Daily True Hausa

Daily True Hausa Daily True Hausa (DTH Africa) kafar yada labarai ce ta Intanet.
(1)

Muna buga labaran da s**a shafi cin hanci da rashawa, shahararrun mutane, take hakkin dan adam, da al'amuran yau da kullum, musamman a Afirka.

Gwamnatin jihar Kano ta ware naira biliyan 2.5 domin gudanar da bukukuwan auren zawarawa a fadin kananan hukumominta 44 ...
01/02/2025

Gwamnatin jihar Kano ta ware naira biliyan 2.5 domin gudanar da bukukuwan auren zawarawa a fadin kananan hukumominta 44 a shekarar 2025.

31/01/2025
Quran Abuja: Malekyari ne ya tara jama’a (malamai) – Sheikh Jalo Jalingo ya tabbatar da ikirarin Dan Bello
31/01/2025

Quran Abuja: Malekyari ne ya tara jama’a (malamai) – Sheikh Jalo Jalingo ya tabbatar da ikirarin Dan Bello

An dakatar da Bin Uthman a matsayin limamin masallacin SahanaHukumar SSS, a cewar majiyoyi, ta gargadi Sheikh bin Uthman...
31/01/2025

An dakatar da Bin Uthman a matsayin limamin masallacin Sahana

Hukumar SSS, a cewar majiyoyi, ta gargadi Sheikh bin Uthman kan tunzurawa, wa'azin da ka iya haifar da rikici ko hari a cikin masallacin.

Ba zamu gushe ba wajen yin kira ga kungiyar Izala da su tuba, su koma ga Allah - Sheikh Idris Bauchi
30/01/2025

Ba zamu gushe ba wajen yin kira ga kungiyar Izala da su tuba, su koma ga Allah - Sheikh Idris Bauchi

Jiga-jigan jam’iyyar sun fara yunkurin maye gurbin Abdullahi Abbas "Kada Allah Ya Kiyaye", wa'adinsa ya kusa karewa daga...
30/01/2025

Jiga-jigan jam’iyyar sun fara yunkurin maye gurbin Abdullahi Abbas "Kada Allah Ya Kiyaye", wa'adinsa ya kusa karewa daga shugabancin jam’iyyar APC na jihar Kano

Sowore Ga Shugaban 'Yan sandan Najeriya: 'Zaka iya karbar fasfo na, amma ba za ka iya sani yin shiru ba'
30/01/2025

Sowore Ga Shugaban 'Yan sandan Najeriya: 'Zaka iya karbar fasfo na, amma ba za ka iya sani yin shiru ba'

Taron Qur'anic/Abuja: Bayan Kasancewar Sa Bidi'a Ga Kuma Almubazzaranci - Inji Sheikh Gumi
30/01/2025

Taron Qur'anic/Abuja: Bayan Kasancewar Sa Bidi'a Ga Kuma Almubazzaranci - Inji Sheikh Gumi

29/01/2025

Yaya ake gane mutanen jihar Kaduna?

“Duk lokacin da aka ambaci manyan mutane a Najeriya, ana nufin ‘yan siyasa ne” – Inji Sheikh Kabiru Gombe, daya daga cik...
29/01/2025

“Duk lokacin da aka ambaci manyan mutane a Najeriya, ana nufin ‘yan siyasa ne” – Inji Sheikh Kabiru Gombe, daya daga cikin jagororin taron Al-Qur’ani/Abuja, wanda rahotanni ke nuni da cewa gwamnatin Tinubu ta shirya domin nunawa kasashen yamma cewa suna da goyon baya a Arewa a zaben 2027

Kudurin kafa sabuwar rundunar jami’an tsaro a kananan hukumomi 44 na jihar Kano ya tsallake karatu na biyu a gaban majal...
28/01/2025

Kudurin kafa sabuwar rundunar jami’an tsaro a kananan hukumomi 44 na jihar Kano ya tsallake karatu na biyu a gaban majalisa.

Gwamnatin NNPP a Jihar Kano za ta samar da jami’an tsaro nata, wanda majalisar za ta ba da izinin daukar makamai domin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar.

DA DUMI-DUMI: Jihar Kano za ta samar da jami’an tsaro nata, wanda majalisar za ta ba da izinin daukar makamai domin kare...
28/01/2025

DA DUMI-DUMI: Jihar Kano za ta samar da jami’an tsaro nata, wanda majalisar za ta ba da izinin daukar makamai domin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano

Me zaku ce ?

27/01/2025

Kalaman da 'yan Najeriya ke yi wa Sheikh Kabiru Gombe kan taron Al-Qur'ani/Abuja. Ba dadi ji.

Yadda Sanata Barau Ya Rabawa Rudunar ‘Yan Sandan Kano Babura 1,000, Zargin Jeafa Kano Cikin RikiciShahararren ɗan jarida...
27/01/2025

Yadda Sanata Barau Ya Rabawa Rudunar ‘Yan Sandan Kano Babura 1,000, Zargin Jeafa Kano Cikin Rikici

Shahararren ɗan jaridar nan, kuma mamallakin jaridar DAILY NIGERIAN, Jaafar Jaafar ya zargi Mataimakin Shugaban Malissar Dattawa, Sanata Barau Jibrin da hannu cikin fitintinu masu nasaba da siyasa da ke faruwa a Jihar Kano.

Jaafar Jaafar ya baiyana hakan ne a cikin shirin "Fashin Baƙi" da su ke gabatarwa a duk ranar Lahadi tare da Lauya, Abdu Bulama Bukarti, Lauya Abba Hikima , Dan jarida Nasiru Zango da kuma Naziru Mika'il.

A cewar Jaafar "Mutane da yawa su na tunanin Ganduje ne, Wallahi Barau ya fi hannu a wannan masifar. Su na shirya gidoga ne su faɗa wa shugaban ƙasa cewa mutane sun dawo daga rakiyar gwamnati mai ci a Jihar Kano ba sa son ta idan ta yi taro aka gani da jama’a da yawa ya soke wannan zargi.

"Kusan duk wannan abubuwan da ake ƙullawa Wallahi da hannunsu. Ko ɗansanda za a kawo Kano sai wanda suke so wanda zai kare muradunsu.

"Irin wannan bai kamata ba. Ko takarar gwamna mutum zai yi, bai kamata ya kasaara al'umma ba. Irin wannan bai dace ba, ba kuma kishin jiha da al'umma ba ne," in ji Jaafar Jaafarya.

A watan nuwambar shekarar 2024, sanata Barau ya rabawa Jami’an tsaro babura, yatın da ake tsaka da takun saka da Gwamnan Kano wanda har ta kai ga yayi ikirarin “Da ‘yan sanda kadai nake da matsala, basa bin umarni na”

A cewar Barau, Domin inganta aikin ‘yan sanda a fadin kananan hukumomi 44 na jihar Kano, na kai babura 1,000 ga rundunar ‘yan sandan jihar Kano a yau.

An gudanar da bikin mika ragamar hukumar ne a hedikwatar 'yan sanda ta Bompai, kuma an gudanar da bukukuwan murna a tsakanin jami'ai da jami'an rundunar 'yan sandan Najeriya NPF.

A jawabina, na yabawa hafsoshi da jami’an rundunar bisa namijin kokarin da suke yi na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a jiharmu.

Tsaro ba alhaki ne kawai na gwamnati, ’yan sanda, ko wasu hukumomin tsaro ba; nauyi ne na gamayya. Kowa yana da rawar da zai taka—ciki har da masu hannu da shuni, sarakunan gargajiya, malaman addini, ɗalibai, har ma da talakawan ƙasa.

Don haka ya zama wajibi mu hada kai domin tallafa wa maza da mata masu kishinmu a cikin rundunar ‘yan sandan Nijeriya, musamman na rundunar ta Kano. Sun cancanci taimakonmu ta kowace hanya mai yiwuwa, ta hanyar samar da bayanai ko kayan aiki don taimakawa ayyukansu.

Baburan dai za su baiwa ‘yan sanda damar isa ga dukkan yankunan jihar yadda ya kamata domin yaki da miyagun ayyuka.

Masu laifi, a yi gargaɗi: lokaci ya yi da za ku dakatar da ayyukanku na banƙyama kuma ku rungumi zaman lafiya. Idan ba haka ba, rundunar ‘yan sandan Najeriya a Kano ta shirya tsaf domin daukar mataki. Za su kasance a ƙofar ku.

Barau ne yake assasa duk wata fitina a Jihar Kano ~ Ja’afar Ja’afar
27/01/2025

Barau ne yake assasa duk wata fitina a Jihar Kano ~ Ja’afar Ja’afar

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje CON ya karbi sama da mutane dubu arba’in daga jam’iyyun ada...
26/01/2025

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje CON ya karbi sama da mutane dubu arba’in daga jam’iyyun adawa da s**a hada da PDP da NNPP a jihar Katsina zuwa APC - Kwamared Muhammad Garba

Gwamnatin Uba Sani Bata Biyan Malaman Makarantun Firamare na Kaduna Sabon Mafi Karancin Albashi N70,000Malaman makarantu...
26/01/2025

Gwamnatin Uba Sani Bata Biyan Malaman Makarantun Firamare na Kaduna Sabon Mafi Karancin Albashi N70,000

Malaman makarantun firamare a jihar Kaduna sun nuna damuwarsu kan matsanancin halin kuncin da ake ciki sakamakon rashin aiwatar da sabon mafi karancin albashi na kasa a jihar.

A wata budaddiyar wasika da s**a aike wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu mai kwanan wata ranar Alhamis, 23 ga watan Janairu, 2025, kuma aka bai wa manema labarai a Kaduna, malaman sun koka da yadda aka cire su daga umarnin gwamnatin tarayya na kara mafi karancin albashi zuwa N70,000.

Wasikar mai dauke da sa hannun “Concerned Primary Schools of Kaduna State” don kaucewa cin zarafin da ake yi mata, ta bayyana irin kalubalen da malaman ke fuskanta na rashin biyan albashi.

Malaman sun jaddada muhimmiyar rawar da ilimin firamare ke takawa wajen ci gaban Najeriya tare da gargadin cewa rashin kula da jin dadinsu na yin illa ga ingancin ilimin da ake bai wa yara a jihar.

Sun bukaci shugaba Tinubu da ya shiga tsakani tare da tilastawa gwamnatin jihar Kaduna aiwatar da sabon tsarin albashi, tare da jaddada bukatar inganta albashin ma’aikata, da kuma bin diddigin ma’aikatan kananan hukumomin da ke da alhakin biyan albashi.

Yadda Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi ke fassara zuwa Hausa ga Mai Girma Aminu Ado Bayero abinda Sheikh Mahi ke cewa ...
25/01/2025

Yadda Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi ke fassara zuwa Hausa ga Mai Girma Aminu Ado Bayero abinda Sheikh Mahi ke cewa da Larabci

Adresse

Dakar

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Daily True Hausa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Vidéos

Partager