Sautul- haqq online media

Sautul- haqq online media Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Sautul- haqq online media, Media/News Company, Bali Street no 4, Jalingo.

WANNAN SHAFI MAI ALBARKA AN QIRQIRESHI NE DOMIN YADA KARATUTTUKAN ADDININ MUSLINCI HARMA DA ABUBUWA ZAMANI, ZAMANTAKEWA DA SAURANSU FATAN MU ALLAH YA ALBARKACI WANNAN SHAFI (SAUTUL HAQQ ONLINE MEDIA).

31/08/2022
HOTUNAN Shugaban Ƙungiyar Izala Reshen Jihar Taraba Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo Ya Jagoranci taron tattaunawa da Ya'...
24/07/2022

HOTUNAN Shugaban Ƙungiyar Izala Reshen Jihar Taraba Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo Ya Jagoranci taron tattaunawa da Ya'yan Ƙungiyar da Safiya Yau lahadi a Masalacin Juma'a na Sheikh Ibrahim Bawa Maishinkafa dake a Garin Ibbi.

Taron Wanda Yasamu halartan Shugabanin Izala dake Kannan hukumomi 16 dake Jiha Taraba, hade da Masu ruwa da tsaki na Ƙungiyar.

Da Fatan Kowa Yakoma Wajen Iyalan sa Lafiya Allah Yasa Haka Amin.
📷🖊️ Usama MBello

JAMA'ATU IZLATIL BID'AH WAIKAMATIS SUNNAH (JIBWIS TARABA STATE)Shugaban Ƙungiyar Izala na Jihar Taraba Sheikh Dr. Ibrahi...
20/07/2022

JAMA'ATU IZLATIL BID'AH WAIKAMATIS SUNNAH (JIBWIS TARABA STATE)

Shugaban Ƙungiyar Izala na Jihar Taraba Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo

Shugaban Majalisar Malamai na Jibwis Taraba Sheikh Ahmad Muhammad Boyi da Shugaban Rundunar Yan Agajin Jihar Taraba Ustaz Muhammad Muhammad Usman.

Amadadin Kungiyar Mai Suna a sama na farin cikin Gayyatar Al'ummar Musulmin Zuwa Wajen Wa'azin Goron Sallah Wanda ta shirya Kuma za'agabatar k**ar Haka 👇

Ranar Asabar
24Dul'Hijja1443H
23Jul 2022

Wuri Garin Ibbi

MALAMAI MASU WA'AZI SUN HADA DA

Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo

Sheikh Imam Barkindo Jungudo

Sheikh Ibrahim Umar (Abokin Sarki)

Sheikh Ahmad Muhammad Boyi

Sheikh Dr. Salisu Ishaq

Ustaz Salihu Muhammad Barau

Sheikh Isa Shehu Rugga

Malam Usman Abdullahi Maimartaba

Sheikh Saad Raji Lau

Imam Abdulhamid Manga Zing

Imam Abdussalami Karim

Malam Nura Sani

Malam Isa Gambo Bali

ALARAMMOMI SUN HADA DA

Alaramma Mustapha Isa

Alaramma Babangida Mayogwai

Alaramma Abdurazaq Ahmad Goji Ibbi

Alaramma Babangida S. Topi Karim

Alaramma Abdulrasheed Lamido Gora

Alaramma Ansaruddeen Musa da sauran Malamai da Alarammomi.

Allah Yabada Ikon Halarta Amin

Sanarwa daga Sakataren Ƙungiya na Jiha Malam Musa Saad Luggere

🖊️ Jibwis Taraba Social Media

17/06/2022

TUNATARWA

Ita Duniya k**an gida ne Mai kofa biyu, ka shiga ta nan, ka fita ta can. Ba wani dade wa akeyi ba. Allah Ta'ala kasa Muna daga cikin waɗanda suke aikata aiki na kwarai, domin samun soyayar ka

14/06/2022

*RAYUWA:*

"Gaba dayanmu a dunia k**ar a dakin jarabawa muke! Kuma a kowane lokaci za'a iya qwace takardar! Kenan lokacin da Ubangiji ya dibar maka ya qare....!Don haka zaifi kyau ka maida hankali kan takardarka ka qyale ta wani.

Ba matsalarka bace me wani ya rubuta? ko mai zai rubuta? ko me yake rubutawa? Dan Allah zai tambayeka kan takardarka ne bata wani ba!!"

Allah yasa mudace!

12/06/2022

Ibn Ƙayyim ya ce
"Sau da yawa za ka ga mutum wanda ke ƙoƙarin guje wa alfasha da laifuka da zunubai, amma bai damu ba, yana sakin harshensa wajen cin mutuncin mutane; rayayyu da matattu. Kamar bai san cewa kalma guda ta ɓatanci da yake faɗi akan bayin Allah za ta iya ruguza ayyukansa ba".

Allah ka kare mu, kar ka bar mu taɓe.

10/06/2022

Yana da kyau iyaye su sanya idanu akan ƴaƴansu, kuma su sa ni Allah Ta'ala zai tambayesu. Haka kuma masu aikata alfasha cikin al'umma suji tsoran Allah su dai na.

Allah Ta'ala ka shiryar damu da zuri'armu, ka karemu daga afkawa cikin saɓan Allah.

KU SHIRYA WA FITA ZABE A RANAKUN ZABE:Dr. Ibrahim Jalo Jalingo 1. Kamar yadda mahankalta cikin Al'umma suke jan hankalin...
22/05/2022

KU SHIRYA WA FITA ZABE A RANAKUN ZABE:

Dr. Ibrahim Jalo Jalingo

1. Kamar yadda mahankalta cikin Al'umma suke jan hankalin baligai na su karbi katin zabe, haka nan ne kuma suke tunatar da su da su shirya wa fita yin zabe kwansu da kwarkwatansu a ranakun zabe.

2. Wajibi ne a kan al'ummar Musulmi su yi iya karfinsu domin su samar da shugaban da Shari'ah ta yi umurnin a samar da irinsa. Lalle wajibi ne su yi hakan a duk inda suke. Kin yin haka daga gurinsu laifi ne babba a idanun Shari'ah.

3. Allah muke rokon Ya taimaki al'ummarmu da ake sharewa a jihar Taraba, da sauran bangarorin Duniya. Ameen.

20/05/2022

*Muhadara! Muhadara!!*

Ana gayyatan Yan uwa zuwa wajen muhadaran goron sallah da za'ayi a yau jumma'a Mai taken: *mahimmancin saka hijabi ga ya' mace*

A Izala central mosque Garba chede Wanda zai kasance bayan sallah Isha

Zaku iya samun audio a group din mu na WhatsApp Mai suna
*Sautul haqq online media*

19/05/2022

haramcin taba macen da bata halatta garekaba

manzan allah s'a'w yace:

Asokawa dayan ku allaurar karfe (Basilla) a kansa shiyafi alkairi a kan yataba matar da bata halatta gareshiba

19/05/2022

*SULHU A TSAKANIN MUTANE*

manzan allah s'w'a yacewa aba ayyub!

shin bazan nunama wata sadaqa da allah da manzansa suke santaba?
sai annabi s'a'w yace masa ka sasanta tsakanin mutanan da suke ke gaba s**a bata tsakaninsu

18/05/2022

Rasa masoya na daga cikin babban jarabta. Wanda ba kowa ke iya hakuri da juriya ba, sai mai karfin Imani.

Yaa ALLAH! Ka wadata mu da hakurin rashi, ka sada mu da masoyanmu cikin Aljannah AMIN.

15/05/2022

Duk abinda ya faru da Dan-Adam, muqaddari ne daga ALLAH (SW). Imani dashi zai sa muyi hakuri da juriya lokacin jarabta. Da hakane zamu samu biyan buqatah daga gareshi.

Kayi gwargwadon iyawarka, sauran kabarwa ALLAH (SW). Shine zai iya maka abinda ba zaka iya ba. Sannan ya nuna maka hanya madaidaiciya.

INNAA LILLAAHI WA INNAA ILAAIHI RAJI'UN !!!Daraktan Agaji na Kasa JIBWIS Engr. Mustapha Imam Sitti na sanar da 'yan Agaj...
14/05/2022

INNAA LILLAAHI WA INNAA ILAAIHI RAJI'UN !!!

Daraktan Agaji na Kasa JIBWIS Engr. Mustapha Imam Sitti na sanar da 'yan Agaji tare da sauran al'umar Musulmai rasuwar Babanin MAL. ABDULMUMIN SHU'AIBU KANO (Dep. Nat. Field Commandant) wadda ALLAH ya yiwa rasuwa ranar Alhamis 12/5/2022.

Muna addu'ar Allah yaji kanta ya Kuma gafarta mata.
(Dep. Nat. Pub. Sec.)

Kungiyar IZALA tayi Allah wadai da zagin Annabi (SAW) da wata yarinya tayi a jihar Sokoto …….Hukuma ce ke da hurumin yan...
13/05/2022

Kungiyar IZALA tayi Allah wadai da zagin Annabi (SAW) da wata yarinya tayi a jihar Sokoto

…….Hukuma ce ke da hurumin yanke hukunci ga wanda ya zagi Annabi, ba ‘dai’daikun mutane ba.

……Ya kuma yi kira ga Hukumomi da su dinga zartar da hukuncin kisa ga wanda ya zagi Annabi (S) Kafin jama’a su kai ga nasu hukuncin, Wannan ne kadai zai hana’dai’daikun mutane daukar mataki na kisa.

Kungiyar wa’azin musulunci ta Izalatil Bidi’ah wa iqamatis sunnah a tarayyar Naijeriya tayi Allah wadai da wata yarinya wacce ba musulma ba da ta zagi Annabi Muhammadu tsira da aminci su kara tabbata a gare shi . Yarinyar mai suna Debora wacce ke karatu a kwalejin Ilimi dake jihar sokoto, tayi mummunan zagi a wani zaure na WhatsApp da s**a bude a matsayin su na dalibai domin tattaunawa, Yarinyar ta kunduma ashariya ga Annabi (SAW) wanda duk musulmi bazaiji dadi ba, wanda hakan har yakai ga wasu jama’a s**a kasheta kuma s**a kona ta. Addinin musulunci bai bada dama ga musulmi ya zagi ko wane Annabi daga Annabawan Allah ba, dan haka akwai bukatar shugabannin kiristoci su dauki aniyar wayar da kan mabiyansu akan illar taba mutunci ko zagin fiyayyen halitta wanda hakan ka iya tayar da husuma a cikin kasa.

Sheikh Bala Lau yayi kira na musamman ga hukuma da ta dinga saurin daukan mataki na kisa ga wanda ya zagi Annabi (S) da wannan shi zai hana jama’a daukar nasu matakin, amma jama’a suna ganin ko an damka wanda yayi zagin ga hukuma Masu kare hakkin dan Adam zasu shigo ayi ta bugawa wanda hakan zai sa a saki wanda yayi zagin, yaci gaba da rayuwar sa ba tare da daukan matakin na shari’a a kansa ba. “Dan haka Ina kira ga hukumomi da su dinga aiwatar da hukuncin kisa ga wanda yayi zagin, Wannan ne kadai zai gamsar da mutane su daina daukar doka a gannunsu” Inji Shi.

Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau ya kuma yi kira ga jama’a a duk lokacin da irin haka ya faru idan an k**a wanda yayi zagin babu wani wanda yake da hakkin zartar wa wani haddi ko hukunci akan tuhumar da ake masa, har sai an gabatar da shi gaban alkali, shi ne wanda zai iya tabbatar masa da wannan laifin ko ya wanke shi.

“Al-Imam An-Nawawi: “Babu wanda yake da hurumin tsayarwa da mutane masu ‘yanci haddi sai shugaba, ko wanda shugaba ya nada, domin babu wanda ya taba zartar da hukuncin haddi akan wani a zamanin manzon Allah (S.A.W) sai da izininsa. Haka abin yake a zamanin halifofinsa duka. Saboda tsayar da haddi wani abu ne da yake bukatar zuzzurfan ilimi, kuma za a iya yin zalunci a cikinsa, don haka bai halatta ba sai da izinin shugaba”. [Al-Maj’mu’, juz’i na 20, shafi na 34].

Al-Imam Al-Kurtubi: “Babu sabani tsakanin malamai cewa, haddin kisa, babu wanda yake da hurumin tsayar da shi sai shugabanni. Su ne aka dora musu wannan alhaki a wuyansu”. [Tafsirinsa, Bakara, aya ta 187].�A wani gurin yana cewa, “Malaman fatwa sun yi ittifaki kan cewa, ba ya halatta ga wani ya yi wa wani haddin kisa, in banda shugaba. Mutane a junansu ba su da wannan hakkin. Wannan hakkin shugaba ne ko wanda shugaba ya nada”. Tafsirinsa, Bakara, aya ta 179.

Malam Ibn Rushd: “Malamai sun yi ittafiki cewa, shugaba ne kadai yake da hakkin tsayar da haddi” Bidayatul Mujtahid, juz’i na 4, shafi na228.

Don haka dole ne jama’a su fahimci, kuma su fahimtar da cewa, wannan aiki da wasu s**a dauka ba koyarwar musulunci ba ne, kuma ba wani malami na musulunci da ya taba fatawar aikata irin wannan aika-aika da sunan son Annabi (S.A.W), ko kishin musulucni, kuma musulunci yana tir da irin wannan ta’asa a duk inda aka yi ta.

A karshe shehin Malamin yayi kira ga hukumomi Kira ga hukumomi da kan daukan mataki domin hukunta masu irin wannan laifi da gaggawa don toshe kafar hana irin wannan saboda masu daukan doka a hanu.
Allah ya ganar da mu. Amin.

JIBWIS NIGERIA

13/05/2022

KANA ZAUNE KA KASHE KANKA 👇👇

~ Baka da aiki sai yin zina, shin kasan cewa ita gubace kuma dattice da bata wankuwa da wuri sannan bala'i ce dakan dawwamar maka da talaucin lahira da duniya?

~ baka da aiki sai istimna'i, shin kasan cewa ita din sabon Allah ce da takan kashewa mutum lafiyarsa ta ciki da ta waje sannan ta jefa kunci a ratuwarsa?

~ Baka da aiki sai shan kida, shin kasan cewa hakan wani babban dabi'a ce dakan haifar da munafunchi da rashin son jin wa'azi a ckn zuciya?

~ Baka da aiki sai shaye-shaye, shin kuwa kasan cewa hkn babban laifi ne dakan nisantar da kai daga rahamar Allah sannan ya ruguzamaka lafiyarka?

~ Baka da aiki sai kallon tsaraici, shin kasan cewa kuwa a kowanne irin yanayi zaka iya tsintar idanuwanka sun daina aiki (makanta)

~ Baka da aiki sai gulmar mutane, shin wai k**a san cewa cin naman yan uwanka kakeyi kuwa, sannan kana qara zurma kanka ckn wutar da nisanta yafi sammai da qassai ne?

~ Baka da aiki sai sace-sace, shin kasan cewa duk abinda ka sata sai an dora mk shi ranar tashin Alqiyama kayi gudin fanfalaqi dashi kuwa?

Ya ubangiji mai ikon juya zukata ka tabbatar da zuciyoyinmu akan shiriyarka

10/05/2022

*_SIRRIN MACE TA GARI_*🧕🧕

A kullum Farin cikin mijinta shine Farin cikinta bata duban surutun mutane Akanta Sak**akon biyayyar da takewa mijinta,

Mai Sallah ce akan lokaci, Da yawaita ambaton ALLAH, Da kiayaye amanonin Mijint, Farjinta da kuma Dukiyarsa,

Mai kokarin tarbiyyantar da yaranta ne akan tafarki na addinin islama, bata ajiye Videos Na Kade -kade da wake-Wake ko Videos na Banza a wayarta Domin gudun lalacewar tarbiyyar yaranta.

Itace mai kiyaye Hakkokin mijinta, mai Kulawace wajen jinsa, 👂Magana mai dadi mai tausasa Harshenta garesa ko da ku yana mata fada ne, Da kuma Hancinsa👃kar yaji wani wari ko bashi a jikinta.

Mai mika lammuranta ne ga ALLAH Shi kadai, Da Dogaro gareshi ga dukkan jarrabawar da yamata na rayuwa.

Bata fitr da Sirrin gidan ga kowa,ko dq iyayenta,Komai damuwar d take ciki takan fadi Gaban ALLAH {SW} tna mai zubar da hawaye,tna mai addu´a tana mai imani Da ALLAH Zai amsa rokonta, tana mai Neman Shiriyar mijinta da `ya`yanta.

Madallah da mace tagari Mai yawaita ibada ga ALLAH, Da biyayya ga Umarnin ALLAH{SW}da kuma mijinta🥰

Mace tagari bari Nabaki Sirrin Addu'a domin Kara mallakan Zuciyar mijinki, batare da kinje wajen Wani mushiriki Yafada maki karya ba, Dama nasani cewa duk mace tagari Takan mallaki zuciyan mijinta ta hanyar da musulunci ya lamince mata, da kuma Baiwar da ALLAH yamata na zamowa Cikkkiyar mace addini,kuma sanyin idniyar mijinta, Hanya tafarko yimasa ladabi da biyayya, Yi nayi bari nabari, sannan Kyautatawa, Tsafta, iya girki mai dadi, Nuna kwadayin kasancewa tare da shi a kowane lkci, iya Soyayya da wasan barkwanci, Tausasa lafazi gareshi, Share masa hawaye, Kankan da kai zuwa gareshi a matsayinsa na shigaba a gareki, Sannan ina horonki da kiji tsoron ALLAH ga lamarin mijinki, Kar ALLAH Yabaki zuciyarsa ki zamo mai cutar dashi wallahi ALLAH Bazai barki ba🙂domin ALLAH bayason zalinci.

07/05/2022

🌹 *TUNATARWA* 🌹

*"Kada yawan abun da wasu s**a tara ta hanyan haram ya ruɗe ka kai ma ka biye musu, rayuwa albarka ne ba yawa ba, Kuma duk abun da yake rabonka ne idan ka yi hakuri zaka same shi ta halal"*.

04/05/2022

Ibnul Qayyim (Rh) ya ce: "Muminin da ya dogara ga Allah, idan halittu s**a qulla masa makirci, Allah zai mayar da makircin da a ka yi masa, kuma zai taimake shi ba tare da dabararsa ko qarfinsa ba".
إعلام الموقعين (٢٢٠/٣)

02/05/2022

*Assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatuh barkan ku da warhaka al'ummar wannan group mai albarka na _sautul haqq online media_ muna yi maku barka da sallah tare da fatan za'ayi bukukkuwa cikin farin ciki da annashuwa muna rokon ubangiji Allah ya karbi ibadun mu da muka gabatar a watan Ramadan da ma wadanda zamu aiwatar a wajen sa Allahumma ameen ya hayyu ya qayyum Allah kuma ya maimaita mana bayan haka fatan alkhairi gare ku bisa ga yadda kuke kasancewa da mu a koda yaushe barikallahu lakum wa taqabbalallahu minna wa minkum bissalam.

Bayan Yan agaji sundawo daga idi 👏👏👏
02/05/2022

Bayan Yan agaji sundawo daga idi 👏👏👏

GARBA CHEDEALHAMDULILLAHGODIYA TA TABBATA GA ALLAH MADAUKAKIN SARKI MAIBKOWA MAI KOMAI  MAQAGIN SAMMAI DA QASSAI DA ABAB...
01/05/2022

GARBA CHEDE

ALHAMDULILLAH

GODIYA TA TABBATA GA ALLAH MADAUKAKIN SARKI MAIBKOWA MAI KOMAI MAQAGIN SAMMAI DA QASSAI DA ABABEN DAKE CIKINSU,

GODIYA TA MUSAMMAN ZUWA GA
MALAMAMMU DAKE GARIN GARBA CHEDE,

1. KHALID HASSAN (CHIEF IMAM)

2. ASHEER YUSUF (DEPUTY IMAM)

3. MUSA HUSSAIN (DA'AWA CHAIRMAN)

4. IDRIS JIBRIL (CHIEF IMAM IN NYAMATA MANDA AS WELL AS 4th IMAM AT GARBA CHEDE)

5. MALAM YAQOOB (ALARAMMA 1)

6. Fa'IZZ HARUN (ALARAMMA 2)

7. SADAM NASIR ADAM (ALARAMMA 3)

DAMA SAURAN MALUMAMMU DAS**AYI KARATU ASAURAN YANKUNAN GARBA CHEDE,

GODIYA TA MUSAMMAN ZUWA GA DUKKAN WADANDA S**A DAU NAUYIN QADDAMAR DA IBADU NA WANNAN WATA MAI ALFARMA CIKIN TALAKAWANMU DAMA MASU KUDINMU

MUNA ROKON ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA AMSHI IBADUMMU YAKUMA GAFARTAMANA ZUNUBBANMU YASA MUNA CIKIN YANTATTUN DA AKE YANTAWA CIKIN WANNAN WATA,

MUNA FATAN ALLAH UBANGIJI YA DAUKAKA GARIMMU NA GARBA CHEDE
YAQARAMANA ZAMAN LAFIYA, TATTALIN ARZIKI DA INGANTACCEN RAYUWA AMEEN 🤲🤲🤲

ABIN DA MURAKKABAN JAHILAI KE YI A NIGERIA ABIN TAKAICI NE:Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo 1. A Shari’ar Musulunci Sarki...
01/05/2022

ABIN DA MURAKKABAN JAHILAI KE YI A NIGERIA ABIN TAKAICI NE:

Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo

1. A Shari’ar Musulunci Sarkin Musulmi shi ne yake da hakkin ba da tabbacin ganin watan azumi ko na salla, ba wai waninsa ba, idan ganin watan ya tabbata a gurinsa sai ya sanar wa mutane ya kuma umurce su da daukan azumi ko sauke shi, ko kuma yin idin Layya.

2. Wannan shi ne yake rubuce a cikin mazhabar Hanafiyyah da Malikiyyah da Shafi’iyyah da Hambaliyyah. Kuma shi ne ingantacciyar sunnar Annabi mai tsira da amincin Allah ta zo da shi.

3. Amma abin takaici shi ne jahilai murakkabai ta kusan dukkan bangarori sun halakar da kawunansu kuma suna nan suna ta halakar da al’ummar Musulmi. Allah muke rokon taimako har kullum. Ameen.

Hotuna a wajen rufe Tafseer a garin nyamatamanda
29/04/2022

Hotuna a wajen rufe Tafseer a garin nyamatamanda

29/04/2022

Videon tallafawa marayu wanda kungiyan jibwis reshen G/chede Bali L.G Taraba state ta gudanar

Address

Bali Street No 4
Jalingo
660213

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sautul- haqq online media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sautul- haqq online media:

Videos

Share


Other Media/News Companies in Jalingo

Show All