Almeen S Aderm

Almeen S Aderm Master At Teloring

فَمِنْهُمْ مَنْ قَضَىٰ نَحْبَهُ...🥺A ƙarshe dai Abu Hisham ya cimma muradi. Bayan sanarwar da Kata'ib ta fitar jiya na t...
10/03/2024

فَمِنْهُمْ مَنْ قَضَىٰ نَحْبَهُ...🥺

A ƙarshe dai Abu Hisham ya cimma muradi. Bayan sanarwar da Kata'ib ta fitar jiya na tabbatar da Abu Hisham ya na raye, da yammacin yau Asabar an samu sanarwar ya cimma muradi (Shahada). Sakamakon raunuka da ya samu a yayin gudanar da aikin Allah, inda ya yi ajalin maƙiya kafin su samu nasarar farmakarsa.

Abu Hisham ɗa ne namiji tilo ga shahidi Kwamanda Hisham Amer, wanda yai shahada lokacin fafutikar intifadar farko wato tsakanin shekarar 1987 zuwa 1993 kenan. Sunansa Hamza, ya na da ƙanwa ɗaya mace, shi ma ya kai matsayin kwamandan fagen fama (field commander) a rundunar Ƙassam wacce mahaifinsa ya kai matsayin kwamanda.

Abu Hisham ya shahara ne bayan da hoton bidiyo ya nuna shi ya na sassarfa dauke da gurnetin harbawa (RPG) a kafadarsa, inda ya tarwatsa tankar yaƙi ta maƙiya Allah, daga nan a ka dinga yawo da hotonsa, a ka dinga yin zane-zane da su ke nuna bajintarsa a fagen fama, ba tare da shi ya ma san muna yi ba, a ƙarshe ya cika alƙawari.

–Baqeer Gashua
10/03/2024

An ruwaito daga imam Baqir (as) yana cewa:-"Mutumin dayake so yagane cewa inya mutu shin zaishiga Aljannah kokuma bazai ...
04/09/2023

An ruwaito daga imam Baqir (as) yana cewa:-

"Mutumin dayake so yagane cewa inya mutu shin zaishiga Aljannah kokuma bazai shigaba, shine ya lissafa yadda zuciyarsa take sonmu (Ahlulbaity), yakuma lissafa yadda darajarmu take acikin zuciyarsa.

Haka kuma imam yakara dacewa:-

"Babban abinda mutum zaiyi yatabbatar mana da soyayyarmu Acikin zuciyarsa shine ya koka da abinda yafaru da imam husayn (as) yakuma yadda Alamarin imam husayn (as) Ako ina.

✍️✍️Anas Isah Ismail.

24/04/2023

SHAYE-SHAYE A RAYUWAR MATASA

KADUNA PRESS

*Journalist Fatima khamis*✍🏻

MENENE SHAYE-SHAYE?

Shaye-shaye shi ne shan magani ko shaka ko yin Allura ba tare da umarni ko sa hannun likita ba, wanda ka iya rikita kwakwalwar mutum ya sa ya fita hayyacinsa.

Shaye-shaye ya zama ruwan dare a cikin Al'umma, wanda s**ai riko da shi ba Maza ba Mata, ba samari ba Yammata, ba babba ba yaro duk Ana samun masu Shaye-shaye a ciki.

A yau Shaye-shaye ya zama wani Abu wanda wasu har su ke ganin wanda baya sha a matsayin wanda bai waye ba. Abin ya na da matukar takaici da ban tausayi a sa'ilin da za ka ga matasa ba sa jin kunyar biyo hanya suna Shaye-shaye.

WASU ABUBUWAN DA SU KE JAWO SHAYE-SHAYE

1: Zaman banza da rashin aikin yi

2: Jahilci

3: Al'adu

4: Shiga bangar siyasa

5: Hulda da masu Shaye-shaye

6: Yanayin wurin da mutum ke zaune

7: Sakacin wasu Iyayen wurin tsawatawa yaransu

8: Aikin karfi(Leburanci)

9: Samun kwayoyin ba tare da shan wahala ba.

10: Gabatar da Rayuwa a unguwar da ake Shaye-shaye

11: Halin gallazawa wurin masu rikon yaro

21: Wani yanayi na talauci ko wani halin Rayuwa da sauransu....

WASU MATSALOLI DA SHAYE-SHAYE KA IYA JAWOMA MUTUM

1: Rage karfin garkuwar Jiki, wanda ka iya sa cututtuka su shiga jikin mutum cikin sauki

2: Yawan tashin zuciya

3: Fizge-fizge, da kuma damuwa ko matsalar rashin gane karatu

4: Matsalolin da su ka shafi Hunhu(Lungs)

5: Matsalar ciwon koda(kidney)

6: Birkicewar tunanin Dan Adam

7: Yana iya jawo ciwon zuciya da rashin Kwarin Jijiyoyin jini

8: Yawan tashin Zuciya ko kuma Amai(Vomiting) da sauransu...

Sannan Shaye-shaye ya na sa zubewar Zumunci da kimar mutum a Idon Al'umma, sannan babba da yaro kowa ganin marasa mutunci da tarbiyya suke masu.

WASU HANYOYI NE ZA'A MAGANCE HARKAR SHAYE-SHAYE?

Za'a iya magance harkar Shaye-shaye ta hanyar sama wa masu yi musamman matasa aikin yi, da kuma nisantar wadanda su ke Shaye-shaye, sannan kuma a rage tsangwamar su domin shima yana sa su Kara shiga wani hali

HAKKIN SHUHADA'UNAIRA DARI NE A WATA(N100)DUBU DAYA DA DARI BIYU A SHEKARA(N1200)Shin ka biya naka? Shin kin biya naki? ...
08/11/2022

HAKKIN SHUHADA'U

NAIRA DARI NE A WATA(N100)
DUBU DAYA DA DARI BIYU A SHEKARA(N1200)

Shin ka biya naka?
Shin kin biya naki?
Shin kun biya naku?

Hakki aka ce malam,ba infaki bane Hakki ne,wajibi ne akan kowa ya sauke nashi,nauyi ne a garemu baki daya,kuma komin daren dadewa sai ka biya.

Yan uwa ya kamata mu zauna muyi tinana,
sau nawa muke cin abinci a rana?
Da wane kalan sabulu muke wanka?
Wane irin tufafi muke sawa a jikin mu?
Takalmammu Kala nawane?

Amma muna tuna
ya yaran shahidammu suke? Muna Tina akwai masu kwana basu ci abinci ba?
Muna tuna wane irin kunci suke fuskanta lokacin da s**a tuna mahaifan su alhalin mu bamu riqe amanar da iyayen su s**a bar mana ba?

kayi tunani abincin dubu daya da Dari biyu (N1200) nawa yake?Mutum nawa ne ke cinye N1200 a cikinsu duk rana?amma wannan a shekara zaka bayar kana ganin kyashi?Wallahi muji tsoron Allah don Hakki abin tambaya ne.

Hakika SHUHADA'U sun bar mana amanar iyalansu, dole ne mu sauke hakkin su, ko kuma Allah ya tambaye mu, Karfa mu manta da jininsu addinin Allah zai tabbata,amma Kuma bama tausayawa abinda s**a bari.

Da ace kowa cikin mu zai biya nashi hakkin da za'a sami abinda za'ai masu hidima har a aje masu ragowa Saboda yawan mu, Amma mu biya Abu ya gagara.

Kuma saura kace na cika magana, na fada in kaji haushi ka biya.

Allah ta'ala duk wanda keda Niyyar badawa ka bashi ikon biya, wanda baida niyya kuma ka shirye shi ya Malikul Mutasaarrifu.

By Journalist Fatima ✍️

07/09/2022
18/08/2022

DANGANE DA LAMARIN DANDALIN SIYASA !!!

Da yawan mu muna fassara jagora (H) da son ranmu ne, wannan Ina magana ne da masu sauwala malam (H) jagoransu ne, amma suke shagube, ko fassara shi akan abinda basu gane ba, ko abinda munsan a hankali zamuji a lokacin da jagoran yaga ya dace ya sanar damu. (Mabiya).

Da ban mamaki idan akaji an gana da jagora shikenan kowa sai yata fassara jagoran da hasashe... Kuma a hakan muna sawwala mabiya ne mu.

Shikenan shi malam baida mutumci a wurin mu da bazamu iya jira muji matsayar shi ba tukunna. Ko kuma baida mutumcin da inma shi baiga dacewar fadin abinda ya tattauna da kowa ba dole sai munta qananan maganganu saboda tsabar munana mashi zaton zaiyi abinda bai dace ba Ko zaiyi abinda baiyi daidai da interest dinmu ba, wannan ya tabbatar da cewa Dayawan mu akan son ranmu muke bin malam (H) duk randa ya saba da son ranmu toh za'aji surutai a kafafen social media daga bakunan mu (mabiya) wasu irin mabiya ne mu? Lallai naga kamanceceniyar aikin mu da wasu marasa kan gado cikin sahabban Imam da Ali da s**a wahal da shi. Wani rashin kyautata zato da mukeyi wa Malam (H) yanzu wllh ko wa abokan mu da muka zauna dasu zama na amana bama yi.

Ni wallahi duk masu jujjuya maganar dandalin siyasa dinnan mamaki suke bani, kwana nawa ne kwata-kwata da faruwar ziyarar amma kowa nata hukunta harkar da jagora gwargwadon son ransa, ba'a tunanin a saurara aji matsayar jagora in yaga dacewar Asani, ba'a kuma kyautata zaton la'allah Komai ya fito daga gare shi Alheri ne.

Bari na qarqare da ba wa magauta haushi,wllh, tallahi,billahi, duk matsayar da Jagora ya bada akan wannan mas'alar da ma na baya da wanda zaizo gaba ni da irina muna kanta daram, ko an fadi me aka tattauna ko ba'a fadi ba bai shafeni ba, hasali ma ban buqata, inada jagora da nake fatan dauwama cikin masa biyayya, Ina rokon Allah ya bani sabaty na kasancewa tare da shi.

-Jamil Musawi Othman

18/08/2022
25/07/2022

-Hadisi Yazo Daga Maulana Imam Ja'afaru Sadiƙ (AS) Yana Cewa Duk Wanda Yayi Alwala Sannan Ya Karanta Waɗannan Addu'o'in Za'a Rubuta Masa Ladan lbadar Shekaru Hamsin 50.

-Ga Yadda Ake Yin Aikin: Kafin Mutum Yayi Alwala Sai Yayi Basmala Ƙafa Ɗaya (1), Bayan An Kammala Sai Ayi Tahamidi Ƙafa Ɗaya (1).

-Sai A Karanta Ayatul Ƙursiyyu Ƙafa Ɗaya (1), Sai A Karanta Suratul Ƙadar Ma'ana INNA ANZALNAHU Ƙafa Ɗaya (1), Sai Ayi Salatin Nabiy (S) Ƙafa Goma (10)." Shikkenan Kalas Angama.

-Yazo A Hadisi Sahihi Daga Manzon Rahama Annabi Muhammad (S) Cewa: "Duk Wanda Ya Zauna Babu Alwala To Duk Abinda Ya Same Shi Na Sharri Yayi Kuka Da Kansa."

-Sannan lta Alwala Tana da Falaloli Masu Yawan Gaske, Amma Ga Wasu Daga Cikin Falalolin:

1. Alwala: Tana Tsawaita Rayuwar Mutum.

2. Alwala: Tana Ƙarawa Mutum Kusanci da Allah Ta'ala.

3. Alwala: Tana Sanya Mala'iku Su Rubutawa Mutum Ladan Ibada Koda Mutum Yana Yin Barci Ne da Daddare.

4. Alwala: Tana Sanya Mutum Yayi Kyakyawan Ƙarshe Yayin Wafatinsa.

5. Alwala: Tana Sanya Allah Ya Gafartawa Mutum Zunubansa.

6. Alwala: Tana Sanyawa Mala'iku Su Rubutawa Mutum Ladan Zikiri Ko da Baiyi Zikirin Ba.

7. Sannan Kuma Sabunta Alwala Alhali Mutum Yana da lta, Tana Janyowa Allah Ya Gafartawa Mutum Zunubisa Ko da Ba'a Yi lstigfari Ba.

-8. Sannan Kuma Karanta Suratul Kadar Sau Ɗaya 1 Duk Bayan Kammala Alwala Tana Sanyawa A Gafartawa Mutum Dukkan Zunubansa Gaba Ɗaya.

9. Sannan Karanta Ayatul Kursiyyu Ma Kazalika Yana da Babban Lada da Ɗaukaka Darajar Mutum Bayan Duk Kammala Alwala.

-Allah Yasa Mu Dace, Bihaƙƙi Ahlul-Bait (AS).

-Muhammad Jiddah Nguru
07037009525

23/07/2022

DUK MAI KARANTA WANNAN BAYAN SALLAR FARILLA, ALLAH BAZAI TSAYAR DASHI AKAN MUNANAN AYYUKANSA BA RANAR ALKIYAMA.

"Manzon Allah yace: Duk wanda yake so kar allah ya tsayar da shi a ranar alkiyama akan munanan ayyukansa, kuma kar abinciki littafinsa, to ya ringa karanta wannan addu'ar a bayan kowani sallar farillah.

ALLAHUMMA INNA MAGFIRATAKA ARJA MIN AMALI, WA INNA RAHMATAKA AW'SA'U MIN ZANBI, ALLAHUMMA INKANA ZANBI IN DAKA AZIMAN FA AFUKA A A ZAMU MIN ZANBI, ALLAHUMMA IN LAN AKUN AHLAN AN TARHAMANI FARAHMATUKA AHLUN AN TABLUGANI, WATASA'ANI LI'ANNAHA WASI'AT KULLU SHAI'IN, BIRAHMATIKA YA ARHAMAR RAHIMIN. 🙏

🖍 Ja'afar Muhammad

Send a message to learn more

22/07/2022

*KANASON KWANCIYAR HANKALI DA ZAMAN LAFIYA?*

To ka dauki wadannan matakan:

1- Kafin ka furta magana ka yi tunanin irin amfani ko rashin amfaninta, nauyinta da tasirin ta ga wanda zaka fadawa.

2- Dukkan abinda zaka yiwa wani kayi tunanin in kai aka yiwa yaya zaka ji, kuma shi mutumin wane irin hakuri ko kawaici yake dashi?

3- In kana son a baka to kaima ka zama mai bayarwa.

4- In kanason ayi maka kara to ka zama mai yawan kara,

5-;In kana so a mutuntaka to ka zama mai mutunta kowa.

6- In kanason a taimakeka to ka zama mai yawan taimako.

7- Ka sani shiru ma maganace, zuru kuwa gargadine kauda fuska gudun fitinane.

8- Ka sani shekaru, ilimi, wayewa da kwarewa dukkansu basu amfani idan basu hana ka keta haddin wasu ba, ko raini ga mai maka kara ba.

9- Kayi taka-tsan-tsan wajen mu'amala da mutane don a nan ne ake gane wanene kai, hakan yana fahimtar da abokan mu'amala irin wacce tarbiyya aka gina ka akai.

10- In kayi tarayya da mutane ka zama akwai gudunmuwar da kake badawa kada ka zama tamkar dabba wadda ko turkenta sai an share abinci sai dai a ajiye mata in ta gama a kauda makayi.

11- Kada ka jira sai abokin mu'amala ya koka kafin ka taimakeshi, ka zama mai lura da walwalar kowa in kaga canji to ka bincika in kuma kayi hasashe to ka bada naka agajin gaggawar kuma kayi domin Allah kawai.

12- Bahaushe yace matar na tuba bata rasa miji don haka ka zama mai gaggawar lallashin wanda ka batawa koda dan da ka haifane wannan yana kara maka kima yana kuma kara dankon kauna da zumunci.

13- Ka zama mai son alkhairi ga dukkan abokin mu'amala, dan uwa, makwabci ko aboki kamar yadda kake sowa kanka. Wannan ya zama cikin kundin kudurce-kudurcenka.

Allah yasa mu dace

22/07/2022

Shaikh Zakzaky (H) Yace;

“Mu a wurin mu, alqur’ani shi ne mabudin Ilimi, shi ya bude kwakwalen mutane ga bincike; don ya na ta nuna musu su yi tsokaci dangane da halittar sama da kasa. Saboda haka, shi ne asalin a fara bincike-bincike har a gano abubuwa da daman gaske. Saboda haka, mu a wurin mu, Ilimi da addini ba su taba karo ba. Bilhasali ma, farkon ayar da ta sauka ta ce a yi karatu ne. Binciken Ilimi bai taba zama hadari ga aqidar Musulunci ba. Sai dai ma ya karfafa shi”.

(Cikin Tafsirin Suratul Fatiha)

15/07/2022

DUK KYAN RUBUTUN KA IDAN BA KA'IDOJIN RUBUTU KAMAR ‘Skeleton’ NE BA NAMA

--Inji Mal. Mal.Hamza Darazo.

Dayake jawabisa a muhallin Mu'utamar din Mediya Forum Yankin Bauchi da kewaye karona na 2 dayake kan gudana a Darazo dake Bauchi.

Yayinda yake gabatar da maudu'insa maitaken BITAR KA'IDOJIN RUBUTUN HAUSA DAKUMA HANYOYIN KAWATA RUBUTU.

Malamin yafarane da gabatarda Harshen Hausa da adadin gyare gyaren da akayiwa yaren yayinda dakuma yace bincike yanuna kusan kashi 65 na Nigeria suna amfani dayaren ne na Hausa.

Malamin yaci gabada fede Harshen na Hausa dakuma nuna yanda za'ayi amfani da shi dakuma ka'idojin Rubuta Hausar, inda yace "Duk kyan Rubutunka idan ba kàidojin Rubutu kamar skeleton ne ba nama, kuma Kwararrun masana hausa ne s**a hadu s**a rattaba wasu tayayyun ka'idoji da s**a kamata a bi wajen rubuta Hausa.

Su Wadannan ka'idojin tun a zamanin hukumar talifi da aka kafa a 1933 nan aka fara tsayar da su da tsarin harshen Hausa Wadda gwamnatin jihar Arewa ta kafa a 1955 ita mata a jami'ar bayero a ranar 22 gawatan satumba 1973 Wanda shi ma ya yi nazarin ka'idojin.

Sai kuma taron da aka yi a yamai ta kasar Nijar ranar 7 zuwa 12 ga watan junairu 1980 Wanda ya yi nazarin ka'idojin da ake bi ana amfani da Hausa a Nigeria da Nijar da sauran wurare yayinda aka rattaba su a Wuri daya don daidaita su su zama tsayayyun hanyoyin da ake bi a ko'ina inda za'a rubuta shi a kalmomi, da jimlolin Hausa da sauran su.

Misali gawasu ka'idojin Kamar yadda masana s**a zayyana su :

1. Ba a yi Amfani da bakin p sai dai f a rubutun Hausa, amma ana iya amfani da su a zayyanannun sunaye Kamar haka :

-Pakistan ba Fakistan ba.
-Sipikin ba Sifikin ba.
-Mustapha ba Mustafa ba.

Sauran kalmomi za'a iya Amfani ne da bakin F
Fensir, Pensir

2. Ba'a amfani da hw da hy hy da fy a daidaitacciyar Hausa.

Misali:
Sarkin fawa. ba Sarkin hwawa ba
Farauta ba. hwarauta ba.
Fyade ba hyade ba."

Wannan kaɗan kenan daga cikin Jawabi Malamin inda malamin yayi gayan koka

19/05/2022

Yin addu'a ranar Alhamis
* ADU'AR DA AKE KARANTAWA ARANAN AL'HAMIS *

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
*BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM*
Godiya ta tabbata ga Allah wanda da ikonsa yake mayar da dare duhu.
* ALHAMDU LILLAHILLAZIE AZHABALLAILI MUZLIMAN BI
*QUDRATIHIE
Kuma ya zo da rana, yana duban rahamarsa.
*WAJAA'A BINNAHAARI MUBSIRAN BI RAHMATHIE*
Ya tufatar da ni da haskensa alhalin ina cikin alherinsa.
* WAKASAANIE DIYAA'AHU WA ANA FIE NI'IMATIHI *
Ya Allah kamar yadda ka kiyaye ni gareshi, to ka kiyaye ni da kwatankwacinsa.
* ALLAHUMMA FAKAMAA ABQAITANIE LAHU FA ABQINIE
LI'AMSILIHIE*
Kuma ka yi salati ga Annabi Muhammadu da alayensa.
*WA SALLI ALAA MUHAMMADIN WA AALHIE*
Kuma kada ka yi baƙin ciki a kansa ko waninsa.
* WALAA TAF'JA'ANIE FIEHI WAFIE GAIRIHIE *
daga darare da yini da aikata zina da zunubi.
* MINALLAYAALI WAL'AYYAAMI BIRTIKAABIL MAHAARIMI
WAKTISAABIL MA'AASIMI*
Ka ba ni alherinsa da na alherin da ke cikinsa da na alherin da ke biye da shi.
* WA KHAIRA MAA FIEHI WA KHAIRA MAA BA'ADAHU *
Kuma ka kawar mini da sharrinta, da sharrin da ke cikinta, da abin da ke biye da shi.
* WASRIF ANNIE SHARRAHUO WA SHARRA MAA FIEHI
WASHARRA MAA BA'ADAHU *
Ya Allah ina karkashin kariyar Musulunci, ina rokonka.
* ALLAHUMMA INNIE BI ZIMMATIL ISLAMI ATAWASSALU
*ILAIKA
Kuma da alfarmar Alqur’ani na dogara gareka.
* WABI HURMATIL QUR'AANI A'ATAMIDU ALAIKA *
Kuma tare da Muhammad al-Mustafa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da alayensa, ina neman cetonka.
* WABI MUHAMMADIL MUSTAPHA SALLALLAHU ALAIHI WA
AALHIE ASTASHFI'U LADAIKA *
Ya Allah ka sani laifina wanda nake fatan biyan bukatata dashi.
* FA'ARIFFILLAHUMMA ZIMMATIELLATIE RAJAUTU BIHAA
QADAA'A HAAJATIE*
Ya Mafi Rahamar Masu Rahma.
*YA AR'HAMARRAAHIMIEEN*
Ya Allah ka kaddara mini ranar Alhamis biyar:
*ALLAHUMMAQDILIE FIL KHAMISI KHAMSAN*
Karimcinka ne kawai zai iya saukar da ita.
* LA YATTASI'U LAHAA ILLA KARAMUKA *
Kuma alherin ku ne kawai zai iya jurewa:
*WALAA Y

10/05/2022

**HADISAI MASU BADA TSORO**
********AKAN ZA'LUNCI*********
AKULA SOSAI DA ZALUNCI DA AZZALUMAI DA GOYON BAYANSU

-Manzon Allah ya ce, Duk wanda yayi tafiya tare da Azzalumi domin ya taimaka masa kuma ya san cewa zalunci zai yi to hakika ya fita Musulunci.
*Wannan Hadisi yana da ban tsoro*

-Imam Sadik ya ce, Duk wanda ya ba Azzalumi uzuri kan zaluncin da yayi to ba zai bar duniya ba sai Allah ya sallado masa wanda zai zalunce shi kuma ba zai samu lada na zaluntar sa da aka yi ba

-Imam Sadik ya ce, Mai yin zalunci da wanda yake taimaka masa da kuma wanda yaji dadi ko ya yarda da abunda aka yi to dukkansu sun yi tarayya a zaluncin da aka yi.

Saboda haka lalle mutum yayi hattara da Azzalumi yayi zalunci ya goyi bayan abunda aka yi ko yaji dadi koma ya taimaka akan zalunci,shi azzalumi dama ya sai da lahirarsa domin ya samu duniya wato shi akalla ya samu duniya kafin ta kubuce masa lahira kam yayi asararta,

to amma ga wanda ya goyi baya ko yaji dadi kan abunda aka yi shi yayi asarar duniya da lahira ne kasantuwar gobe kiyama za a tattara shine da Azzalumai su fuskanci makoma guda

ALLAH YASA MUDACE

Husainiyya Islamic production yola

08/05/2022

Ya ku jama'ar ArewaShaikh Zakzaky na magana da ku.....Ku kalla ku saurara.

08/05/2022

TSOKACIN JAGORA SHAIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H) KAN HALIN DA KASA KE CIKI

"Wannan irin ƙasa, mutane suna ta ɓaganniya, ana yaƙarku amma ba ku gane ba. (Ana kaɗa ku) kamar shanu. Ka san saniya ina ruwanta in ma ƙwata za a kai ta (a yanka)? Ana tafiya tana cin ciyawarta.... Amma mutum wanda yake da hankali, kuna gani ana neman a ƙarisa ku, a gurgunta ku da ƙarfin tsiya.

"Har ma an riga an gama gurguntawar, ana ta ta yi ne, kudinku baya sayan komai. A 1980 Dala 1 ne Naira 2, Yanzu Naira 570+ ne Dala 1, amma da kuwa Naira 2 ne Dala 1. To kuma amma wai mu ke da 'Golden Zone', amma kudinmu bai da daraja.

"Mu nan irin diban 'Gold' din da suke a kewayen Zamfara din nan, Helicopters suke zuwa da shi su yi ta diba, har mutane sai su ce sun ji karar jirgin sama, wasu Helicoptoci ne, kuma 'Gold' ake diba a yi waje da su, ba tare da biyan ko kwabo ba. Kuma su wadanda ake cewa shugabannin sun sani. Su abin da ya dame su kawai a basu nasu kason.

"Kuma ni na lura magana ma in ka yi ma (kamar) ba amfani, saboda su mutanen kasar nan ma in ka yi maganar ma suna cewa kai mahaukaci ne. Wata rana da nake magana din nan, su wadanda nake maganar don su lura amma ba su damu ba, amma sai aka ce har wani General ya daki tebur, yace wannan mutumin 'is dangerous!' ka ga yana magana da talakawa ne. Lokacin da nake cewa ku gane ba wata Boko Haram, mai suke diba, yanzu haka akwai rijiyar mai 25 a Borno, mai ake diba. Shine ya bugi Tebur yana cewa akwai hadari don ana fadawa talakawa ne. To su kuma talakawar ba su damu ba ma....

"Wato muna wata irin kasa ce da komai ya faru, in musiba ta samu wani mutum, sai ka ga kamar ma har murna suke yi. Sai su yi ta murna. Ka san da ban mamaki ko? Idan musiba ta samu wani sai ka ga wani yana murna. Shima sai tasa ta zo, sai ya yi bakin ciki, sai wani kuma shima ya masa murna. Sai ta je ga wancan, ka ga ba wanda ya san yaushe za ta kare kenan.

"Yanzu wa ya san ya al'amari zai kasance nan da baɗi, ko kuma bayan shekara biyu zuwa uku? Tunda abubuwan suna gudu ne ba kadan ba, gudu suke ba kadan ba. Da ana bin jirgin kasa, an fi aminci, to yanzu jirgin kasan ka ga abin da s**a yi masa. To daga nan kuma ka ga yanzu ba aminci kenan a jirgin ma ko da an gyara shi....

"Su abin da kowanne (daga Mahukuntan Kasar nan) yake da bukata shine a bashi mukami, ala bashi a yi duk abin da aka ga dama. Ko me aka ga dama a yi, shi dai a bashi mukami. To. Idan ka ce ga mafita, mutane s**a ce ba haka nan bane. Ya za ka yi da su? Ba sai ka kyale su ba? Muce to shikenan ku nemi mafita inda za ku samu. Amma an ce musu ga mafitar, sun ce ba haka bane.

"Wasu su kan ce eh gaskiyarka ne, musulunci din ne mafita, amma fa kai kana nufin Shi'a ne, mu kuma ba za mu yi Shi'a ba. Ta wani dan Tawayiyya yace, wai yanzu in ma aka yi 'revolution' a kasar nan za a kafa Gwamnatin Shi'a ne, shi kuma da a yi shiaa gara ma a cigaba da Dimukuradiyyar. Yace gara 'Statuesque' da ISLAM wanda shi a wajensa sunansa Shi'a. To sai mu ce ai ba wata matsala, kai ka yi Sunnah Islam din mana. Shi kuma ba zai yi ba. Sunnah Islam din nasa shine ya bi azzalumai. Ya samu nasa kason.

"To yanzu kuma na ga ko a Shi'a din ma abin da (wasu) suke ta matsawa a kan mu kenan. Wai sai mu hada kai da azzalumai mu rayu. Shi kuma azzalumi ba ruwansa shi, ko me ka masa, ko Sujjada ka masa ma yanka ka zai yi. Ko Sujjada ka masa, kace yanzu ka tuba ka mai she shi ubangiji, zai ce kai Sujada mu gani. In ka yi ya dauko bindiga (ya nemi ya kashe ka). Duk abin da ka masa ba zai ta a yarda da kai ba (matukar ka taba masa bara'a). Amma ta yiwu in tun farko dama baka masa tawaye ba, kana tare da shi ne, ya zama ka samu rabonka a wajensa....."

— Yanki daga bayanan Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) yayin ganawa da Maziyarta a ranar Juma'a 6 ga Shawwal 1443 (6/5/2022).


08/05/2022

Address

Kofar Idi Bauchi
Bauchi

Opening Hours

09:00 - 17:00

Telephone

+2348140296934

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Almeen S Aderm posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share



You may also like