29/09/2022
ATIKU KAWAI INSHA ALLAH
Maigirma dan takaran shugaban Kasarmu Nigeria Alhaji Atiku Abubakar a gurin kaddamar da littafin da ya rubuta jiya a Abuja, da yazo bayani akan harkan ilmi, yace "Ba zan yarda ‘ya’yana su fita kasar waje karatu ba idan na zama shugaban kasa"
Wato harkan ilmi yana daya daga cikin manyan kudurori guda biyar na Atiku Abubakar da yake son ya gyara idan ya zama shugaban Kasa
Zai gyara mana harkan ilmi ta yadda sai dai mutanen Kasashen waje su zo neman ilmi a Nigeria, da ikon Allah Atiku Abubakar zai aiwatar da wannan kuduri don babu wani shugaban siyasa a Arewacin Nigeria da ya kaishi zuba hannun jari a harkan ilmi cikin Nigeria da kuma bayar da tallafin karatu da kudin aljihunsa
Ko Sanata Rabiu Musa Kwankwaso bai kai Atiku bada tallafin karatu ba da kudin aljihunsa, duk tura yaran talakawa da Kwankwaso yayi karatu zuwa kasashen waje yayi ne da kudin Gwamnatin jihar Kano da ba da kudin aljihunsa ba, Atiku ne ya bada tallafi da kudin aljihunsa
Atiku zai zama alheri ga Nigeria InshaAllah