Malumfashi Post

Malumfashi Post Exclusive News

Ya ta kaya a mazaɓarka ko kaima an buga ka da ƙasa.??
19/03/2023

Ya ta kaya a mazaɓarka ko kaima an buga ka da ƙasa.??

HOTUNA: An ruwaito cewa nan wasu ma'aikatan zaɓe ne, da s**a sha da ƙyar a ƙaramar hukumar kirfi ta jihar Bauchi.
19/03/2023

HOTUNA: An ruwaito cewa nan wasu ma'aikatan zaɓe ne, da s**a sha da ƙyar a ƙaramar hukumar kirfi ta jihar Bauchi.

DÁ ƊUMÍ ƊUMÍ: An Karrama Matashíyar Líkitar Nan Dr. Na'ima Idris Usman Kan Gudummuwar Da Také Bayarwa Wajén Ilmantar Da ...
27/12/2022

DÁ ƊUMÍ ƊUMÍ: An Karrama Matashíyar Líkitar Nan Dr. Na'ima Idris Usman Kan Gudummuwar Da Také Bayarwa Wajén Ilmantar Da Mata Da Kan Lafiyarsú A Kafafen Sadarwa Na Zamaní Wató "Social Innovation For Making The Best Use Of Social Media To Advocate Women Issues”

Wanné fata za kuyí mata ?

2023: Kotu ta tabbatar da hukuncin korar Al-Mustpha da wasu ƴan takarar AAA yau Alhamis ne wata babbar kotun tarayya da ...
27/12/2022

2023: Kotu ta tabbatar da hukuncin korar Al-Mustpha da wasu ƴan takarar AA

A yau Alhamis ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da bukatar ta janye hukuncin da ta yanke a ranar 4 ga watan Nuwamba na amincewa da ‘yan takarar da jagorancin Dr Adekunle Rufa’i Omo-Aje ya jagoranta na jam’iyyar Action Alliance (AA).

Mai shari’a Zainab Abubakar, a hukuncin da ta yanke, ta ce karar da Kenneth Obidiche Udeze ke jagoranta ya shigar ba ta da wani inganci.

Kamfanin dillancin labarai na Ƙasa ya rawaito cewa mai shari’a Abubakar a ranar 4 ga watan Nuwamba ta umarci hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ta amince da ƴan takarar da jagorancin Omo-Aje na jam’iyyar AA ya gabatar domin zaɓen 2023.

Alkaliyar ta kuma umurci INEC da ta yi watsi da ‘yan takarar da shugabancin ɓangaren Udeze ya gabatar, daga cikinsu har da Manjo Hamzat Al-Mustpha (mai ritaya).

Amma Udeze, wanda aka amince da dakatarwarsa da kuma korar shi a matsayin shugaban AA na kasa a wasu hukunce-hukunce guda biyu na kotun daukaka kara, ya bukaci babbar kotun ta Abuja da ta janye hukuncin na ranar 4 ga watan Nuwamba, yana mai cewa an same shi ta hanyar zamba ne, kuma ya na da'awar cewa har yanzu shi ne shugaban jam'iyyar na kasa.

Da ta ke yanke hukuncin a yau, Mai shari’a Abubakar, ta ce, bayan hukuncin kotun daukaka kara biyu da kuma wani hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke a Abeokuta, Udeze ba zai iya yin ikirarin cewa shi ne shugaban jam’iyyar ba a bisa doka.

Hukunce-hukunce guda biyu na Kotun Daukaka Kara an yanke su ne a ranar 7 ga watan Janairu da 11 ga watan Nuwamba, yayin da kotun Abeokuta ta yanke hukuncin a ranar 8 ga watan Satumba, ƙarƙashin mai shari’a J. O. Abdulmalik a cikin wata kara mai lamba: FHC/AB/CS/120/2022.

Alkalin kotun ta ce hukuncin da ta yanke a ranar 4 ga watan Nuwamba bai samu ta hanyar zamba ba kamar yadda Udeze ya yi zargi.

Ta bayyana Udeze a matsayin mutum ne mai cike da ruɗani kuma mai shiga tsakani, ya na kokarin tsoma baki a harkokin jam’iyyar da aka dakatar da shi daga bisani kuma aka kore shi.

Don haka Abubakar ta yi watsi da karar.

NAN ta ruwaito cewa Al-Mustapha, tsohon mai taimaka wa marigayi Janar Sani Abacha ne ya lashe zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na jam’iyyar da bangaren Udeze s**a gudanar da jimillar kuri’u 506, inda ya doke Samson Odupitan wanda shi ne abokin hamayyarsa tilo a ranar 9 ga watan Yuni a Abuja.

Dokar takaita cirar kuɗi ba don taimaka wa APC a zaɓen 2023 ba ne, CBN ya faɗa wa majalisar wakilaiBabban bankin Najeriy...
27/12/2022

Dokar takaita cirar kuɗi ba don taimaka wa APC a zaɓen 2023 ba ne, CBN ya faɗa wa majalisar wakilai

Babban bankin Najeriya, CBN, ya ce manufarsa ta kayyade yawan kudaden da za a riƙa cire wa a banki ba don siyasa ba ne, sabanin zarge-zargen da ake yi.

Aisha Ahmad, mataimakiyar gwamnan CBN, ta bayyana haka a Abuja a yau Alhamis lokacin da ta ke amsa tambayoyi daga ‘yan majalisar a zauren majalisar wakilai yayin zaman majalisar.

Misis Ahmad, wacce ta wakilci gwamnan babban bankin kasa CBN, Godwin Emefiele, ta ce manufar ta zo ne bayan tunani da bincike mai zurfi.

Ta yi wannan tsokaci ne ga tambayar da Chinedu Obidigwe (APGA-Anambra) ya yi ma ta, wanda ke son sanin ko manufar tana da nufin fifita jam’iyyar APC a zaben 2023.

Ahmad ta ce bankin na CBN ya bayar da umarnin a buga Naira biliyan 500 domin zagaya wa cikin al'umma, inda ta ce bankin ya yi sassauci ta hanyar duba manufofin cire kuɗi sama da Naira 100,000 zuwa Naira 500,000 ga daidaikun mutane da kuma daga Naira 500,000 zuwa Naira miliyan 5 ga kamfanoni. .

Ta ce ana sa ran manufar za ta samar da sabbin guraben ayyukan yi a bangaren fasahar sadarwa, sabanin yadda ake ta yada jita-jita cewa za ta kai ga rasa ayyukan yi.

Ta ce manufar ba za ta shafi masu gudanar da kamfanin na Point on Sales, POS, inda ta ce CBN na sane da cewa POS din ya samar da hanyar rayuwa ga ‘yan Najeriya kimanin miliyan 44.

Ahmad ta sha tambayoyi da ga ƴan majalisar da su ka yi tambayoyi masu da dama a kan sabon tsarin kudi.

Femi Gbajabiamila, shugaban majalisar, ya ce dalilin da ya sa ya kamata a yi wa majalisar bayani a kan irin wadannan manufofin shi ne, ‘yan majalisar su wakilai ne na wakilci jama’a.

Ya kara da cewa duk da cewa sake fasalin naira na iya zama kyakkyawar niyya, amma ya zama dole babban bankin ya dauki ‘yan majalisar.

KACICÍ-KACICÍ: Ko masu karatú zasu iya faɗa mana sunan waye wannan ?
27/12/2022

KACICÍ-KACICÍ: Ko masu karatú zasu iya faɗa mana sunan waye wannan ?

Idan na sauka da ga mulki zan yi nesa da Abuja -- BuhariShugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce ba zai tare a babban birnin...
27/12/2022

Idan na sauka da ga mulki zan yi nesa da Abuja -- Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce ba zai tare a babban birnin tarayya Abuja ba bayan ranar 29 ga watan Mayun 2023 domin kada ya shiga cikin harkokin mulkin magajinsa.

Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin mazauna babban birnin tarayya Abuja, karkashin jagorancin Ministan Abuja, Mohammed Bello, wadanda s**a kai masa ziyarar bikin Kirsimeti a jiya Lahadi a fadar shugaban kasa, Abuja.

A wajen bikin Kirsimeti na karshe da ya yi da al’ummar babban birnin tarayya Abuja, shugaban ya jaddada cewa zai dawo garinsa Daura na jihar Katsina a karshen wa’adinsa.

A cewarsa, matakin da ya dauka na kin mayar da Abuja ta zama mazauninsa dindindin shi ne ya baiwa magajinsa damar gudanar da harkokin gwamnati ba tare da katsalandan ba.

Shugaban ya kuma shaida wa al’ummar babban birnin tarayya cewa bai gina sabon gida a Daura ba ko kuma a ko’ina ba, kuma yana fatan ya zauna a gidan na sa kwaya ɗaya na tsawon shekaru.

Shugaba Buhari ya kuma yi amfani da wannan dama wajen yabawa Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, inda ya ce ya dade yana rike da mukamin minista saboda gaskiya da kwazonsa.

Kisan Ummita: Alkali ya sake kiran mahaifiyar Ummukulsum da ɗan sanda A yau Juma’a ne wata babbar kotun Kano ta umarci g...
27/12/2022

Kisan Ummita: Alkali ya sake kiran mahaifiyar Ummukulsum da ɗan sanda

A yau Juma’a ne wata babbar kotun Kano ta umarci gwamnatin jihar Kano da ta dawo da mahaifiyar Ummulkulsum, Fatima Zubairu da PC Aminu Halilu domin sake yi musu tambayoyi kan zargin kisan da wani dan kasar China, Frank Geng Quangrong, mai shekaru 47 ya aikata a kan ƴarta.

Ana tuhumar Frank, wanda ke zaune a Railway Quarters a Kano da laifin kisan kai, kuma ya aikata laifin ne a ranar 16 ga Satumba, a Janbulo Quarters ,Karamar Hukumar Gwale a Kano.

Ana zarginsa da daɓa wa Ummulkulsum, wacce aka fi sani da Ummita, mai shekaru 22 wuka a unguwar Janbulo da ke Kano.

Lauyan da kare Quanrong, Muhammed Dan’azumi ya roki kotun da ta sake kirawo mahaifiyar Ummulkulsum da kuma ɗan sanda Halilu domin a sake yi musu tambayoyi, kamar yadda sashe na 258 na kundin dokar laifuka, ACJL, ya bada dama.

ACJL ya ce “kodayaushe kotu na iya kiran shaidu ko kuma ta kira shaidu don bincike da sake bincikarsu idan ana ganin suna da mahimmanci ga shari’a.

Dan’azumi ya kuma yi rokon kotu ta gayyaci babban daraktan lafiya ko babban jami’in kula da lafiya na asibitin kwararru na Murtala Muhammed da ya gurfana a gaban kotun.

Ya roki kotu da ta amince da wannan rokon nasa.

Ibrahim Arif Garba, lauyan masu shigar da kara bai yi s**a a kan hakan ba.

Bayan sauraron dukkan bangarorin biyu, Alkalin kotun, Mai shari’a Sanusi Ado Ma’aji ya amince da rokon sake kiran shedu da babban daraktan lafiya ko babban jami’in kula da lafiya na asibitin kwararru na Murtala Muhammed da su gurfana a gaban kotu.

Ma’aji ya ɗage ci gaba da shari’ar har zuwa ranar 11 ga watan Janairu da kuma 12 ga watan Janairu domin jin shaidun kariya.

27/12/2022

Shin wa ya fi burge ka da kwanta maka a rai a cikin ‘yan siyasar Najeriya ?

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya bukaci al'ummar kasar da su zabi wanda suke so daga kowace jam'iyya a babban zab...
11/11/2022

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya bukaci al'ummar kasar da su zabi wanda suke so daga kowace jam'iyya a babban zaben shekarar 2023.

Shugaba Buhari ya kuma ce, ba za a lamuncewa wani ya yi amfani da kudi ko 'yan bangar siyasa wajen tsoratar da wata mazaba.

Mene ne ra'ayinku game da kalaman shugaban?

Yan bindiga sun sace mutum fiye da 30 daga gonaki a karamar hukumar Faskari da ke jihar Katsinan Najeriya, mazauna yanki...
06/11/2022

Yan bindiga sun sace mutum fiye da 30 daga gonaki a karamar hukumar Faskari da ke jihar Katsinan Najeriya, mazauna yankin na cewa, hare-haren 'yan bindiga sun dawo gadan-gadan.

ZAƁÈN 2023: Idan Múka Cí Zaɓé, Cìkìn Watanní 6 Za Mú Gama Da Matsalar Tsarón Nájeriya, Céwar Kashìm Shettíma - Mé za kúc...
06/11/2022

ZAƁÈN 2023: Idan Múka Cí Zaɓé, Cìkìn Watanní 6 Za Mú Gama Da Matsalar Tsarón Nájeriya, Céwar Kashìm Shettíma

- Mé za kúcé ?

Muddín Na Zama Shúgaban Ƙasa, NECO, WAEC, NABTEB, NBAIS, Za Sú Kasancé Kyaúta, Wa'adin JAMB Kúma Zaí Kasance Shékaru Húɗ...
05/11/2022

Muddín Na Zama Shúgaban Ƙasa, NECO, WAEC, NABTEB, NBAIS, Za Sú Kasancé Kyaúta, Wa'adin JAMB Kúma Zaí Kasance Shékaru Húɗú, Céwar Kwankwaso

Kwankwaso ya bayyana haka ne dai dai lokacin da yake bayyana manufofin takarar sa na shugaban kasa.

DÁGA Salisu Magaji Fandalla'fih

05/11/2022

Faɗa mana súnan ɗan siyasar da ka sani kuma kaké ganìn yana yìwa al'ummar da yake wakilta abinda ya kamata.

MASHA ALLÀH: Za'a Gúdanar Da Tarón Hada Kan Músulman Nájerìya Ɗan gídan Sheíkh Ɗahíru Bauchi, Sheikh Ibrahim Sheíkh Tahi...
05/11/2022

MASHA ALLÀH: Za'a Gúdanar Da Tarón Hada Kan Músulman Nájerìya

Ɗan gídan Sheíkh Ɗahíru Bauchi, Sheikh Ibrahim Sheíkh Tahir Bauchí ne ya sanar da hakan a shafinsa.

Sheik Ibrahim Sheíkh Ɗahíru Bauchí ya ce "tare da Sheíkh Bala Lau, yayin tattaunawa ta musamman cikin cigaba da shirye-shirye da muke yi na shirya taro na musamman don samun ingantaccen hadin kai da zaman lafiya tsakanin musulman Nijeriya baki daya".

EFCC ta ƙwace gidaje 40 na Sanata Ekweremedu.Cikin gidajen da EFCC ta kwace a hannun Sanata Ike Ekweremedu akwai a wurar...
05/11/2022

EFCC ta ƙwace gidaje 40 na Sanata Ekweremedu.

Cikin gidajen da EFCC ta kwace a hannun Sanata Ike Ekweremedu akwai a wurare kamar haka;

3 a Amurka
2 a Ingila
10 a Enugu
9 a Dubai
15 a Birnin Abuja
1 a Legas

Wadannan sune s**a bayyana.

Gwamnan jihar Rivers Nyesom Wike ya nada mutum 200,000 a cikin kwana biyu a matsayin mataimakansa na musamman. Gwamnan y...
05/11/2022

Gwamnan jihar Rivers Nyesom Wike ya nada mutum 200,000 a cikin kwana biyu a matsayin mataimakansa na musamman. Gwamnan ya ce kokari ne na ganin ya taimaka wa mutanen jihar samun kudin kashewa domin samun rufin asiri.

Shin wannan mataki ne na kyautata wa al'umma ko kuma bata kudaden al'umma?

📷 Gov Nyesom Ezenwo Wike - CON

ZARAR BÚNÚ: Wató dúk lokacìn ka Saurarì Baba saí ka ga dama can kó Kansíla baí dacé ya zama ba. Ní na rasa ma mé muka ga...
05/11/2022

ZARAR BÚNÚ: Wató dúk lokacìn ka Saurarì Baba saí ka ga dama can kó Kansíla baí dacé ya zama ba. Ní na rasa ma mé muka ganì tún farko har muka haƙiƙice cewa sai wannan bawan Allahn. Ba aiki a ƙasa, ba magana mai daɗi, ba tausayi, ba nadama kuma ba kunya, Cewar Barista Bulama Bukarti

Mé za kúcé ?

Address

Malumfashi

Telephone

+2348085428262

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Malumfashi Post:

Videos

Share