Abokiya HAUSA News Magazine

Abokiya HAUSA News Magazine Magazine at always, anytime, anywhere. For easy reading and self entertainment.
(1)

17/10/2022

Arewa Ta Gabas ba Matemakin Shugaban Kasa Ta ke So ba
Sabo da tayi Shi a baya
Shugaban Kasa Mukeso
A yanzu

25/09/2022
A wata ganawa ta musan man da ta gudana a yau, 22 ga watan Satumba 2023 tsakanin shuwagabanin kungiyar ( Bauchi North PD...
22/09/2022

A wata ganawa ta musan man da ta gudana a yau, 22 ga watan Satumba 2023 tsakanin shuwagabanin kungiyar ( Bauchi North PDP Supporters Club) Da Mai girman tsohon Matemakin Gwamnan Jihar Bauchi Arc. Abdu Sule Katagum a gidan sa da ke cikin garin Bauchi. Da fatan Allah ya yi mana Jagora 2023.

Masha Allah yadda tattaunawa tagudana tsakanin Shuwagabannin kungiyar Bauchi North PDP Suppoters Club, Da wakilan dan ta...
05/09/2022

Masha Allah yadda tattaunawa tagudana tsakanin Shuwagabannin kungiyar Bauchi North PDP Suppoters Club, Da wakilan dan takarar Sanata mai wakiltar Arewacin Bauchi a karkashin inuwar Jam'iyyar PDP, Dr. Sama'ila Dahuwa (Kachallan katagum) Da fatan Allah ya cigaba da yi mana Jagora.

Wazirin Adamawa Ne, Yafi Sauran Yan Takarar Chanchanta, A Kakar Zabe Da Ke Tafe Na Shekarar 2023.Ya jama'a masu hankali ...
04/08/2022

Wazirin Adamawa Ne, Yafi Sauran Yan Takarar Chanchanta, A Kakar Zabe Da Ke Tafe Na Shekarar 2023.

Ya jama'a masu hankali muna so kusani duk wani dan siyasar da a yau ya ke Nageriya ya na cin albarka cin Atiku Abubakar ne a siyasan ce Dalilin mu kuwa.

Shi ne dan Siyasar da ya rusa mummunan shirin nan na ne man Zango na Uku da Tsohun Shugaban Kasa Obasanjo, Ya ne ma wanda da ga karshe bai yi nasara ba, Da a ke kira da (Third Term) da shirin ya yi nasara da Damokaradiyyar Kasar tashiga wani yanayi na rudani a wan can lokacin.

Kafin hakan yana daga cikin yan tsirarun mutane yan Siyasa da s**a yi ta Fafutuka da Gwagwarmayar ganin kasar nan ta da wo kan Turba irin ta Salon Mulkin Damokadiyya, A lokacin Gwamnatin Marigayi Janar Sani Abacha, duk da shakkar sa da tsoran sa da jama'a su ke yi wa Janar din bai hana su Atiku yin Kiraye kiraye ba ga Gwamnatin ta Abacha da ta dawo da kasar kan turbar mulkin Siyasa, Ba a samu wani lokaci mai tsawo ba Allah ya yi wa Janar Abacha rasuwa, Da zuwan Janar Abdussalam Abubakar a matsayin Shugaban Kasa hakar su Atiku ta cinma ruwa.

Bugu da kari kuma shi ne dai dan Siyasar da tun Shakarar Alif Dubu Daya da Dari Tara da Casain da Tara (1999) Da aka kafa wannan Damokaradiyyar duk wan da Allah ya sa yazamo shugaban kasar nan to ya samu Goyan bayan Wazirin Adamawa Atiku Abubakar.

Haka zalika kuma a Alif Dari Tara da Casain da Uku (1993) ya na daga cikin manyan yan Siyasar kasar nan da su ka temakawa Abiyola samun Nasara a zaban fidda Gwani da Jam'iyyar su ta (SDP) ta gudanar a cikin garin Jos, A sakamakon janyewar da shi Atiku ya yi wa Abiyola wanda hakan ne ya kai shi ga samun nasarar lashe Zaban da a ka gudanar na kasa baki daya a shekarar, Da ga baya Shugaban Kasa na wannan lokacin Janar Ibrahim Badamasi Baban Gida ya rusa zaban Wanda a kafi sani da (June 12).

Har ila yau dai shi ne dan Siyasar da babu wani dan siyasa Kwatankwacin sa a fadin wannan kasa tamu duba da yadda Atikun ya ba da Gagarumar Gudun mawa ta ganin an gudanar da Sahihiyar Damokaraddiya mai daurewa a fadin Kasar baki daya da ga nin Hadin kan kasar ya daure, Ta yadda kowane bangaren kasar ya ke jin ana damawa da shi wan da hakan shi ya kawo mata samun Muhimman Nasarori da su ka hada da Zaman Lafiya, Morar Romon Sahihiyar Damokaradiyya, Karfi Tattalin Arziki, da dai sauran su, A sanadiyar hakan kasa tayi fice a fadin Nahiyar ta Afirka baki daya a lokacin mulkin na su Atiku.

Duk wayan nan Nasarori da kasar tasamu sun samu ne sanadiyar Gogewa da Jajircewa irin ta wannan Bawan Allah Atiku Abubakar sakamakon yana Matemakin Shugaban Kasa na wancan lokacin.

A takai ce da wannan dalilai ne yasa muke ganin Atiku yafi saura Chachanta da wannan kujera ta Shugaban Kasa.

01/08/2022

Tinibo da Kashim ba Addinin Musulunci Su ke wakilta ba kuma ba Musulmai Su ke Wakilta ba Jam'iyyar Su ta APC Su ke Wakilta Kawai

28/07/2022

Duk Wanda Ya Zabi Jama'iyyar APC
A Matakin Shugaban Kasa
K**ar Ya Amice Ne, A ci gaba Da Kashe Yan Arewa
Allah Ka Tsare My.

26/07/2022

Babban Kuskuren Da Talakawa Ya K**a Ta
Su Guji Tafkawa Shine Su Sake
Zaban Jama'iyyar APC Da Dan Takarar
Shugaban Kasarta

Kai yan Jama'iyyar Tsintsiya Kuyi Hakuri Wanda Ya Tara Taron Ya Watsa Shi, Taron Ya Watse. Kuma Kusani Shure -Shure Ba y...
25/07/2022

Kai yan Jama'iyyar Tsintsiya Kuyi Hakuri Wanda Ya Tara Taron Ya Watsa Shi, Taron Ya Watse. Kuma Kusani Shure -Shure Ba ya Hana Mutuwa !!!

NAGARI AMININ KOWA, WAZIRIN ADAMAWA KAI NE ZABIN WAYAYYU MASU WAYO DA MA'ABUTA ILMI DA MASU HANGEN NESA, DA MASU LURA DA...
25/07/2022

NAGARI AMININ KOWA,
WAZIRIN ADAMAWA KAI NE ZABIN WAYAYYU MASU WAYO DA MA'ABUTA ILMI DA MASU HANGEN NESA, DA MASU LURA DA AL'A'MURAN YAU DA KULLUM, DA MANAZARTA, MU NA MAKA FATAN NASA, ALLAH YAYIMAKA JAGORA 2023

To Jama'a Barkan Mu da Sake Saduwa Da Ku, A Dai Dai Wannan Lokaci, Har Yau Dai K**ar Kullum Ga Shi Mun Sake Dawo Mu ku D...
23/07/2022

To Jama'a Barkan Mu da Sake Saduwa Da Ku, A Dai Dai Wannan Lokaci, Har Yau Dai K**ar Kullum Ga Shi Mun Sake Dawo Mu ku Da Wani Jan Hankali, Mu dai Har Yanzu Mu na Sake Tunatar Da Masu Hankalin Cikin Mu, Da Masu Wayan Cikin Mu, Da Masu Ilmi Da Hangen Nesa, Da Allah Ya Arzuta mu da su, mu na rayuwa tare, A wannan yanki namu na Arewa mai Albarka da yawan Jama'a fiye da kowane yanki na kasar nan. Mu na masu roko a ga reku do ba da irin baiwar da Allah ya muku a tsaka nin Al'umma ku tabbatar ba kuyi kasa a gwaiwa ba wajan ganin kun wayar da kan Mutane game Mahimmancin Zaban Wazirin Adamawa, Shi ne kawai mafita da yardar Allah, Musanman ga yayan wannan yankin namu na Arewa. ALLAH KAYIMASA JAGORA 2023. Masha Allah

23/07/2022

Salon Milkin Jama'iyyar APC
A Najeriya K**ar
Mahaukaci Ne Ya Hau Kura
Sai Geran Allah !!!

Kukan Kurciya..........Allah Muna Masu Sake Godiya A Gareka Bisa Ni'imomin da Kayi Mana Wanda ba Za Mu iya Kidaya Su ba....
22/07/2022

Kukan Kurciya..........

Allah Muna Masu Sake Godiya A Gareka Bisa Ni'imomin da Kayi Mana Wanda ba Za Mu iya Kidaya Su ba. A cikin wayannan ni'i Kukan momi sunhada da nisan kwana, A sanadiyar nisan kwanan da Allah ya yi mana shi ya bamu damar ganin irin salon mulkin Jama'iyyar nan ta APC mai mulkin kasar a yanzu. A tun bayan zaban shekarar 2015 da ya yi sanadiyar kawo karshan mulkin Jama'iyyar PDP bayan ta shafe Shekaru Shashida (16) tana shimfida irin nata kwarewar a sha'anin gudanar da mulki. Duba da yadda mulkin na APC ya ke gudana ya zama tamkar mahaukaci ne ya hau kura sabo da irin yanayin da kasar da yayanta su ka samu kansu a halin da akeciki a yanzu. Tun kafin cikar kwana dari na gwamnatin ta APC mutane da dama s**a dawo da ga rakiyar ta manazarta kuwa da sauran masu hangen nesa s**a ci gaba da kalubalantarta da yi mata raddi sakamakon mummunar gazawarta da kuma kasa cika alkawarin da tayiwa yan kasar. Sanadiyar gazawar ta Gwamnatin masu Tsintsiyar
ya jawowa Nageriyar gagarumin koma baya ta fannuni da ban da ban kamar su karyewar Tattalin Arziki, Rashin Tsaro, Garkuwa Da Mutane a biya kudin Fansa, Mummunan Talauci a tsakanin yan Kasa, Rashin samar da aikinyi ga matasa, Cinhanci da Rashawa da ba a taba ganin irin saba a tuntarihin kafuwar kasar nan haka shima dai maganar man Fetur Gwamnatin ta gaza kawu saukin sa ga Talakawa, Haka shima bangaren Ilimi babu wani abu illa wahala da yayan Talakawa su ke sha sakamakon yajin aikin da haryau Gwamnatin APC ta Kasa shawowa kansa. Ya Jama'a wannan dumbun rashin nasara da mummunan koma baya da kangin da Kuma halin ha'ula'in da a ka Jefa kasar a ciki ya samo a saline da ga zaban bara gurbi ko ka ce zaban tumun dare a bin da muke nufi shi ne ba a zabi wayanda su cancantaba da ita kanta Jama'iyyar ta APC. Da ga karshe muna ba da shawara ga yan uwanmu Talakawa tun da Allah ya sa munga kamun ludayin kowace Jama'iyya tsakanin PDP.da APC a baya Munga irin yadda rayuwarmu tagudana tattalin Arzikinmu ya gudana zaman lafiya yagudana saukin kayan masarufi saukin sufiri walwala a tsakanin a Al'umma rashin fargaba da kwanciyar hankali da karuwar Arziki, Wallahi duk munsaida wayannan a bubuwa a Karkashin Mulkin Jama'iyyar PDP. Karkashi jagorancin Gwamnatin su mai Girma Wazirin Adamawa Allah muna rokonka ka sake amintar da mu kamar yadda ka amintar da mu a wan can lokacin. Allah Kayiwa Atiku Jagora 2023

Ya ku yan Uwanmu yan Arewa, Muna Sake Kira A ga reku Musamman Wayan da Allah ya basu Hangen Nesa Haka Zalika Kuma da Way...
21/07/2022

Ya ku yan Uwanmu yan Arewa, Muna Sake Kira A ga reku Musamman Wayan da Allah ya basu Hangen Nesa Haka Zalika Kuma da Wayan da ya h**e musu Hankali, da Masu Lura, da Kuma Masu Wayo da ga Cikinmu. Ya zamo wajibi ne a gare ku da ku tabbatar kunyi iya bakin kokarinku na ganin kunwayar wa da Al'ummar wannan yanki kai dan gane da gagarumin kalobalen da ke tunkararta a wannan kakar zaban da ketafe na shekar 2023 ganin wannan Al'ummar ta Arewa bata shiga hanun makiyanta ba kuma bata fada gadar zaren da akashirya mataba. Wadda wasu mara kishin yanki s**a wadda ake amfani dasu domin biyan bukatar kawunansu tahanyar abiyasu kudi ko mukamai. To da wannan ne muke kira a gareku ya ku ma'abuta hankalin cikinmu da wayayyu da masu wayo da masu shekarun mu, to mulura kada musake wawayen cikinmu susa a yi mana sakiyar da ba ruwa ayi yaki a barmu da kuturon bawa. Daga karshe muna masu rokon Allah ka tsaremu da aikin wawaye kuma Allah muna rokanka karkaka mamu da abin da wawayen cikinmu s**a jawo mana. Gawanda jama'ar Arewa sukeso nan Allah kabashi mulki, Kayi Masa Jagora 2023. Da Arziki a garin wasu gwanda ga rinku.

21/07/2022

Yardar Allah Muke Nema
Ba Ta Kistoci Ba
Allah Kayiwa Atiku Jagora
2023

Faɗuwar APC a Osun darasi ne gare mu - Abdullahi Adamu.Shugaban jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya, Sanata Abdullahi Ada...
19/07/2022

Faɗuwar APC a Osun darasi ne gare mu - Abdullahi Adamu.

Shugaban jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce kayen da jam’iyyar ta sha a zaɓen gwamnan jihar Osun jarrabawa ce daga Allah.

A wata tattaunawa da ya yi da BBC, Adamu ya ce ya zama wajibi ga 'ya’yan jam'iyyar su gyara abubuwan da suke yi waɗanda ba daidai ba ne game da tafiyar da lamuran siyasar ƙasar gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Ya ce "Wannan ya nuna cewa akwai aiki a gabanmu, dole ne mu ga abin da muke iya yi, mu canza salo."

Ya ƙara da cewa "Dole ne mu dubi kawunanmu, mu ga mene ne abubuwan da muke yi a tafiyar nan waɗanda daidai ne, mene ne wanda ba daidai ba, mene ne ke neman gyara, domin mu gano mece ce mafita a tafiyar nan."

Sai dai shugaban jam'iyyar na APC ya ce wannan faɗuwa ba ita ce ke nufin jam'iyyar za ta faɗi a babban zaɓen ƙasar na 2023 ba.

A cewarsa jam'iyyar za ta yi nazarin abubuwan da s**a sanya jam'iyyar ta faɗi zaɓen na jihar Osun domin ta samu nasara a zaɓen ƙasa mai zuwa.

A cikin wannan wata na Yuni ne dai Senata Ademola Adeleke na jam`iyyar PDP ya samu nasara a kan gwamna Gboyega Oyetola na APC, wanda ya nemi wa`adi na biyu, da ratar ƙuri`a kusan dubu talatin.

Hakan ya faru ne kuwa duk da cewar jihar Osun tana a kudu-maso-yammacin Najeriya ne, yankin da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar APC Bola Ahmed Tinubu ya fito.

'Baraka tsakanin ‘yan jam’iyya'

Shugaban na jam'iyyar APC na ƙasa ya kuma tabbatar da cewa ɓarakar da ke tsakanin manyan 'yayan jam'iyyar ne ya haifar da faɗuwar ta a zaɓen na Osun.

Ya ce "Ya tabbata akwai rashin jituwa tsakanin magabata, masu isa a tafiyar siyasar jihar Osun na jam'iyyar APC."

Ya ce waɗannan jiga-jigai na jam'iyyar APC jihar ta Osun sun rinƙa s**ar da zargin junansu.

Ya ƙara da cewa "Idan s**a buɗe baki cewa suke yi ba za su yi zaɓe ba idan ba a yi masu abin da suke so ba."

Ya tabbatar da cewa jiga-jigan na APC a jihar ta Osun sun kasa jituwa tsakanin su duk da cewa suna a jam'iyya ɗaya.

'Mun karɓi ƙaddara'

"Harka ta siyasa kamar sauran lamurra ne na rayuwa, kana iya nema ka samu ko kuma ka rasa. Iko ne na Allah, babu yadda muka iya" in ji Abdullahi Adamu.

Sai dai Abdullahi Adamu ya ce ba an kayar da APC ne saboda ba ta iya siyasa ba, sai dai saboda abubuwan da s**a faru tsakanin 'yayan jam'iyyar gabanin zaɓen.

A cewarsa, jam'iyyar ta amince da ikon Allah.

Allah Muna Masu Cigaba Da Rokon ka, Kabawa Dan Yankinmu Na Arewa Mulkin Najeriya, A Kakar Zaban Shekarar 2023 Da Ketafe....
17/07/2022

Allah Muna Masu Cigaba Da Rokon ka, Kabawa Dan Yankinmu Na Arewa Mulkin Najeriya, A Kakar Zaban Shekarar 2023 Da Ketafe. Ya Mai Bayarwa, Allah Inkabashi Kasa Ya Zama Alkhari A Kasar Da Kuma Yan Kasar Baki Daya, Kuma Allah Kasa A Samu Zaman Lafiya Tahanun sa, Kasa Kuma Ya Zama Shine Sanadiyar Samun Saukin Al'umma.

16/07/2022

Allah Wadaren Naka Ya Lalace Rakumin Dawa Yaga Na Gida,
Wai Bahause Da Tallen Bayarebe
Har kunmanta Da
OPC

Nasara Bata Tabbata Sai Da Hassada Sai Da Kushe, A kullum Kuma Ita Hassada Ga Mai Rabo Taki ce, Muna Rokon Allah Ya Raba...
14/07/2022

Nasara Bata Tabbata Sai Da Hassada Sai Da Kushe, A kullum Kuma Ita Hassada Ga Mai Rabo Taki ce, Muna Rokon Allah Ya Rabamu Da Ita. Kuma Muna Masu Addu'a A Gare Ka, Da Fatan Allah Yaci Gaba Da Shiga Lamarinka Kuma Ya Maka Jagora 2023.

Muna Masu Rokon Allah Ya Sa Makiyanka Su Zamu Masoyanka, Kuma Muna Maka Fatan Alhiri, Allah Ya Maka Jagora 2023. Da Yard...
13/07/2022

Muna Masu Rokon Allah Ya Sa Makiyanka Su Zamu Masoyanka, Kuma Muna Maka Fatan Alhiri, Allah Ya Maka Jagora 2023. Da Yardarsa Madaukakin Sarki.

10/07/2022

Allah Ka Tsare Mu da Mulkin Yan O P C
Da na yan B H
A Nageriya

05/07/2022

Allah Kayiwa Dan Takararmu Da Yafito Da ga Arewa Ta Gabas
Jagora 2023

05/07/2022

Mudai Bamu Da Wani Yanki A Nigeria Da Muke Alfahari Da Shi Da Yawuce
Arewa Ba
Da Wannan Dalilin Ne Ya sa Baza muki
Dan Arewa Ba!

Peter Obi danmu ne amma Atiku za mu yi a kudu maso gabas – Ekweremodu.Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike ...
22/06/2022

Peter Obi danmu ne amma Atiku za mu yi a kudu maso gabas – Ekweremodu.

Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike Ekweremadu, ya bayyana cewa mutanen kudu maso gabas ba za su zabi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, ba a zaben 2023. Obi, wanda ya kasance daya daga cikin masu neman takarar shugaban kasa na PDP ya sauya sheka zuwa jam’iyyar Labour Party kafin zaben fidda gwanin jam’iyyar wanda Atiku Abubakar ya lashe.

Duk da kasancewarsa dan yanki daya da Obi, Ekweremadu ya ce kudu maso gabas ba za su iya yin kasadar zabar jam’iyyar Labour Party ba a zaben shugaban kasa na 2023, Daily Trust ta rahoto.

Koda dai Ekweremadu ya yi furucin ne jim kadan bayan an sanar da Gwamna Ifeanyi Okowa na jihar Delta a matsayin abokin takarar Atiku, yanzu haka bidiyon na nan yana yawo a shafin soshiyal midiya.

Address

Waff Road Kaduna
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abokiya HAUSA News Magazine posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abokiya HAUSA News Magazine:

Share

Category