Tabbas da shine zai kasance Gawa bisa wannan Dalilin soyayya Dake tsakanin Nafi'u da Hafsat Yanzu dai Hafsat ta kashe Nafi'u, Allah ya jikansa da rahama, jama'a don Allah a kiyaye dokar Allah a zaman aure idan ba haka Bala'i zai Cigaba da faruwa tsakanin Al'ummarmu.
An turamin Hotunan yaron Amma ba zan iya sakawa ba..
Rundunar yan sandan jihar Oyo ta kora tare da kwaɓe kakin wasu yan sanda biyu da aka ɗauki bidiyonsu suna tambayar wata Baturiya da ta zo yawon buɗe ido Nijeriya, cewa ta ba su kuɗi
A yau an kore su kwatakwata daga aikin dan sandan, sak**akon samun su da laifin zubar wa rundunar yan sanda mutunci, da saɓa dokar aiki
AL'AJABI: Macijiya Mai Shekaru 963 Da Ta Yi Rayuwa Da Sarauniya Amina Ta Yi Gargaɗi Ga Mutane
Macijiyar mai kimananin shekaru 963 a Duniya ta yi wa mazauna wajen gargaɗi, gargadin dai ya faru ne ta yadda ta tayar da hankalinsu da kuka da fitar da wani hayaƙi daga kogonta dake kan Dutsen Turunku.
Mazauna wajen dai sun zargi hakan ya faru ne sak**akon wani maciji da aka kashe bayan ya sakko daga dutsen zuwa kasa inda mutane ke gudanar da al'amuransu.
Al'amarin da ya faru a ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar Kaduna.
KASTELEA TAYI ZAMAN WAYAR DA KAI KUNGIYOYIN MASU SUFIRI DAKE JIHAR KADUNA
GWAMNATIN JIHAR KADUNA TA FARA SHARAR HANYAR TUDUN BIRI GABANIN KADDAMAR DA AYYUKA
Daga Shuaibu Abdullahi
Gwamnatin jihar Kaduna ta fara sharar hanyar shiga kauyen Tudun-Biri, gabanin kaddamar da ayyukan cigaba da Gwamnatin tayi alkawari.
Tawagar Gwamnatin ciki har da Shugaban KASUPDA dana hukumar tsare tsare gidaje KADGIS da mai temakawa Gwamnan Kaduna kan hulda da jama'a da sauran su ne s**a shiga garin a madadin Gwamnatin.
Kafin yanzu Kauyen Tudun Biri dake karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna, shine wanda Sojojin kasa s**a yi kuskuren sakin Bam da yayi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 80 da raunata da dama.
Shugabannin sun yi alkawarin inganta garin tabangaren samar da Titin mota da Makarantu da ofishin yansanda da Asibitin kiwon Lafiya da lantarki da sauran su.
Ko a makon daya gabata Sai da kungiyar Gwamnonin Arewacin kasa karkashin jagorancin Gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, s**a baiwa garin Tudun-Birin, tallafin nera miliyan 180.
Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, yace ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, kan irin jajircewa da kokarin ganin an gudanar da sahihin bincike game da batun.
Ba Batun Diyya Muke Yi Ba A Halin Yanzu, Tambaya Muke Kan Me Yasa Aka Kashé Mana Mutane? Kuma A Fito Mana Da Waɗanda S**a Yi Wannan Aika-aikar Mu Gansu, Sannan A Hukunta Su Domin Gudun Sake Faruwar Haka Ko Da Akan Dabbobi Ma Ba Mutane Ba
Cewar Mai Martaba Sarkin Kano Na 14 Muhammadu Sanusi II (Khalifan Tijjaniya Na Najeriya).
CIGIYYA! CIGIYYA!! CIGIYYA!!!
Don Allah Ana Cigiyya Iyayen Wannan Yaro Yace Suna Shi Sadiq, Sun Zo Biki Zariya A Kwarbai Daga Nasarawa Doya, Yanzu Haka An Tsince Shi A Cikin Garin Kaduna. Allah Ya Bayana Iyayen Shi Duk Mai Neman Kari Bayani Ya Kira Wannan Number Waya 08027183008
Jam'ar British Amerika ta tabbatarma Eng kailani Mohamed da matsayin farfesa a Abuja
CIN AMANAR AURE
Shi kuma wannan matashin 'yan sanda a jihar Bauchi sun k**ashi saboda yayi yunkurin kashe matarsa da tabarya don ya samu damar sayar da kayanta ya kara jari a shagonsa
Matashin mai suna Tijjani Ahmadu Diye bayan ya buge matar nasa da tabarya har ta suma, sai ya kai rahoto cewa wai barayi ne s**a shiga gidansa s**a buge matar
Cikin ikon Allah bayan an kai matarsa Asibitin koyawar na Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa University Bauchi ta farfado, kuma tayi bayani wa 'yan sanda cewa rahoton da mijinta ya bayar karya ne
Ba'a yi kasa a gwiwa ba 'yan sanda s**a k**a mijin, kuma ya amsa laifinsa cewa ba barayi bane, shine yayi niyyar kasheta don ya sayar da kayanta ya kara jari a shagonsa
Wannan itace irin rayuwar da mukeyi a yau, kusan kowa idonsa ya rufe, ana neman kudi ta kowace irin hanya, abin mamaki wai miji da yunkurin kashe matarsa don ya mallaki dukiyarta
Allah Ya sauwake, Ya nesanta tsakanin mu da masoyan karya
Wasu da ba'asansu ko suwaye ba sun sari wani matashi a kaduna yanzu haka yana asibitin Barau Dikko
Yau Ranar yaki da cin hanci da rashawa ta duniya hukumar EFCC ta Gudanar da zagayen wayar da kan Al'uma da hadin guiwar sauran rundunonin tsaro dake jihar
Wani Dan majalisar kano ya kwashe yan mazabar shi ya dawo dasu Zaria a zauren majalisar ana ganin fate yasha ya shi wannan tukuici
Me zakuce
JERIN SUNAYEN SHUWAGABANNIN KARAMAR HUKUMAR ZARIYA DAGA 1973 ZUWA YAU
1. Alh. Mijinyawa Dikko 1973-1977
2. Alh. Ahmadu Fatika 1977-1979
3. Alh. Salisu Ahmad 1980-1983
4. Alh. Dayyabu Kurfi 1984-1986
5. Alh. Muhammadu Lawal 1986-1988
6. Alh. Hamidu Yahaya 1988-1989
7. Alh. Muhammad Amfani 1989-1989
8. Mr Thomas Kazah 1989-1991
9. Alh. Armiyau Suleiman 1991-1993
10. Alh. Jafaru Suleiman 1994-1996
11. Alh. Bashir Ismail Ahmad 1997-1997
12. Alh. Mohammed Bashir Ali 1997-1997
13. Alh. Muhammad Tukur 1997-1997
14. Alh. Samaila Nabara 1997-1998
15. Alh. Idris Adamu 1998-1999
16. Alh. Musa Iyah 1999-2003
17. Alh. Abdussalam Baba Ahmad 2003-2003
18. Alh. Mohammed Tukur Abashe 2003-2004
19. Alh. Yahaya Aminu 2004-2007
20. Alh. Lukuman Musa 2007-2007
21. Major Muhammad Aliyu 2007-2008
22. Alh. Yahaya Aminu
23. Alh. Lukuman Musa 2008-2008
24. Muhammad Umar Raba Gardama
25. Hon. Lawal Balarabe 2012-2014
26. Yusuf Bature Mai zarman 2014-2015
26. Barr Jafar Abbas 2016-2016
27. Eng Abubakar Maude 2016-2018
29. Eng Aliyu Idris Ibrahim 2018-Date
Wai ya dace a irin wannan lokacin malaminan yayi irin wannan maganar
Gara basa !
Gara basa !!
Gara basa !!!
Kudinka kalilan ka kwashi kasiran sai yardan Allah
Dolene abiya diyar wadanda aka kashe a gurin mauludi a kaduna bazamu yarda ya zama k**ar yan uwamu da aka kashe a filato ba Inji Sheikh Dahiru Usman bauchi
Yadda Aka Gudanar Da Jana'izar sama da mutane 80 da harin bom ya kashe a kaduna
Ba sojojin sama bane s**a jefa bom a gurin mauludi a kaduna
Korafin wani daga yankin da aka jefa bom kan masu mauludi a tudun biri dake yankin buruku a karamar hukumar Chikun kenan
Hon Mamadi yayima masu hudar shanu kyautar da wani bai taba yi musu ba sama da shekaru 50 Karamar hukumar Igabi
Ga rahoton saurara kaji
Dan Dumi Dumi Wani jirgin yakin sojojin saman najeriya ya jefa bam kan wasu masu mauludi a kaduna karin bayani na zuwa nan gaba kadan
LABARAI DA DUMI-DUMI !!
Tsohon Shugaban Mulkin Soja Na Najeriya Ibrahim Badamasi Babangida, Yayi Kira Tare Dajan Hankali Ga Babban Mai Shari'a Na Kasa Alkalin Kotun Koli, Yasani Cewa: Zaman Lafiyar Najeriya Yarataya Awuyan Bangaran Shari'a, Kasancewar Yanzu Mulkin Najeriya Na Dimokaradiyane Mai Cike Da Kalubale Da Sarkakiya, Akwai Bukatar Asamu Adalchi Awajan Hukunce Hukuncen Kararrakin 'Yansiyasa, Ayi Kokarin Kaucewa Sanrai Ko Bukatun Wasu Manya Ko Shuwaga Bannin Siyasa, Domin Cigaba Dasamun Dawwamamman Zaman Lafiya A Najeriya Kasarmu Tagado, Yazama Wajibi Ayi Hattara Wajan Zartar Da Hukunci Tahanyar Adalci Bangaran Mai Kara Da Wanda Ake Kara, Kada Ayadda Ayi Anfani Da Bangara n Shari'a Don Biyan Bukatun Wasu Tsirari Don Atozarta Wasu, Saboda Gudun Abinda Zai Biyo Baya Bazaiwa Kowa Dadiba Harda Mu Kanmu Tsofaffin Iyayan Kasa !
SAKON GODIYA DA KUMA BAN GAJIYA
Assalamu Alaikum.
Ina amfani da wannan dama domin mika godiya a gareku bisa kauna, karamci da kuma mutuntawa da kuka nuna a gareni, na halartar bikin nadin sarauta na a matsayin SARKIN SAMARIN GONA da kukayi wanda mai martaba Lamido Gona ya karramani da ita, hakika ba zan manta da wannan halacci naku gareni ba.
Ina adduar Allah ya sakawa kowa da alheri ya kuma huce gajiya.
Nagode.
Bilya Yaro Dawakin Tofa
SARKIN SAMARIN GONA
MUTUM NA FARKO DA YA GINA ISLAMIYYA A GARIN KADUNA
Marigayi Alhaji Abdu Kwangila, shahararren attajiri mai son cigaban addinin musulunci. Mutum na farko daya fara kafa makarantar Islamiyya a garin Kaduna. Asalinsa mutumin kasar Bidda ne, ya komo Kaduna da zama a wajejen 1935. Mutum ne mai gaskiya, da kwazo da son malamai da yawan taimako. Shine mai masaukin malamai da yawa a Kaduna. Allah Ya Jikan Shi Yayi Mishi Rahama Yasa Yana Kyakyawan Matsayi.
Shugabannin kungiyar dakon mai ta PTD sunyi kira ga membobin kungiyar dasu zauna lafiya su kaucema masu kiran suyi zanga zanga ko yajin aiki
Wani Dan sanda ya harbe mutane biyu a kaduna saboda takaddamar labule da me adaidaita sahu
Kaduna
Be the first to know and let us send you an email when Taskira TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.
Shugabannin kungiyar dakon mai ta PTD sunyi kira ga membobin kungiyar dasu zauna lafiya su kaucema masu kiran suyi zanga zanga ko yajin aiki
Shugabannin kungiyar nufawan kaduna sun gudanar da wani Babban taron hadin kan jama'arsu domin tattauna hanyoyin da zasu samar da cigaban Al'umar nufawa dake kaduna
Nufawa suka kafa garin kaduna kamar yadda tarihi ya nuna inji jigo a jam'iyar APC Injiniya kailani Mohamed
Zabe za'a rikayi ba nadiba a kungiyar dakon mai ta PTD Inji tsohon shugaban kungiyar na jihar Kaduna kwamared Nuhu Mohamed Marafan Nassarawa
Malaman karamar hukumar kaduna ta kudu suma sun sheda tallafin Husseni Kero na kudi daya basu domin rage radadin halin da ake ciki
Daya daga cikin shugabannin kungiyar Direbobi ta NURTW yayi kira ga gwamnan jihar kaduna da sauran jami'an tsaro da suyi gaggawar shiga cikin lamarin kungiyar gudun rikici da wasu ke kokarin sata a ciki
Hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Kaduna karkashin jagorancin Dr Yusuf yakubu Arrigasiyyu ta shirya taron bita ga malamai kan fara karbar aikin hajjin data fara
Hon Mamadi ya daukin nauyin sayawa makarantar Islamiya fili da gudumawar kudi daya basu a Riga Chikun
Dan malisar wakilai dake wakiltar karamar hukumar Kaduna ta kudu a Abuja Hon Husseni Kero ya tallafama wasu daga Al'umar da kudi sama da naira miliyan arba'in
WAATÀ SABÚWA: Sai Da Buhari Ya Lalata Ƙasar Nan Ƙafin Ya Sauka Daga Kan Mulki, Céwar Mawaƙi Dauda Kahutu Rarara Mé zakú cé?
Kungiyar Dalibai musulmi ta kasa wato MSSN ta zagaya Dalibai musulmi daga makarantu daban daban dake jihar Kaduna domin Ilmantar dasu wasu mahimman abubuwa na musulunci
NNPP shiyar Arewa maso yamma tayi wani Babban taro a kaduna domin farfado da jam'iyar bayan zargin Sanata Rabiu kwankwaso da shirya makarkashiyar rusa jam'iyar
Alu Dan sidi old boys association member
Prison Road Zaria City