TRT Afrika Hausa

TRT Afrika Hausa Afirka tsantsarta

Hukumar ƙididdiga ta Ghana ce ta tabbatar da raguwar inda ta ce an samu raguwar ne a watan Janairun 2025 idan aka kwatan...
04/02/2025

Hukumar ƙididdiga ta Ghana ce ta tabbatar da raguwar inda ta ce an samu raguwar ne a watan Janairun 2025 idan aka kwatanta da watan Disamban 2024.

Hukumar ƙididdiga ta Ghana ce ta tabbatar da raguwar inda ta ce an samu raguwar ne a watan Janairu 2025 idan aka kwatanta da watan Disamban 2024.

'Yan tawayen sun jaddada buƙatarsu ta karewa da kuma kiyaye fararen-hula a duk inda suke.
04/02/2025

'Yan tawayen sun jaddada buƙatarsu ta karewa da kuma kiyaye fararen-hula a duk inda suke.

Manchester City ce ta fi kowace ƙungiya kashe kuɗi wajen sayen ’yan wasa inda ƙungiyar ta kashe fan miliyan 180, wato ha...
04/02/2025

Manchester City ce ta fi kowace ƙungiya kashe kuɗi wajen sayen ’yan wasa inda ƙungiyar ta kashe fan miliyan 180, wato hakan yana nufin abin da ta kashe ya fi jimullar abin da duka sauran ƙungiyoyin Gasar Premier 19 s**a kashe waɗanda s**a kashe fan miliyan 177.
Shin kuna ganin cefanen da City ta yi zai sa ta farfaɗo har ta iya cin Gasar Premier?

03/02/2025

Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta fara ɗaukar matakin tabbatar da cewa duka motocin da ke faɗin kasar an yi musu inshora don tabbatar da kiyaye hadura da kuma kare hakkin waɗanda haɗari ya rutsa da su, a cewar rundunar.

Dokar masana'antar mai ta Nijeriya, ta umurci masu samar da mai da s**a hada da kamfanonin mai na kasa da kasa da su sad...
03/02/2025

Dokar masana'antar mai ta Nijeriya, ta umurci masu samar da mai da s**a hada da kamfanonin mai na kasa da kasa da su sadaukar da wani takamaiman adadin danyen mai ga matatun cikin gida kafin a fitar da shi zuwa kasashen waje, wata bukata da ake kira wajibcin samar da danyen mai a cikin gida.

Hukumar kula da albarkatun man fetur ta Nijeriya ta ce za ta hana izinin fitar da man fetur ga masu samar da man da s**a kasa cika ka’idojin da aka gindaya musu na samar da man ga matatun mai na cikin gida.

Kocin Arsenal Mikel Arteta ya jinjina wa ’yan wasan ƙungiyar bayan da s**a doke Manchester City da ci 5-1 a filin wasa n...
03/02/2025

Kocin Arsenal Mikel Arteta ya jinjina wa ’yan wasan ƙungiyar bayan da s**a doke Manchester City da ci 5-1 a filin wasa na Emirate a ranar Lahadi.
Da wannan sakamakon wasan yanzu Arsenal tana matsayi na biyu a teburin Gasar Premier da maki 50 yayin da Liverpool take saman teburin da maki 56.
Shin kuna ganin Arsenal za ta iya ɗaukar kofin gasar a bana?

‘Yan bindiga ne ke iko da kimanin kashi 80 cikin 100 na birnin Port-au-Prince, kuma tashin hankalin na ci gaba da ƙaruwa...
03/02/2025

‘Yan bindiga ne ke iko da kimanin kashi 80 cikin 100 na birnin Port-au-Prince, kuma tashin hankalin na ci gaba da ƙaruwa, inda aka kashe fiye da mutum 5,000 a hare-haren da s**a shafi ‘yan daba a shekarar 2024 kawai.

‘Yan bindiga ne ke iko da kimanin kashi 80 cikin 100 na birnin Port-au-Prince, kuma tashin hankalin na ci gaba da ƙaruwa, inda aka kashe sama da mutum 5,000 a hare-haren da s**a shafi ‘yan daba a shekarar 2024 kawai.

Kazalika kamfanin dillancin labaran Nijar ya ambato Ministan Sufuri da Kayayyakin Aiki na ƙasar Kanal-Manjo Salissou Mah...
03/02/2025

Kazalika kamfanin dillancin labaran Nijar ya ambato Ministan Sufuri da Kayayyakin Aiki na ƙasar Kanal-Manjo Salissou Mahaman Salissou yana cewa an riga an kafa kwamiti domin gaggauta bayar da takardun da ake buƙata wajen samar da waɗannan kamfanonin.

Kamfanin dillancin labaran Nijar, ANP, ya ambato Ministan Sufurin Nijar yana mai bayyana hakan a lokacin da yake bayani kan ma’aikatarsa a birnin Yamai.

Ɗan wasan gaban Manchester United Marcus Rashford ya kammala komawa Aston Villa a matsayin aro.Rashford mai shekara 27 y...
03/02/2025

Ɗan wasan gaban Manchester United Marcus Rashford ya kammala komawa Aston Villa a matsayin aro.
Rashford mai shekara 27 ya ƙulla yarejejeniya Aston Villa har zuwa ƙarshen kakar nan, inda yake da zaɓin komawa can na dindindin a kan fan miliyan 40.
Ƙarkashin Koci Ruben Amorim, Rashford ya shafe fiye da makonni shida bai buga wa United wasa ba.

Kamal Abu al Rub, gwamnan Jenin da ke Gaɓar Yammacin Kogin Jordan, ya ce hukumomin Isra'ila suna aiki tuƙuru domin ruguz...
03/02/2025

Kamal Abu al Rub, gwamnan Jenin da ke Gaɓar Yammacin Kogin Jordan, ya ce hukumomin Isra'ila suna aiki tuƙuru domin ruguza sansanin 'yan gudun hijira na Jenin ta yadda ba za a iya sake zama a gidaje da sauran matsugunan da ke cikinsa ba

Yarjejeniyar tsagaita wuta da musayar fursunoni tsakanin Isra'ila da yankin Gaza ta shiga kwana na 16 — bayan dakarun Isra'ila sun kashe Falasɗinawa fiye da 47,498. Kazalika Netanyahu ya tafi Amurka domin tattaunawa da Trump.

Yahudawa ‘yan kama-wuri-zauna sun kai hare-hare fiye da 2,970 a shekarar 2024 a kan Falasɗinawa da dukiyoyinsu a Gaɓar Y...
02/02/2025

Yahudawa ‘yan kama-wuri-zauna sun kai hare-hare fiye da 2,970 a shekarar 2024 a kan Falasɗinawa da dukiyoyinsu a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da Isra’ila ta mamaye.

02/02/2025

Fitaccen ɗan wasan Kannywood Yakubu Muhammad ya yi ƙarin bayani dangane da irin rawar da yake takawa a cikin wasu fina-finai masu dogon zango da yake ciki waɗanda s**a haɗa da Garwashi da Labarina da Gidan Sarauta.

Matatar ta Dangote ta ce kasuwa ce ta yi halinta shi ya sa aka samu wannan ragin inda ta ce a 'yan kwanakin nan farashin...
02/02/2025

Matatar ta Dangote ta ce kasuwa ce ta yi halinta shi ya sa aka samu wannan ragin inda ta ce a 'yan kwanakin nan farashin ɗanyen mai ya karye a kasuwannin duniya.

01/02/2025

Yanayin siyasa ya fara ɗaukar ɗumi a Nijeriya inda a cikin ‘yan kwanakin nan tsohon gwamnan Kaduna Nasiru El-Rufai ya soki gwamnatin Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC kan yanayin yadda al’amura ke tafiya a ƙasar.

Rahotanni sun ce dakarun RSF na Sudan ne s**a yi ɓarin wuta a wata kasuwa da ake sayar da kayan lambu a birnin na Omdurm...
01/02/2025

Rahotanni sun ce dakarun RSF na Sudan ne s**a yi ɓarin wuta a wata kasuwa da ake sayar da kayan lambu a birnin na Omdurman, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum 40, wasu da dama s**a jikkata.

Address

Ahmet Adnan Saygun Cd
Istanbul
34347

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TRT Afrika Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share