Potiskum Online News

Potiskum Online News Sashen Labarai.

Masu Yaɗa Ƙarya Akan Gwamnan Bauchi Ba Za Ku Yi Nasara Ba!Muna jan hankalin jama’a game da wani labari na ƙarya da ake y...
07/01/2026

Masu Yaɗa Ƙarya Akan Gwamnan Bauchi Ba Za Ku Yi Nasara Ba!

Muna jan hankalin jama’a game da wani labari na ƙarya da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta, wanda ake zargin cewa an bai wa wata ƙungiya da ake alaƙantawa da ta’addanci kuɗi daga Gwamnatin Jihar Bauchi. Wannan labari ba shi da tushe, b***e Malama, babu hujja, kuma ƙarya ce tsagwaronta.

Babu wani lokaci da Gwamnatin Jihar Bauchi, ko Mai Girma Gwamna Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya amince ko ya ba da umarnin bai wa kowace ƙungiya da ke da alaƙa da ta’addanci kuɗi, ko ta kowace hanya. Wannan zargi an ƙirƙire shi ne kawai domin ɓata suna, yaudarar jama’a, da tayar da fitina.

Muna kira ga jama’a da su yi watsi da irin waɗannan labaran ƙarya, su kuma guji yaɗa bayanan da ba su tantance ba. Gwamnatin Jihar Bauchi ta himmatu wajen tabbatar da tsaro, zaman lafiya, da bin doka da oda, tare da haɗin gwiwa da hukumomin tsaro na ƙasa.

Duk wanda ke yaɗa wannan labari na ƙarya, yana da niyyar ɓata sunan shugabanci da ya samu amanar jama’a, kuma hakan ba zai hana gwamnati ci gaba da ayyukan alheri da ci gaban jihar Bauchi ba.

Gaskiya ce za ta yi nasara a kowane lokaci.

Kungiyar Arewa Media Writers Ta Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Da Ya Gaggauta Sauke Ministan Abuja, Nyesom Wike…Kungiyar ta c...
05/01/2026

Kungiyar Arewa Media Writers Ta Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Da Ya Gaggauta Sauke Ministan Abuja, Nyesom Wike

…Kungiyar ta ce dole ne a dakatar da duk wani yunkuri da ke barazana ga dimokaradiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Daga Kungiyar “Arewa Media Writers”

Kungiyar Marubutan Arewa "Arewa Media Writers" ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Comr. Haidar H. Hasheem (Kano), ta nuna matuƙar damuwa tare da yin Allah-wadai da abin da ta bayyana a matsayin k**a-karya, nuna wariya da cin zarafin ‘yan ƙasa, da ake zargin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, na aikatawa.

Kungiyar ta ce abin takaici ne yadda ake zargin Ministan da amfani da ƙarfin iko wajen cuzgunawa ‘yan Arewa da ‘yan adawa, musamman saboda banbancin ra’ayin siyasa, abin da hakan ke tauye ‘yancin ‘yan ƙasa tare da zama barazana ga tsarin dimokaradiyyar Najeriya.

A cewar ƙungiyar, ana zargin Wike da amfani da hukumar EFCC da jami’an tsaro wajen tsoratarwa da musgunawa abokan hamayya, lamarin da ke haifar da fargaba, rashin adalci da rashin amincewa ga hukumomin gwamnati.

Kungiyar Arewa Media Writers ta kuma nuna damuwa kan yadda Ministan ke yin furuci da ayyuka masu ɗauke da wariya ga al'ummar Hausawa/Fulani, inda ta jaddada zargin da Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya yi a baya-bayan nan, wanda yace ya samu wata masaniya daga mai jiya mai tushe dake nuna cewa hatta hukumomin EFCC, Wike ke amfani da su wajen matsin lamba ga yan adawa, haka kuma ya tabbatar dasa hannun Ministan wajen ƙoƙarin bata masa suna ta hanyar jingina shi da zargin ɗaukar nauyin ta’addanci a kotu.

Kungiyar ta bayyana cewa irin waɗannan zarge-zarge ba komai ba ne illa kiyayya ta kabilanci da siyasar adawa, wanda hakan ya saba wa ruhin haɗin kan ƙasa. Idan baku manta ba tun a lokacin da Wike ke Gwamnan Jihar Rivers, an samu rahotannin rusa masallatai, rufe shaguna da gidajen ‘yan Arewa, tare da korar su daga jihar, abin da har yanzu ke ci wa zukatan al’umma tuwo a ƙwarya.

Haka kuma ƙungiyar ta yi tsokaci kan sauke Sakataren Ilimi na Abuja, Dr. Danlami, wanda ɗan Arewa ne, inda ta ce yadda aka yi hakan ya ƙara nuna amfani da iko ba bisa ƙa’ida ba, tare da mayar da shi aiki bisa wasu sharudda.

Ba wannan kaɗai ba, kungiyar ta kuma nuna damuwa kan zargin amfani da jami’an tsaro wajen tarwatsa rikici a helkwatar jam’iyyar PDP, inda aka ce har aka yi amfani da hayaki mai sa hawaye ga wasu gwamnoni ciki har da Seyi Makinde da Bala Muhammad, lamarin da bai dace ba ga shugabanni da kundin tsarin mulki ya tanadar musu da rigar kariya.

Kungiyar Arewa Media Writers ta jaddada cewa tsarin shugabancin Najeriya bai ginu kan kabilanci, wariya ko ramuwar siyasa ba, illa adalci, daidaito da mutunta ‘yancin kowa.

A ƙarshe, Kungiyar Arewa Media Writers tana kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta dakatar da duk wani yunkuri da ke barazana ga dimokaradiyya Najeriya, taka wa Ministan Abuja burki, ko kuma a sauke shi daga mukaminsa, domin kare martabar dimokaradiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Arewa Media Writers za ta ci gaba da tsayawa kan gaskiya, adalci da kare haƙƙin al’umma.

✍️✍️
Comr Nura Siniya
Chairman Arewa Media Writer's Katsina Chapter

GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKEMaigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senator Bala Abdulk...
02/01/2026

GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKE

Maigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Daular Usmaniyyah) ya fallasa asiri na makircin da Ministan Abuja Nyesom Wike yake kulla masa da jihar Bauchi gaba daya

Maigirma Gwamna yayi wannan fallasa ne a cikin shirin Sunrise Daily na Channels TV dazu da safe, yace akwai wanda yake shirya min makirci, kuma na san shi, shine Ministan Abuja na yanzu Nyesom Wike, ya fada wa duniya cewa zai kunna wuta a jihata na Bauchi

Kauran Daular Usmaniyyah yaci gaba da cewa; na fahimci Wike ne yake bada umarni wa hukuma irin na EFCC wajen batani, yana bawa mutane cin hanci, yana sayar da filayen Abuja yana amfani dasu wajen cimma burinsa, ba sabon abu bane a gareni saboda na taba rike mukamin Ministan Abuja na shekaru 6 na san komai

Gwamnan Bauchi yaci gaba da cewa; yana da hujjoji daga majiyarsa na sirri dake EFCC wanda s**a tabbatar masa da cewa Wike ne yake tsara duk abinda yake faruwa da ‘yan adawar siyasa a Nigeria

Kaura yace tsohon Accountant General dinsa na jihar Bauchi yaci amanata, ni na kaishi Kotu da kaina domin a masa hukunci, daga bisani Kotu ta bada belinsa, to a yanzu Wike ne yake aiki dashi a Kotu wajen bada shaida na karya akan mukarrabaina da aka k**a

A matsayina na Gwamna wanda na rike manyan muk**ai tun daga Sanata har Minista, ina shugaban al'ummah ta ya zai kasance ina daukar nauyin ta'addanci, ana min wannan sharri ne saboda ina cikin manyan 'yan adawa

Zan bi duk matakan da s**a dace domin na kare kaina, na rubuta wa Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya takardan korafi, tare da sanar da hukumomin tsaro, kuma zan kai korafina zuwa ga hukumonin Majalisar dinkin duniya, inji Maigirma Gwamna

Sannan Gwamna Bala yace Shugaban Kasa Tinubu yana kewaye da 'yan daba, 'yan damfara wadanda suke son ha||akashi a siyasance irinsu Wike

Muna rokon Allah Ya kare jihar Bauchi daga wadanda suke neman jingina mana ta'addanci, Allah Ya sa mugun nufinsu ya kare a kansu da iyalansu kadai.

Ƙungiyar “Kano Youth For Good Governance” Ta Caccaki Sanata Rufa’i Hanga Bisa Gazawa, Raini Da Butulci A Kano Ta Tsakiya...
31/12/2025

Ƙungiyar “Kano Youth For Good Governance” Ta Caccaki Sanata Rufa’i Hanga Bisa Gazawa, Raini Da Butulci A Kano Ta Tsakiya

Ƙungiyar Kano Youth For Good Governance ƙarƙashin jagorancin Comr. Nura Sale na zargin Sanata Rufa’i Hanga da zama Sanata mafi gazawa a tarihin Kano ta Tsakiya.

Sanata wanda ya kasa kawo ko aiki ɗaya da al’umma za su nuna su ce “ga abin da ya mana”, sai dai zama a Abuja yana cin moriyar mukami tare da iyalinsa, alhali jama’ar Kano ta tsakiya na fama da talauci da rashin kulawa.

Mutumin da ya sanyawa karen gidansa sunan “Kwankwaso” akwai butulcin da ya wuce wannan, ba soyayya bane, cin mutunci ne kai tsaye ga tafiya da kuma abinda al’ummar Kano ke girmamawa, kuma hakan ya nuna a sarari cewa Sanatan ba shi da kishin jama’a ko dabi’ar girmamawa ga Kwankwaso.

Butulcin Sanata Rufa’i Hanga ya kai matakin da ya kasa taimakawa iyalan marigayi Alh. Yawale, mutumin da ya yi masa riga da wando, ya tsaya masa a lokacin bukata. Wannan hali na nuna cewa Sanatan ba ya tuna alheri, kuma bai cancanci amanar jama’a ba.

Abin mamaki shi ne yadda Sanatan ke fitowa yana zargin wasu da butulci da cin amana, har sanata ne yake da bakin cin mutuncin manyan Jihar Kano, alhali shi ne cikakken misalin abin da yake zargi na cin amana da rashin amfani.

Kano Youth For Good Governance na jaddada cewa tarihin Sanata Rufa’i Hanga ba tarihin aiki ba ne, tarihin gazawa ne, raini da cin amana irin ta siyasa.

✍️
Kano Youth For Good Governance
Comr. Nura Sale
Shugaban Kungiyar

19/12/2025
Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga bara...
16/12/2025

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle
....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga barazana ce ga tsaron Najeriya.

Ƙungiyar Odua People’s Assembly (OPA) ta nuna damuwa matuƙa kan zargin da ake yi wa Ministan Tsaron Ƙasa (State), Bello Matawalle, dangane da alaƙa da ‘yan bindiga. Ƙungiyar ta ce zargin yana da hatsari ga tsaron ƙasa da amincewar jama’a.

OPA ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gudanar da bincike mai zaman kansa, tare da sanya gaskiya kuma ba tare da son kai ba, domin fayyace gaskiyar lamarin. Ta ce rashin daukar mataki zai ƙara raunana amincewar jama’a da hukumomin gwamnati, musamman a lokacin da Najeriya ke fama da matsanancin matsalar tsaro.

Ƙungiyar ta ce bayyanar wani bidiyo da ke nuna Bello Turji, shugaban ‘yan bindiga, yana kare Matawalle abin tayar da hankali ne, domin yana nuna yiyuwar haɗin kai tsakanin jami’an gwamnati da masu laifi.

OPA ta bayyana cewa duk wata alaƙa, kai tsaye ko a kaikaice, tsakanin jami’an gwamnati da ‘yan bindiga cin amanar ‘yan Najeriya ne, musamman waɗanda s**a sha wahala sak**akon rashin tsaro.

A matsayin mataki na dawo da amincewar jama’a, OPA ta buƙaci a sauke Matawalle daga muƙaminsa nan take, tare da kafa cikakken tsari na bincike mai zaman kansa. Ta kuma gargadi cewa rashin daukar mataki mai tsauri zai ƙarfafa ‘yan bindiga tare da ƙara ta’azzara rashin tsaro.

Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Najeriya su kasance masu faɗakarwa, su kuma riƙa kira ga alhakin shugabanni, tana jaddada cewa yaƙi da ‘yan bindiga ya zama na bai ɗaya, ba tare da la’akari da siyasa ko yanki ba.

Sa Hannun
Sunday Daniel
Mai magana da yawun Odua People’s Assembly

Yak**ata Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Na Gaggawa Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga Da Musa Kamarawa Yayi Ga ...
15/12/2025

Yak**ata Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Na Gaggawa Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga Da Musa Kamarawa Yayi Ga Bello Matawalle
.... Dole a gaggauta binciken Musa Kamarawa da kuma Ƙaramin Ministan Tsaron kan alaƙa da yan bindiga domin tabbatar da tsaron al'ummar Arewacin Najeriya.

Ni, Comr. Haidar H. Hasheem, ɗan Arewa kuma mai kishin zaman lafiya da tsaron ƙasa, ina bayyana damuwa mai tsanani kan manyan zarge-zargen da ke yawo a fili, musamman ikirarin da tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Gwamnan Zamfara, Musa Kamarawa, ya yi a faifan bidiyo dangane da Ministan Tsaron Ƙasa na yanzu, Bello Matawalle.

Waɗannan zarge-zarge sun haɗa da alaƙa da ’yan bindiga, zargin tura kuɗaɗe ga fitaccen shugaban ’yan bindiga Bello Turji, sayen motocin Hilux ga yan ta'adda, da kuma tallafawa da dukiya k**ar gidaje, saya musu dusa da sauran kayan more rayuwa, tare da zargin cewa wasu ’yan siyasa daga Zamfara da maƙwabtanta sun taka rawa a hakan.

Waɗannan ba ƙananan maganganu ba ne. Zarge-zarge ne masu nauyi da ke nuna yiwuwar alaƙa mai zurfi tsakanin wasu masu rike da madafun iko da ’yan bindiga, abin da ke iya rushe ƙoƙarin jami’an tsaro tare da ƙara jefa rayukan al’umma cikin haɗari.

Ina da cikakken ra’ayi cewa musantawa kawai ba za ta wadatar ba. Idan ba a yi cikakken bincike ba, shakku zai ci gaba da ƙaruwa, kuma amincewar jama’a ga gwamnati da hukumomin tsaro za ta ƙara raguwa.

Haka kuma, matakin kai ƙara kan Sheikh Murtala Asada yana iya fassaruwa a idon jama’a a matsayin yunƙurin tsoratarwa da hana faɗin gaskiya, maimakon kare mutunci. Ina kira ga Sheikh Asada da ya fito da duk wata hujja da ke hannunsa, domin gaskiya ita ce ginshiƙin adalci, haka kuma bayyana dukkan gaskiyarsa gaban kotu zai taimaka don tabbatar da kare tsaron ƙasa.

A bayyane yake cewa babu wanda ya fi ƙarfin doka, kuma duk wani yunƙurin kare masu hannu a ta’addanci yana raunana tsaro tare da cin zarafin mutanen Arewa da Najeriya baki ɗaya.

Saboda haka, ina kira da a gaggauta kafa bincike mai zaman kansa, marar son zuciya, wanda Majalisar Ƙasa, hukumomin tsaro, da Ofishin Babban Lauyan Ƙasa za su jagoranta, domin binciken kuɗaɗe, kayan aiki, sadarwa da duk wata hulɗa da ka iya taimaka wa ’yan bindiga.

Dole ne a kare masu fallasa gaskiya, kuma duk jami’in gwamnati da aka samu da laifi ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ko ƙarfin ikonsa ba.

Arewa ta sha wahala ƙwarai sak**akon ’yan bindiga. Wannan lokaci ne na fuskantar gaskiya, ba na ɓoyewa ba. Lokacin shiru ya wuce. Lokacin gaskiya, adalci da ɗaukar mataki ya yi.

Ɗan'uwanku
Comr. Haidar H. Hasheem
Ɗan Arewa Mai Kishin Tsaro Da Tabbatar Da Adalci

Dole A Gaggauta Binciken Ƙaramin Ministan Tsaro Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga ~ Cewar CNG..... Gamayyar Kungiyoyin Are...
14/12/2025

Dole A Gaggauta Binciken Ƙaramin Ministan Tsaro Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga ~ Cewar CNG
..... Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Buƙaci A Gaggauta Bincike Mai Zurfi Kan Zargin Da Ake Yiwa Matawalle Da Alaƙa Da Yan Bindiga

Ƙungiyar Coalition of Northern Groups (CNG) ta bayyana damuwa mai tsanani kan ikirarin da Musa Kamarawa, tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Gwamnan Zamfara kuma Ministan Tsaron Ƙasa na yanzu, Bello Matawalle, ya yi a wani faifan bidiyon da yake nuna Matawallen na da alaƙa da tallafawa yan bindiga.

CNG ta ce zargin ya shafi tura kuɗi kai tsaye ga fitaccen shugaban ‘yan bindiga Bello Turji, sayen motocin Hilux da dama ga ƙungiyoyin ta’addanci, da kuma bayar da tallafin kayan aiki k**ar gidaje, shanu da sauran dukiya, wanda ake zargin ‘yan siyasa daga Zamfara da maƙwabtanta s**a taimaka wajen aiwatarwa.

A cewar CNG, waɗannan ikirari suna nuna yiwuwar alaƙa mai zurfi tsakanin wasu manyan jami’an gwamnati da ‘yan bindiga, lamarin da ka iya rusa ƙoƙarin sojoji tare da ƙara jefa al’umma cikin haɗari.

Ƙungiyar ta ce irin waɗannan zarge-zarge ba za a iya watsi da su ta hanyar musantawa kawai ba, domin hakan na ƙara haifar da shakku cewa ana ɓoye gaskiya.

CNG ta kuma soki matakin Ministan na kai ƙara kan Sheikh Murtala Asada, tana mai cewa hakan na iya zama yunƙurin hana faɗin gaskiya, maimakon kare mutunci. Ta bukaci Sheikh Asada da ya fito da dukkan hujjojin da ke hannunsa ba tare da tsoro ba.

Ƙungiyar ta jaddada cewa babu wanda ya isa ya fi karfin doka, kuma ɓoye masu hannu a ta’addanci na raunana tsaro da amincewar jama’a.

Saboda haka, CNG ta nemi bincike mai zaman kansa, binciken da babu son zuciya, wanda Majalisar Ƙasa, hukumomin tsaro da Ofishin Babban Lauyan Ƙasa za su jagoranta, domin binciken kuɗaɗe, kayan aiki, sadarwa da duk wata shawara da ka iya taimaka wa ‘yan bindiga.

Ta ce dole a kare masu fallasa gaskiya, kuma duk jami’in gwamnati da aka samu da laifi ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ko ƙarfin ikonsa ba.

CNG ta jaddada cewa Arewa ta sha wahala matuƙa sak**akon ‘yan bindiga, kuma wannan lokaci wata dama ce ta fuskantar tushen matsalar. Kare masu aikata laifi zai lalata makomar tsaro da amincewar jama’a. Lokacin ɓoyewa ya wuce, lokacin gaskiya da adalci ya yi.

Sa Hannun
Comr Jamilu Aliyu Charanchi
National Coordinator CNG

OPA Ta Soki Naɗin Amupitan a Matsayin Shugaban INEC, Ta Ce Cancantarsa Ba Ta Kai Ya Riƙe Hukumar Zaɓe BaOdua People’s As...
28/11/2025

OPA Ta Soki Naɗin Amupitan a Matsayin Shugaban INEC, Ta Ce Cancantarsa Ba Ta Kai Ya Riƙe Hukumar Zaɓe Ba

Odua People’s Assembly (OPA) ta fito fili ta bayyana rashin gamsuwarta da nadin Joash Ojo Amupitan, SAN, a matsayin sabon Shugaban INEC, tana cewa wannan nadin na iya zama barazana ga sahihancin zaɓe da kwanciyar hankali na demokradiyya a Najeriya.

A cikin sanarwar da Richard Olatunji Kayode ya fitar, OPA ta ce kasar tana fuskantar mawuyacin hali na rashin amincewa da sak**akon zaɓe, don haka wajibi ne INEC ta samu shugaba mai gaskiya, kwarjini da cikakken tarihin tsayuwa kan adalci wanda duka wannan halayen Amupitan bai cika su ba.

Kungiyar ta goyi bayan ƙungiyar kwararrun lauyoyi sama da 1,000 (ALDRAP), wadda ta riga ta yi tir da nadin, tana cewa akwai bayanan da ke nuna alakar siyasa tsakanin Amupitan da Ministan Abuja, Nyesom Wike, wasu majiyoyin ma na zargin yaron Wike ne, alakar da OPA ta ce na iya haifar da shakku game da ikon Amupitan na yin aikin da bai dace ba.

OPA ta yi gargadin cewa duk wani shugaban INEC da ke da inuwa ko kusanci da manyan ‘yan siyasa ba zai iya gina sahihin tsarin zaɓe ba. Ta ce idan aka yi watsi da waɗannan korafe-korafe, za a iya sake fadawa cikin rikici, rashin tabbas da asarar amincewar jama’a ga INEC.

Ta bukaci Majalisar Dattawa da ta yi amfani da mukamin amincewa cikin gaskiya, ba tare da siyasa ta shige ciki ba, domin kare demokradiyyar Najeriya.

A ƙarshe, OPA ta kira kungiyoyin farar hula, matasa, lauyoyi da ‘yan jarida su kasance masu sa ido, su kare muradun kasa, domin a samar da INEC da za ta yi aiki bisa gaskiya, ba tare da fargaba ko tsoron siyasa ba.

NDYC Ta Caccaki Wike da INEC Kan Yunkurin Rusa Dimokuraɗiyyar NajeriyaƘungiyar Niger Delta Youth Congress (NDYC) ta yi t...
25/11/2025

NDYC Ta Caccaki Wike da INEC Kan Yunkurin Rusa Dimokuraɗiyyar Najeriya

Ƙungiyar Niger Delta Youth Congress (NDYC) ta yi taron ’yan jarida domin bayyana damuwa kan yadda Ministan FCT, Nyesom Wike, da kuma yadda INEC ke nuna rashin adalaci game da sak**akon gangamin PDP na Ibadan ke zama babbar barazana ga dimokuraɗiyyar Najeriya.

NDYC ta zargi Wike da amfani da muƙaminsa wajen tsoma baki cikin jam’iyya, tayar da rikici, tsoratarwa da kokarin tilasta ra’ayinsa, abin da ke yi wa tsarin dimokuraɗiyya mummunar illa. Ta ce halayensa na nuna girman kai, raina doka da neman iko su na iya tarwatsa ƙasa.

Kungiyar ta roki Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gargaɗi Wike, ya tunasar da shi cewa shi bawa ne na jama’a, ba sarki ba.

A bangaren INEC kuwa, NDYC ta nuna damuwa kan yadda take jan kafa wajen tabbatar da zababben shugaban PDP Kabiru Turaki, tana nuna fifiko ga Damagum. Ta ce wannan ya tauye adalci, ya kuma lalata amincewar jama’a da hukumar zabe.

NDYC ta jaddada cewa sak**akon taron Ibadan halastacce ne, kuma INEC dole ta tsaya kan doka ba tare da shiga hannun masu son murde sak**akon siyasa ba don biyan buƙatar Wike.

Ta kuma bayyana cewa halayen Wike ba sa wakiltar mutanen Niger Delta gaba ɗaya.

A ƙarshe, NDYC ta ce za ta ci gaba da kare dimokuraɗiyya da doka, domin Najeriya ta fi kowane mutum girma, kuma duk wanda ya yi barazana ga tsarin mulki dole a tsawatar masa.

Da hannun
Comr. Israel Uwejeyan, National Coordinator, NDYC

22/11/2025

INEC's Shameful Bias

It’s now clear that INEC under this new chairman has abandoned neutrality and is gradually turning into Wike’s personal agency. The same INEC that spoke with confidence on Arise News on November 11 is now contradicting itself just to please Wike.

This sudden turnaround shows dangerous bias, a deliberate attempt to weaken the PDP and serve selfish political interests. A national institution should not dance to the tune of one politician, yet this INEC chairman seems ready to destroy credibility at all cost.

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDPA babban taron da ja...
21/11/2025

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDP

A babban taron da jam’iyyar PDP ta gudanar a Ibadan ranar Asabar da ta gabata, an ga wani sabon salo na shugabanci da jajircewa wanda ya tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa PDP har yanzu tana da waɗanda za su tsaya tsayin daka domin kare darajarta.

A cikin waɗanda s**a fito fili wajen nuna wannan kwazo, akwai Kauran Bauchi, wanda ya jagoranci aikin gyara da tsaftace jam’iyya da tsantseni. Tsayuwarsa wajen korar masu tada zaune tsaye a ciki, musamman waɗanda ke aiki da boyayyun manufa don rusa jam’iyyar daga cikin gida, ya zama abin yabo da koyi. A gaskiya, Kauran Bauchi ya zama ginshiƙin da ya hana jam’iyyar durkushewa.

Baya ga haka, Gwamnan Zamfara Dr. Dauda Lawal ya nuna irin kishinsa ga dimokuraɗiyya. Goyon bayansa ga sahihin tsari da adalci a cikin jam’iyya ya karfafa gwiwar mambobi da magoya baya, ya tabbatar masu cewa PDP na da shugabanni da ba za su lamunci karya ko shisshigi ba.

A bangaren Seyi Makinde, Gwamnan jihar Oyo, ya ba da cikakken gudunmawa wajen tabbatar da cewa taron Ibadan ya kasance sahihi, kuma cikin tsarin da ya dace. Makinde ya tabbatar da cewa jam’iyya ta gudana bisa ka’ida, ba tare da batan batu ko rikice-rikice ba, aikin da ya kara tabbatar da cewa PDP jam’iyyar da take da ni’imar shugabanni masu hangen nesa.

A tare, waɗannan manyan shugabanni uku sun yi abin da ake kira ceto martabar PDP, tare da dawo da yarda da kwarin gwiwar jama’a. Sun nuna cewa jam’iyyar adawa ba ta mutu ba, kuma ba za ta mutu ba, muddin akwai shugabanni irin su Kauran Bauchi, Dr. Dauda Lawal da Seyi Makinde.

A Ibadan, PDP ta sake tsayawa kan kafafunta kuma hakan ya sake busawa dimokuraɗiyya a rai.

Address

Potiskum State
Potiskum
YOBE

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Potiskum Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Potiskum Online News:

Share