Niamey Online

Niamey Online Informations de contact, plan et itinéraire, formulaire de contact, heures d'ouverture, services, évaluations, photos, vidéos et annonces de Niamey Online, Société de médias/d’actualités, Niamey, Niamey.

A kudancin Ukraine, kekuna suna jiran dawowar masu suDaruruwan kekunan da aka yi watsi da su a wani karamin gari da ke k...
03/10/2022

A kudancin Ukraine, kekuna suna jiran dawowar masu su

Daruruwan kekunan da aka yi watsi da su a wani karamin gari da ke kusa da layin gaba na kudancin Ukraine, sun ba da labaran da yawa na masu su, wadanda aka tilasta musu tserewa daga mamayar Rasha.

Gasar wanka na Omaris Fashion 2022
31/08/2022

Gasar wanka na Omaris Fashion 2022

Karfe 00:03 daga nan babban Birnin Jamhuriyar Niger ( Niamey)
26/08/2022

Karfe 00:03 daga nan babban Birnin Jamhuriyar Niger ( Niamey)

🙏 Allah Yajikan Maza
08/08/2022

🙏 Allah Yajikan Maza

03/08/2022
Wasu da ake zargin mayakan jihadi ne sun kashe fararen hula fiye da 130 a tsakiyar kasar Mali, in ji jami'aiWasu da ake ...
21/06/2022

Wasu da ake zargin mayakan jihadi ne sun kashe fararen hula fiye da 130 a tsakiyar kasar Mali, in ji jami'ai

Wasu da ake zargin mayakan jihadi ne sun kashe fararen hula fiye da 130 a karshen mako a wasu garuruwan da ke makwabtaka da tsakiyar kasar Mali, wanda shi ne kisan gilla na baya bayan nan a yankin Sahel mai fama da rikici

Jami’an yankin sun ba da rahoton kisan gilla da wasu ‘yan bindiga s**a yi a Dillassagou da wasu garuruwa biyu da ke kewaye a da’irar Bankass, wurin da aka dade ana tashe tashen hankula a yankin Sahel .

Tun a shekara ta 2012 ne kasar Mali ke fama da tashe tashen hankula daga kungiyoyin boko haram, lamarin da ya jefa kasar cikin rikici.

Rikicin da ya faro a arewacin kasar ya bazu zuwa tsakiya da kuma makwabtan Burkina Faso da Nijar .

Niamey Online

Babban birnin kasar Libya ya yi kazamin fada tsakanin mayakan sa kai Wani kazamin fadan da ya barke da yammacin jiya Jum...
11/06/2022

Babban birnin kasar Libya ya yi kazamin fada tsakanin mayakan sa kai

Wani kazamin fadan da ya barke da yammacin jiya Juma’a tsakanin wasu ‘yan bindiga masu fada a ji, ya yi sanadin mutuwar akalla mutum guda tare da yin barna mai yawa, k**ar yadda wata majiyar tsaro ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP.

An yi ta harbe-harbe da fashe-fashe a fadin birnin Tripoli a lokacin fadan, wanda wani mazaunin garin ya bayyana da cewa mai yiyuwa ne "mafi nauyi" da aka gani a birnin fiye da shekaru goma.

Wannan dai shi ne tashin hankali na baya-bayan nan da ya girgiza kasar yayin da wasu firayim minista biyu masu hamayya da juna ke fafatawa a kan karagar mulki -- lamarin na baya-bayan nan na rikicin siyasa don cike gibin mulkin da ya barke bayan hambarar da gwamnatin marigayi Moamer Kadhafi a shekara ta 2011.

Hotunan da kafafen yada labaran Libya s**a watsa sun nuna fararen hula da s**a hada da mata na tura yara a cikin motocin daukar kaya, suna gudu a kan tituna masu cunkoson jama'a a wani yanki da aka gina bayan an k**a su a cikin wuta.

Niamey Online

Mutunan Nigeria shin wannan Karon Sak zakuyi Ko Chanchanta Allah yazaba muku mafi Alkhairi Niamey Online
08/06/2022

Mutunan Nigeria shin wannan Karon Sak zakuyi Ko Chanchanta

Allah yazaba muku mafi Alkhairi

Niamey Online

DA DUMI DUMI: Bola Ahmed Tinubu ya lashe zaben fidda gwani na kujerar shugaban kasa a jam'iyyar APC da kuri'a 1668
08/06/2022

DA DUMI DUMI: Bola Ahmed Tinubu ya lashe zaben fidda gwani na kujerar shugaban kasa a jam'iyyar APC da kuri'a 1668

Eid Mubarak
01/05/2022

Eid Mubarak

30/04/2022

Shugaban kasa Mohamed Bazoum yanama Daukachin Al'ummar Nijar barka da sallah

MAFI MUNIN TARIHI DA ZALUNCIN FARANSA GA MUSULMIKasar France ta tara malamai musulmi guda 400, s**a yanke kawunansu da a...
22/04/2022

MAFI MUNIN TARIHI DA ZALUNCIN FARANSA GA MUSULMI

Kasar France ta tara malamai musulmi guda 400, s**a yanke kawunansu da adduna; A lokacin mamayar kasar Chadi a shekara ta 1917 miladiyya

Lokacin da Faransa ta shiga birnin Laghouat na Aljeriya a shekara ta 1852 AD, ta halaka kashi biyu bisa uku na al'ummarta... ta hanyar kona su da wuta, kuma duk a cikin dare daya

Faransa ta gudanar da gwaje-gwajen Nukiliya har sau 17 a kasar Aljeriya a tsakanin shekarar 1960 zuwa 1966, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane dubu 27 zuwa dubu 100 da ba a bayyana tabbacin adadinsu ba.

Lokacin da Faransa ta bar Aljeriya a shekara ta 1962, ta buda ma'adanai fiye da na al'ummar kasar ta Aljeriya a lokacin sunada ma'adanai miliyan 11 karkashinsu.

Faransa ta mamaye Aljeriya tsawon shekaru 132. Faransawa sun mamaye musulmi miliyan daya a cikin shekaru 7 na farkon zuwansu, kuma miliyan daya da rabi a cikin shekaru 7 kafin tafiyarsu.

Wani masanin tarihin kasar Faransa Jacques Gorky ya kiyasta cewa adadin wadanda Faransa ta kashe a kasar Aljeriya, daga zuwanta a shekara ta 1830 har zuwa tafiyarta a shekara ta 1962 sun haura musulmi miliyan 10.

Faransa ta mamaye Tunisia tsawon shekaru 75, Algeria shekaru 132, Maroko shekaru 44, da Mauritania shekaru 60.

A lokacin da Faransa ta shiga Masar a yakin da take yi, sojojin Faransa sun shiga masallatai da dawakansu, inda s**a rika yi wa mata fyade a gaban iyalansu.

Kuma sun sha barasa a cikin masallatai, kuma sun mayar da masallatai da dama matsugunin dawakansu.

A karshe saboda zalunci da karya sun ce Musulunci addinin ta'addanci ne, kuma Annabinmu Annabin ta'addanci ne

Wani abin mamaki sai ka ga wasu suna ta baje kolin wayewar kasar Faransa har ma suna kare ta suna mantawa da bakaken tarihinta.

Wannan ita ce Faransa.

Repost Daga: Editing: Munir Assalafiy

Allah ya ruguza makiya Musulunci da Musulmai.

CHIGABAN TARIHIN KASAR NIGER 3Maudu'i - RABA NIGER DA NIJERIYA Ƴardaji da Yekuwa karo na farko an raba su a dalilin mulk...
10/04/2022

CHIGABAN TARIHIN KASAR NIGER 3

Maudu'i - RABA NIGER DA NIJERIYA

Ƴardaji da Yekuwa karo na farko an raba su a dalilin mulkin mallaka na Faransa da turawan Birtaniya, inda yekuwa ta faɗa ɓangaren Nijar a ƙarƙashin mulkin mallakan faransa, inda kuma dukkanin Daura, Ɓaure da kuma Zango s**a faɗa Najeriya ƙarƙashin mulkin mallakan turawan ingila. TURAWA sun zo Ƙasar Hausa sun zo ƙasar hausa ne a ƙarshen ƙarni na 17. A shekarar 1906 zuwa 1908, Kaptin Tilho da kuma Majo O’shee’ sune s**a saka turaka 148 a matsayin shaida akan inda Najeriya ta tsaya zuwa inda Nijar ta fara. Turaka 63 suna da tsawon ƙafa 15, wanda aka turke a cikin ƙasa, abisa nisan ƙafa 4-5. A tsakanin turaka na 93 da 94 aka samar da iyakan Nijar da Najeriya, wanda ya raba ƴardaji dake Najeriya da yekuwa dake Nijar



Harshen Hausa shi ne mafi girma da kuma mafi sanayyar harshe a nahiyar Afirka, harshen hausa ya aro wasu kalmomi daga wasu harsuna musamman Larabci kana kuma harshen na tafiya tare da yanayin mu na zamani bisa al'adar cudeni-in cudeka. Harshen Hausa dai ya zama harshen yau da kullum ga miliyoyin jama'a da ba Hausawa bane a nahiyar Afirka

Hausa Bakwai sune

Daurawa,

Kanawa,

Gobirawa,

Ranawa,

Zazzagawa,

Katsinawa

Birmawa.

Zaria: yawancin mutanen dake zaria ba asalin tsatsan hausawa bane a mahanga ta tarihi, yawancinsu mutane ne ƴan asalin ƙabilar fulani, da kuma mutanen da s**ayi hijira zuwa zaria



Yawancin Hausawa Musulmai ne mabiya Sunna, suna bin mazhabin Malikiyya, wanda shine mazhabin da'aka basu tin a jihadin Usman Dan Fodiyo, Musulunci ya kasan ce a kasar Hausa ti kimanin karni na 11th, wanda akan iya bada tarihin Wali Muhammad dan Masani (d.1667) da kuma Wali Muhammad dan Marna (d. 1655) na jihar Katsina, wanda masu fatauci suke yada addinin zuwa garuruwan Hausawa, amman a karni 11, yawan cin Hausawa na wannan lokacin Maguzawa ne.

A farkon karni na 19th ne aka yi jihadi domin jaddada addinin musulunci a kasar Hausa, inda aka yaka sarkin Gobir mai suna Yunfa, sannan aka kafa daular musulunci ta farko a garin Sokoto a shekarar 1804. Hausa tun taka rawan gani sosai wajen yada musulunci a cikin kasar Hausa, da kuma Afirka ta Yamma, suna kiran sarakunan su da wakilai na Musulunci, amman sarkin Sakkwato shine Sarkin Musulmi.[37] Karatun Alƙur’ani yana da matuƙar muhimmanci a ƙasar hausawa, wanda tunda ada da yanzu sukeyi

Mafi akasarin hausawa musulmai ne, sabili da haka galibin al’dunsu da s**a shafi aure da haifuwa da mutuwa, duka sun ta’allaƙa ne da wannan addini. Sai ɗan abinda ba a rasawa na daga al’adunsu na gargajiya, musamman wajen maguzawa. Msulunci yana da matuƙar muhimmanci da tasiri a wajen Hausawa, ta yanda hakan Hausawa suke kallon duk wanda bahaushe ne amma ba musulmi ba k**ar ba bahaushe bane. Aikin hajji yana ɗaya daga cikin Rukunnan Musulunci guda biyar Hausawa suna zuwa aikin Hajji sosai zuwa makka, musamman ma mutanen Kano, Sokoto, da Katsina, Hausawa su kance Alhaji suna nufin wanda yaje Makkah ya yi Aikin Hajji, Jam’in sa shine Alhazai, mace kuma Hajiya. Hakan ya samo asali ne tin a karni na 19 a kasar Hausa, amman a karni na 21, kalman Alhaji da Hajiya yana daukan ma'anar mutum mai kudi, koda ko bai taba zuwa aikin Hajji ba



Ginshikokin al'adun Hausawa na da mutukar jarunta, kwarewa da sanayya fiye da sauran al'ummar dake kewayenta. Bugu da kari, akwai cincirindon al'ummar Hausawa a manyan biranen yammacin Afirka da arewacin Afirka da kuma yankunan cinikayyar al'ummar Hausawa da kuma yankunan da Hausawa s**a jima suna bi a hanyar ta zuwa aikin Hajji. Akwai kuma rubutattun adabi masu zurfi da kasidodi da kuma rubuce-rubuce a rubutun ajami da aka buga tun kafin zuwan Turawa 'yan mulkin mallaka na Birtaniya.

Har ila yau, kuma wani tsarin rubutu a ajami da aka kirkiro tun kafin zuwan Turawa, da ba kasafai ake amfani da shi ba yanzu.[43][44]
Hausawa mutane ne masu tsananin riƙon al’adunsu na gargajiya, musamman wajan tufafi, da abinci, da al’amuran da s**a shafi aure. Ko haifuwa, ko mutuwa, da sha’anin mu’amala tsakanin dangi da abokai da shuwagabanni da sauransu da kuma ala’amuran sana’a ko kasuwanci ko neman ilimi.

Tun daga zuwan turawa har zuwa yau, hausawa suna cikin alummomin da basu saki tufafin su na gargajiya sun ari na baƙi ba. Yawanci adon namiji a hausa baya wuce babban riga, da wando musamman tsala. Da takalmin fata ko ƙafa ciki da hula ƙube ko ɗankwara, ko dara. Idan kuma basarake ne ko malami ko dattijo, yakan sa rawani. Adon yamma kuwa, zane ne, da gytton yafawa, watau gyale da kallabi, da ƴan kunne da dutsan wuya watau sarƙa.[45] Mai Gari: A ƙasar Hausa shugaban ƙauye ko unguwa shi ake kira da Mai-gari

Hausawa suna da al'adu daban daban, k**an hawan sallah, hawan daba, bikin kamin kifi a Argungun, kalankuwa da wasanni irin su dambe dadai sauransu

Niamey Online

CHIGABAN TARIHIN KASAR NIGER 2TarihiSunan kasar :Jamhuriyar NijarAdadin jama'a: Miliyan 24.9 ( 2021)Babban Birni: YamaiM...
09/04/2022

CHIGABAN TARIHIN KASAR NIGER 2

Tarihi

Sunan kasar :Jamhuriyar Nijar

Adadin jama'a: Miliyan 24.9 ( 2021)

Babban Birni: Yamai

Manyan harsuna: Faranshi (na gwamnati), Larabci, Hausa, Songhai

Addinai: Islam, addinan gargajiya

Hasashen tsawon rayuwa: Shekaru 50 (maza), 52 (mata)

Abubuwan da tafi fitarwa: Uranium, kayan noma

Lambar waya ta kasa da kasa: +227

Daular Kanem-Bornu

Kanem–Bornu Empire ta kasance daula ce data taba kasancewa a inda ayau itace kasar Cadi da Nijeriya. Masanan kasashe larabawa suna kiran daular da Kanem Empire daga karni na 9th harzuwa sanda takasance daular musulunci Bornu ( Bornu Empire) a 1900. Kanem Empire CE tun daga shekara ta (c. 700 zuwa 1380) takasance ne kasashen Chad, Nigeria da Libya.[1] A matukar girmar daular ta tattara kasashe ba kawai daukacin kasar Chad ba, takai har zuwa kudancin kasar Libya (Fezzan) da gabashin Nijar, arewa maso gabas din Nigeria da arewacin kamerun. A yayin da Daular Bornu take a shekara ta (1380s zuwa 1893) takasance kasace a inda ake kira ayau arewa maso gabashin Nigeria, wanda tacigaba da girma fiye da daular Kanem, tatattari kasashen da ayau sune ko kuma suke daga cikin kasashe k**ar Chad, Nijar, Sudan, da Cameroon; amsameta daga shekara ta 1380s zuwa 1893. Farkon tarihin daular ansansa ne da jerin masu sarautar ko Girgam matafiyin bincike dan kasar jamus wato Heinrich Barth wanda aka gano a shekarar 1851

Kanem takasance a kudancin dake yankin kasuwanci da ake kira wato trans-Saharan trade dake tsakanin garin Tripoli da kuma yankin tabkin Cadi. Baccin mutanen biranen kasar kawai ta tattari harda wasu kungiyoyin al'ummu makiyaya masu amfani da harsuna k**ar Teda–Daza (Toubou).

Daga wani nazarin daya karbu, ansamu cewar masarautar tafara kafuwa ne a shekara ta 700 AD a karkashin makiyayan masu amfani da harshen Tebu-Kanembu. Ance mutanen Kanembu an tursasa sune s**abar yankunansu har zuwa kasar noma dake yankin kudu maso yammacin tabkin Chadi daga matsin siyasa da desiccation a tsohuwar mazauninsu, yankin nada yancin kanta tun asali, walled city-states belonging to the Sao culture. A karkashin mulkin Duguwa dynasty, Kanembu sun mamaye Sao, bawai bayan sun dauki aladun matanen ba.[4] ancigaba da gwabza yaki tsakanin su har zuwa karshen karni na goma sha shida (16th).

Samuwar Agisymba

Wani nazarin ya nuna cewar batacciyar kasar Agisymba wanda (Ptolemy ya ambata tun a tsakiyar karni na biyu (2nd) AD) itama mafiriyar daular Kanem din ce

Shugaba Hamani Diori ɗan siyasan Nijar ne. An haife shi a shekara ta 1916 a Soudouré, Yammacin Afirkan Faransa; ya mutu a shekara ta 1989 a Rabat, Maroko. Hamani Diori shugaban kasar Nijar ne daga Nuwamba 1960 zuwa Afrilu 1974 (bayan Charles de Gaulle, shugaban Faransa - kafin Seyni Kountché).

🐪Hausa a Niger

Hausawa al'umma ce dake zaune a arewa maso yammacin tarayyar Nijeriya da kudu maso yammacin jamhuriyyar Nijar. Al'umma ce mai dimbin yawa, sun bazu a cikin kasashen Afirka da kasashen Larabawa kuma a al'adance masu matukar hazaka, akalla akwai sama da mutane miliyan hamsin wadanda harshen Hausa shi ne asalin yarensu. A tarihi kabilar Hausawa na tattare a salasalar birane. Hausawa dai sun sami kafa daularsu ne tun daga shekarun 1300's, sa'adda s**a sami nasarori da dauloli k**ar su daular Mali, Songhai, Borno da kuma Fulani, a karni na 19 Hausawa suna amfani da Doki ne domin yin sifiri da balaguro. Mutane kimanin sama da miliyan 50 ne ke magana da yaren hausa a Najeriya, Nijar, Arewacin Gana da kuma wasu al’uma daga yankin Kaolack a senigal har zuwa khartum dake ƙasar sudan, Asalin inda zuciyar hausawa take shine garin Kano, Katsina da Sokoto.]

Asalin hausawa maguzawa ne, a ƙarƙashin mulkin sarakunan Haɓe, wanda suke yin bori da tsbbace-tsubbace, zuwan Shehu Usman Ɗan Fodio ne yasa ya jadddada addinin ƙasar hausa, ta hanyar yaƙar maguzawa da sarakuannasu na haɓe a Gobir, Zazzau da wasu yankunan ƙasar hausa. Wanda wannan jihadin ne yasa Usman Ɗan Fodio ya kafa Daular Khalifanci na Hausa Fulani a ƙasar hausa, kuma da yawan hausawa s**a karba musulunci a ƙasar hausa. Hakan yasa masarautun ƙasar hausa sun kasance a ƙungiyar Tuta ɗaya na Usman Ɗan Fodio. Hausawa suna kiran al’adansu da al’adan gargajiya, wacce sukeyi duk shekara, ko a talabijin ko Bidiyo, ko kuma aikace cikin al’amuran yau da kullum. Na daga cikin rubutun hausawa, suna yin rubutu ne asali da Ajami, rubutu ne da haruffan larabci amman a luggar hausa, kuma suna rubutawa ne a fallen takarda.

A farko-farkon karni na 1900, a sa'adda kabilar Hausa ke yunkurin kawar da mulkin Aringizo na Fulani, sai Turawan Mulkin Mallaka na Birtaniya s**a mamaye arewancin Nijeriya, da kuma kafa manufofin mulkin bayan gida, a bisa karkashen mulkin Birtaniya,'yan mulkin mallaka sai s**a marawa Fulani baya na cigaba da manufofin Aringizon siyasarsu, har yanzu dai mulkin gamin gambiza tsakanin Hausawa da Fulani shi ne yayi kane-kane a arewacin Nijeriya. Kodayake, Hausawa na farko-farko maharba ne, amma da zuwan Addinin Musulunci da kuma karbarsa da hannu bibbiyu ya sanya labari ya sha bambam. Daura Kasace wacce a kasani mai dadewa da tarihi a kasar Hausawa.A ƙabilun Fulani majiɓinta hausawa akwai Sulluɓawa, Mallawa Yolawa, Danejawa, Dambazawa da Modibawa. bahaushe yakan ce “ Bahaushe mai ban haushi. Kaso mutum ka rasa abinda zaka bashi”.[6] Miles a cikin littafin shi ya kawo ma'aunan da Hausawa suke la'akari da shi a hankalce wajen gane cikakken bahaushe, suna duba wadannan abubuwan k**ar haka

Addini

Garin Haihuwa

Ancestral

Jama’a

Ƙasa

Ƙabila

Birni Ko Gari

Launin Fata

🐪Bayajidda: Sunanshi Abu Yazidu. ya auri sarauniyar Daurama na wannan lokacin, sun haifi yara biyu. yaronsu mai suna Bawo ya Haifa Bakwai na Halas, sune Daurawa, Kanawa, Gobirawa, Ranawa, Zazzagawa, Katsinawa da kuma Birmawa, sannan kuma ya haifa yaran Banza guda Bakwai sune.
Hausa sun cakuɗe da wasu yare, ta yanda suke da ƙabilu k**ar su:

Hausa Fulani

Hausa Kanuri,

Hausa Buzu

Hausa Beri-Beri

Hausa: musulunci yana da matuƙar muhimmanci ds tasiri a wajen Hausa, ta yanda hakan Hausawa suke kallon duk wanda bahaushe ne amma ba musulmi ba k**ar ba bahaushe bane

🐪Fatauci, Ci rani da almajiranci

Hausawa sun shahara a fannin kasuwanci da safarar haaja zuwa wurare masu nisa. Kuma sunyi shahara ne wajen kutsa kai zuwa wasu ƙasashe, domin yaɗa addini ko neman aiki. Kusan ma ace afirka tsawonta da faɗinta babu inda basu buga ba. Tun ƙarni na goma sha ɗaya (11) hausawa ke hulɗa da ƙasashen larabawa. Suna ƙetara hamadar rairayi ta sahara, suna zuwa Maghrib (watau maroko da Aljeriya da Tunis) da lubayya ko Turabulus (watau Libiya). Kuma suna ƙetara chadi zuwa Sudan da Masar da Ƙasar Makka (Saudi Arabiya). Suna kai musu fatu, da ƙiraga da bayi, su kuma suna sayo tufafi da mak**ai. Wajen kudu da yamma kuwa, hausawa suna kutsa kai cikin ƙasar yarbawa, da Gwanja, da Dogomba, da AShanti a Ghana, a nan babban abin safarar su shine Goro da Gishiri. Su kuma s**an kai musu kanwa.
Bauta da Baranci a wurin bahaushe ba munanan abubuwa bane, musamman abinda ya shafi koyan sana’a, bawa yana fansar kansa ne ta hanyar sana’a kuma mai koyan sana’a yana yin barance ne a gidan mai koya masa ne. Irin wannan almajirancin ana kiransa bauta. Duk mai wata sana’a. Ko dan kasuwa, ko malami, yana alfaharin ace ga wasu sun koya a wurinsa har su n ƙasaita, kuma sun fishi.

Niamey Online

TARIHIN KASAR NIGER Wato Kasar Nijar dai ta kasan ce tana daya daga cikin kasashen Afrika ta yamma.Tana makwabtaka da ka...
08/04/2022

TARIHIN KASAR NIGER

Wato Kasar Nijar dai ta kasan ce tana daya daga cikin kasashen Afrika ta yamma.Tana makwabtaka da kasashe bakwai (Nijeriya, Libya, Aljeriya, Mali, Burkina Faso, Benin, Cadi). Tana da al'umma da ta kai fiye da mutum miliyan sha bakwai(17). Kuma tana da kabilu daban-daban, k**ar su: Hausawa, Zabarmawa, Fulani, Kanuri, Bugaje, Barebari, Larabawa, Tubawa, da Gurmawa. Nijar ta na daya daga cikin kasashen kungiyar tattalin arzikin kasahen yammacin Africa (CEDEAO).
Nijar ta samu ƴancin kan ta a shekarar 1960 daga Turawan mulkin mallaka na Faransa. Tana da arzikin ma'adani cikin kasa k**ar Zinariya, da Karfe, da Gawayi, da uranium da kuma Petur

Yankunan Gwamnatin kasar Sune:

Yankin Agadez

Yankin Diffa

Yankin Dosso

Yankin Maradi

Yankin Tahoua

Yankin Tillabéri

Yankin Zinder

Niamey (Babban birni

Jamhuriyar Nijar ta samo sunan ta ne daga kogin Naija duk kuwa da cewa ba ta kusa da wata babban mashigin ruwa. Nijar na makwabtaka da Najeriya da Benin ta kudanci, Burkina Faso da Mali ta yammaci, Aljeriya da Libiya ta arewaci, sai kasar Chadi ta bangaren gabas.

Kodayake sai a cikin karni na goma sha tara ne Turawa k**ar Mungo Park dan kasar Burtaniya, s**a fara shiga can bangaren kogin Naija, to amma dai tun kafin wannan lokacin Faransa ke ta kokarin ganin ta mallaki Nijar, inda ta samu nasara a shekarar 1890.

A wannan lokaci Faransa ta na da gwamnonin dake tafiyar da harkokin dukkanin yankunan da ta mamaye a yammacin Afirka ciki harda Nijar, wadanda ke aiki karkashin babban gwamna, wanda ke zaune a Dakar na kasar Senegal.
Ranar goma sha takwas ga watan Disambar shekarar 1958, Niger ta zamo Jumhuriya mai cin gashin kanta a karkashin ikon Faransa.
Sannan a ranar uku ga watan Agusta na 1960, jamhuriyar Nijar ta samu 'yancin kai, wato shekaru hamsin da s**a wuce.

Jamhuriyar Nijar ta yi fama da juyin mulki daga sojoji daban daban wadanda s**a mamaye madafen iko a kasar bayan ta samu 'yancin kai.

Kasar wacce ke fama da matsanancin fari, na fadi-tashin ciyar da jama'arta.
Babban abin da take fitarwa dai shi ne ma'adanin Uranium wanda shi ma a shekarun baya ya fuskanci rashin tabbacin farashi, yayin da kwararowar hamada ke barazana ga aikin noma.

Amma a gefe guda kasar na fatan fara hako man fetur wanda ka iya bunkasa tattalin arzikinta. Bayan samun 'yancin kai, kasar ta fuskanci mummunan fari wanda ya lalata albarkatun noma.

Kasar dai ba ta da wani tsarin ilimin Firamare na azo a gani, abin da ya sa take cikin jerin kasashen da ke fama da rashin ingantaccen ilimi a duniya. Harkar lafiya ma ba ta da kyau sosai, kuma akwai yaduwar cututtuka a ko'ina cikin kasar.

A lokuta da dama kasar ta yi fama da boren 'yan tawayen Abzinawa a Arewacin kasar. Sai dai a shekara ta 2009, gwamnati da 'yan tawayen sun sanya hannu kan yarjejeniyar samar da zaman lafiya a birnin Tripoli na kasar Libya.

Niamey babban birnin kasar Nijar ne. Wannan birnin yana a matsyin babbar gundumar Birni kuma ya hada gunduma biyar ne. Bisa ga ƙidayar jama'a a shekarar 2011, jimilar mutane 1,302,910 (miliyan ɗaya da dubu dari uku da biyu da dari tara da goma). An gina birnin Niamey a farkon karni na ashirin bayan haifuwan annabi Issa. Babban kogin nan na "Niger" wanda cibiyarshi take tsakanin Sierra Leone da Guinée, y ratsa birnin Niamey.

Birnin Niamey ya fara ci gaba ne wajen shekarar 1900, a daidai wani waje inda Fulanin Koira, Gaweye, Kalley, Maourey, Zongo, Gamkalé da Saga suke a lokacin. Kabilar da tafi yawa sune Zabarmawa ko kuma Songhai. Turawa sun iso Niamey ne a makare saboda tana can yammacin kasar inda babu wani kasuwanci da akeyi. Mutanen Gurmance (Gourmantché) ne s**a fara rayuwa a yankin Niamey. Amma, wadanda s**a kafa kauyen Niamey, Arawa ne da s**a zo daga Matankari

Niamey Online

Wata tsohuwa ‘yar shekara 102 mai suna Misis Nonye Josephine Ezeanyaeche ta bayyana aniyar ta na tsayawa takarar kujerar...
01/03/2022

Wata tsohuwa ‘yar shekara 102 mai suna Misis Nonye Josephine Ezeanyaeche ta bayyana aniyar ta na tsayawa takarar kujerar shugaban kasa a zaben 2023 mai zuwa. A Nigeria

Ta ce tana da tsare-tsare masu kyau ga Najeriya idan a karshe ta zama shugaban kasa

Ezeanyaeche, wacce kuma ake kira ‘Living Legend’ da ‘Mama Africa’, ta fito ne daga Aguata a jihar Anambra, kuma ita ce ta kafa kungiyar ‘Voice for Senior Citizens of Nigeria’.

A wata ziyarar da ta kai wa tawagar gudanarwa na Hukumar Gidan Talabijin ta Najeriya (NTA) kwanan nan, ta bayyana shirye-shiryen ta na tsayawa takarar babban mukami idan matasan kasar nan ba su shirya ba.

Me zakuche..... Akan Ra'ayin Wagga Tsohuwa Zata Iya Kuwa ?

Natasha Perakov. Kwararriya wajan Tukin Jirgin yaki na Sojoji ta Zama mache ta Farko da mutu a Gumurzun da akeyi Na Rash...
28/02/2022

Natasha Perakov. Kwararriya wajan Tukin Jirgin yaki na Sojoji ta Zama mache ta Farko da mutu a Gumurzun da akeyi Na Rasha da Ukraine. Bayan tasamu Wani Mummunan Rauni Na wani Hari da Rasha ta kawo.

Wani dan Afghanistan dayayi Hijra zuwa Ukraine Lokachin da Taliban Ta Amsa mulki ya futo yache wannan Rashin sa'ane Gare...
28/02/2022

Wani dan Afghanistan dayayi Hijra zuwa Ukraine Lokachin da Taliban Ta Amsa mulki ya futo yache wannan Rashin sa'ane Gareshi

Ukraine Zata saki Fursunoninta.Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce zai saki fursunonin da ke da "kwarewar ya...
28/02/2022

Ukraine Zata saki Fursunoninta.

Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce zai saki fursunonin da ke da "kwarewar yaki" domin su taimaka wajen yaki da Rasha.

Jamhuriyar Afrika ta tsakiya ta saki dakarun wanzar da zaman lafiya na Faransa 4 bayan da Majalisar Dinkin Duniya ta kok...
28/02/2022

Jamhuriyar Afrika ta tsakiya ta saki dakarun wanzar da zaman lafiya na Faransa 4 bayan da Majalisar Dinkin Duniya ta koka

28/02/2022

Karfe 10 da rabi daga nan babban birnin Jamhuriyyar Nijar Niamey

Kim Jong-un yana goyan bayan Rasha Akan Rikichinsu da UkraineYayin da ake ci gaba da cece-kuce a duniya dangane da mamay...
27/02/2022

Kim Jong-un yana goyan bayan Rasha Akan Rikichinsu da Ukraine

Yayin da ake ci gaba da cece-kuce a duniya dangane da mamayar Ukraine, Koriya ta Arewa ta fito tana goyon bayan shugaban Ƙasar Rasha Putin.

A cikin kalamanta na farko tun bayan da Rasha ta mamaye kasar Ukraine, ma'aikatar harkokin wajen Koriya ta Arewa ta fitar da wata sanarwa da wani mai bincike ya bayyana cewa Amurka ce "tushen" rikicin kasashen Turai.

Tushen rikicin na Yukren kuma ya ta'allaka ne a kan girman kai da son kai na Amurka," in ji sakon da aka buga a shafin yanar gizon ma'aikatar harkokin wajen Arewa.

Don taimakon Ukraine Amurka ta yi alƙawarin ƙarin dala miliyan 350 a cikin taimakon soja ga Ukraine, gami da mak**an kare dangi, sulke, da ƙananan mak**ai. Jamus ta ce za ta aike da mak**ai masu linzami da na tankokin yaki zuwa kasar ta Ukraine, kuma za ta rufe Lasisin jiragen sama na Rasha.

Shugaba Vladmir Putin bai bayyana shirinsa na karshe ba, amma jami'an kasashen yammacin Turai sun yi imanin cewa ya kuduri aniyar hambarar da gwamnatin Ukraine tare da maye gurbinta da tsarin mulkin kansa, da sake zana taswirar Turai tare da farfado da tasirin Moscow a lokacin yakin cacar baka.

Ministan lafiya na Ukraine ya ba da rahoton a yau Asabar cewa mutane 198 da s**a hada da kananan yara uku ne aka kashe yayin da wasu fiye da 1,000 s**a jikkata a yakin kasa mafi girma a Turai tun bayan yakin duniya na biyu.

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya sha alwashin karfafa alakar da ke tsakaninsa da kasar Sin tare da yin barazana d...
27/02/2022

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya sha alwashin karfafa alakar da ke tsakaninsa da kasar Sin tare da yin barazana da manufofin nuna kyama daga Amurka da kawayenta.

Da yake mayar da martani, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ce, Beijing a shirye take ta yi aiki tare da kasar Koriya ta Kudu, wajen raya dangantakar abokantaka da hadin gwiwa a tsakanin jama'ar kasar Sin Dana Koriya ta Arewa

Rasha na fuskantar barazanar dakatarwa da gasar cin kofin duniyaRasha ta fuskanci kiraye-kirayen a kore ta daga gasar ci...
27/02/2022

Rasha na fuskantar barazanar dakatarwa da gasar cin kofin duniya

Rasha ta fuskanci kiraye-kirayen a kore ta daga gasar cin kofin duniya ta 2022 a ranar Lahadin, Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Faransa Noel Le Graet ne ya jagoranci bukatar janye kasar Rasha daga gasar wasan kwallon kafa.

FIFA ta yarda, duk da haka, za ta ci gaba da tattaunawa da sauran kungiyoyin wasanni don tantance ƙarin matakan "ciki har da yiwuwar cirewa daga gasa".

Sai dai a cikin 'yan mintoci da sanarwar FIFA, hukumar ta Poland ta sake jaddada cewa ba za ta kara da Rasha a gasar cin kofin duniya ba.

Ana ci gaba da gwabza fada a tashar jirgin sama a wajen KyivDakarun Rasha da na Ukraine a ranar Alhamis din nan suna faf...
24/02/2022

Ana ci gaba da gwabza fada a tashar jirgin sama a wajen Kyiv

Dakarun Rasha da na Ukraine a ranar Alhamis din nan suna fafatawa a wani sansanin sojin sama da ke wajen arewacin Kyiv bayan da wasu jiragen sama masu saukar ungulu da dama s**a yi tattaki zuwa kudu daga Belarus zuwa babban birnin kasar.

Sojojin saman Rasha sun kwace iko da filin jirgin na Gostomel, amma shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya sha alwashin cewa za a yi musu kawanya tare da murkushe su.

Zelensky ya fada a cikin wani jawabi na bidiyo cewa "An toshe jami'an tsaro na abokan gaba a Gostomel, kuma sojoji sun sami umarnin halaka su."

Tun da farko dai manema labarai na AFP sun ga jirage masu saukar ungulu suna shawagi a kasa-kasa a kan birnin daga arewa kuma babban kwamandan sojojin Ukraine Valeriy Zaluzhny ya tabbatar da cewa: "Ana fafatawa a filin jirgin na Gostomel."

Kaine Aka dauki nauyinka na wata Daya Free travel Shin wasu Kasashe kakeda Burin Ziyarta a Rayuwar Ka , Kuma Adadin kwan...
15/02/2022

Kaine Aka dauki nauyinka na wata Daya Free travel
Shin wasu Kasashe kakeda Burin Ziyarta a Rayuwar Ka , Kuma Adadin kwanaki nawa Zakayi a Kowache kasa kafun wata Dayanka Yachika ?

You got an international Passport for Free Travel in One month, which Countries you wish to visit?. And how many days you will spend in each Country?

Vous avez un passeport international pour voyager gratuitement en un mois, quels pays souhaitez-vous visiter ?. Et combien de jours passerez-vous dans chaque pays ?

🌉🌇🌁🏙️🕋⛩️🏛️🛫✈️

Karfe Goma da Rabi na dare Daga nan babban birnin jamhuriyyar Niger ( NIAMEY )
14/02/2022

Karfe Goma da Rabi na dare Daga nan babban birnin jamhuriyyar Niger ( NIAMEY )

An ji karar harbe-harbe a kusa da fadar gwamnatin Guinea-BissauKamfanin dillancin labaran reuters ya bayyana cewa, an ji...
01/02/2022

An ji karar harbe-harbe a kusa da fadar gwamnatin Guinea-Bissau

Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayyana cewa, an ji karar harbe-harbe a jiya Talata a babban birnin kasar Guinea-Bissau daura da wani gidan gwamnati, inda ake gudanar da taron majalisar ministocin kasar.

Har yanzu dai ba a bayyana ko wanene ke harbin bindigar ba.

Wata majiyar tsaro da ta samu tuntuba a cikin ginin ta ce harbe-harbe ne ya rutsa da mutane. Wata majiya ta biyu ta ce mutane biyu sun mutu, amma babu tabbas ko jami’an tsaro ne ko kuma wadanda s**a kaddamar da harin.

Rikicin siyasa ya addabi kasar shekaru da dama. Juyin mulki tara ko yunkurin juyin mulki tun bayan samun ‘yancin kai daga kasar Portugal a shekarar 1974 sun kawo cikas ga kokarin da ake na jawo tattalin arzikin kasar ya wuce yadda ya dogara da fitar da goro.

Niamey Online ✍️.

OfficialSojojin Burkina Faso sun hambarar da shugaban kasar a wani juyin mulki na baya bayan nan da aka yi a yammacin Af...
24/01/2022

Official

Sojojin Burkina Faso sun hambarar da shugaban kasar a wani juyin mulki na baya bayan nan da aka yi a yammacin Afirka.

A ranar 24 ga wata, sojojin kasar Burkina Faso sun bayyana cewa sun hambarar da shugaba Roch Kabore daga kan karagar mulki, da dakatar da kundin tsarin mulkin kasar, da rusa gwamnati da majalisar dokokin kasar tare da rufe iyakokin kasar.

Sojoji sun hambarar da gwamnatoci a cikin watanni 18 da s**a gabata a Mali da Guinea. Sojoji sun kuma karbi ragamar mulki a kasar Chadi a shekarar da ta gabata bayan da shugaba Idriss Deby ya mutu a fada da 'yan tawaye a fagen daga a arewacin kasar

Niamey Online ✍️.

Mali ta hana jirgin sojin Jamus shiga  kasartaGwamnatin mulkin soja a Mali ta ki barin wani jirgin saman sojan Jamus da ...
20/01/2022

Mali ta hana jirgin sojin Jamus shiga kasarta

Gwamnatin mulkin soja a Mali ta ki barin wani jirgin saman sojan Jamus da ke jigilar kaya ya yi shawagi a cikin kasarta.

Ma'aikatar harkokin wajen Jamus ta ce an hana zirga-zirgar jiragen MINUSMA da dama tun ranar Alhamis din da ta gabata. Majalisar Dinkin Duniya a ranar Talata ta kuma ce kasar Mali ta fara toshe jiragen da dama na Kasashen Turawa.

Shugabar kwamitin tsaro na majalisar dokokin Jamus Bundestag, ta ce kin ba da izini ba za a fahimce shi ba, don haka akwai bukatar gwamnatin mulkin soja ta yi bayani.

Gwamnatin mulkin soji wacce ta karbi mulki a juyin mulki a shekarar 2020, ta rufe iyakokin kasashen yammacin Afirka da ke makwabtaka da ita. Tuni dai kungiyar ECOWAS ta rufe iyakokinta da kasar Mali a wani bangare na takunkumin diflomasiyya da na tattalin arziki bayan da gwamnatin mulkin sojan kasar ta ki amincewa da gudanar da zaben da aka yi alkawarin yi a watan gobe .

Kungiyar Tarayyar Turai ta sanar da kakaba takunkumin da kungiyar ECOWAS ta dauka.

Niamey Online ✍️.

Faransa za ta kawo karshen tallafin soji da take baiwa Mali yayin da alakar da ke tsakaninta da gwamnatin mulkin soji ke...
20/01/2022

Faransa za ta kawo karshen tallafin soji da take baiwa Mali yayin da alakar da ke tsakaninta da gwamnatin mulkin soji ke kara tabarbarewa

Yayin da dangantaka tsakanin Faransa da Mali ke yin tsami cikin sauri, birnin Paris na tunanin ko lokaci ya yi da za a daina ba da tallafin soji ga kasar da ke karkashin mulkin soja da ta bijirewa tsare tsarensu

Niamey Online ✍️.

Fatan Alheri
17/01/2022

Fatan Alheri

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci gwamnatin  ta Mali da ta gabatar da jadawalin zabeMajalisar Dinkin Duniya ta yi kira a...
13/01/2022

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci gwamnatin ta Mali da ta gabatar da jadawalin zabe

Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira a yau Alhamis ga mahukuntan kasar Mali da su sanar da jadawalin gudanar da zabe a daidai lokacin da s**a fusata kan shawarar da ta bayar na ci gaba da mulki na tsawon shekaru biyar kafin gudanar da zabe.

Matakin dai ya biyo bayan shawarar da gwamnatin rikon kwaryar kasar ta Mali ta ba da shawarar ci gaba da mulki har na tsawon shekaru biyar kafin gudanar da zabe, inda ta bijirewa bukatun kasashen duniya na cewa ta mutunta alkawarin gudanar da zabe a ranar 27 ga watan Fabrairu.

Niamey Online ✍️.

Rasha da China sun hana kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya goyon bayan sabon takunkumin da aka kakaba wa MaliA ra...
12/01/2022

Rasha da China sun hana kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya goyon bayan sabon takunkumin da aka kakaba wa Mali

A ranar Talata ne kasashen Rasha da China s**a hana kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya goyon bayan sabon takunkumin da aka kakabawa kasar Mali, saboda matakin da shugabannin sojin kasar s**a dauka na jinkirta zaben watan gobe har zuwa shekara ta 2026, lamarin da ke zama wani rauni ga maido da tsarin dimokuradiyya a kasar da ke yammacin Afirka

Jakadan Majalisar Dinkin Duniya na kasar Mali Issa Konfourou ya shaidawa kwamitin tsaro cewa babu sojojin haya a kasar ta Mali. Ya ce masu horas da 'yan wasa na Rasha suna kasar Mali don ba da shawara da horas da sojojinta kan amfani da kayan aikin soja da gwamnati ta samu daga Rasha.

Jakadan kasar Faransa Nicolas De Riviere ya sake nanata yin Allah wadai da matakin da kasarsa ta Mali ta dauka

Niamey Online ✍️.

Farashin Kudin da Kungiyoyin kwallon Kafar Africa Na Kasashe  Zasu samu Niamey Online ✍️.
11/01/2022

Farashin Kudin da Kungiyoyin kwallon Kafar Africa Na Kasashe Zasu samu

Niamey Online ✍️.

Adresse

Niamey
Niamey
8000

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Niamey Online publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Contacter L'entreprise

Envoyer un message à Niamey Online:

Vidéos

Partager