Malumfashi Reporters

Malumfashi Reporters Domin samun sahihai kuma ingantattun labarai, na yau da kullum.

Aunty Fauziyya D. Sulaiman; Gatar Marasa Gata. Burbushin Matan Sahabbai.Haqiqa ita gata ce, garkuwa ce, kuma uwa ce ga w...
26/10/2023

Aunty Fauziyya D. Sulaiman; Gatar Marasa Gata. Burbushin Matan Sahabbai.

Haqiqa ita gata ce, garkuwa ce, kuma uwa ce ga wadanda s**a rasa gata, mace ce irin wacce tayi fintinkau a cikin tsararrakin ta mata da maza, samun tamkarta sai an tona kwarai, ta sanya walwala a fuskokin mutanen da bata san adadin su ba, tayi sanadiyar canzawar rayuwar mutane marasa adadi, ita abar yarda ce dari bisa dari ga masu buqatar sarrafa dukiyar su ta hanyar taimakawa mabuqata, ina mai basu tabaccin dukiyar su zata kai ga ire-iren mabuqatar da suke cikin yanayi na buqatar taimako kwarai.

Kuyi amfani da dukkan wani nau'in suna na Girmamawa da kuka sani, a yayin da kuka tashi ambatar sunan wannan baiwar Allah, dukkan sunan girmama da kuka ambace ta da shi, ba alfarma kuka yi mata ba, ina yi muku rantsuwa da Allah ta cancanci hakan daga garemu, alkairan ta ba zasu lissafu ba, babu abinda zamu ce da Aunty Fauziyya D. Sulaiman saidai muce Allah ya saka mata da alkhairy, zuciyar (FAUZIYYA) ba bu hassada ko ƙyashi a ciki, bata da ƙyamar mutane, ta na da tsarkin zuciya, kullum hannun ta mai bayarwa ne ga talakawa, ba ta da kwaɗayi, ta na girmama kai, amma sam - sam ba ta da girman kai, ta na da tausayi, mai son karatu da makaranta ce, mai son nishaɗi ce da raha, akwai ta da ƙoƙarin dogaro da kai, ta na son rayuwa ta girmama juna da mutunta juna.

HAJIYA FAUZIYYA D. SULAIMAN YAR ALJANNA CE IN SHA LLAHU DAMU BAKI DAYA.

Gwagwarmaya itace da gewa da jajircewa domin kawowa al'umma mafita a cikin cigaban rayuwarsu ko addininsu, Hajiya Fauziya D sulaiman duniya ta shaida da tarin alkhairin dake yi a cikin gwagwarmayarta, Macece mai fikirar rubutun labari, ko na film ko kuma na littatfi masu ma'ana da suke koyar da darasi ga rayuwar al'umma, kullum cikin fafutuka take da gwagwarmaya domin nemawa al'umma talakawa marasa qarfi taimako, tayi sanadin ceton rayuwar jama'ar annabi marasa adadi wanda s**a kamu da matsanantan rashin lafiya wajen nema musu tallafin kudin magani karkashin qungiyarta mutanen data ciyar bazasu lissafu sannan tayi sanadin da marayu da talakawa da yawa s**a samu matsuguni ko da yaushe dare da rana aikin tallafawa mabuqata shine a gabanta samun mutanen arziki irinsu hajiya fauziyya babbar rahama ce, duniya ta shaida da ayyukan alkhairinta bugu da kari macece mai kare mutuncin addininta a duk inda take bata wasa da addininta da al'adarta.

A shekarun baya lokacin ina yawan karance karance litattafin hausa ina yawan karanta litattafanta. To amma daga baya da na daina karatun litattafai sai na daina jin d'uriyarta. Kwatsam yanzu kuma sai nake yawan cin karo da postings dinta a media duk da dai bata cikin friends nawa.

Fauziyya D. Suleman marubuciya ce. Kuma macece jajirtacciya mai tsayawa akan lamarin talakawa wadanda basu da gata Ta zama tamkar uwa ko uba a garesu.Yawan kai kawo da take yi akan abin da ya shafi tallafi da nemawa bayin Allah taimako har ya mantar da ita aikinta. Kuma da alama Allah ya hadata da miji mai goya mata baya da bata had'in kai kan wannan aikin da ta d'orawa kanta.

Malama Fauziyya ba wai da aljihunta take taimakawa mabuqata ba a'a Tana dai amfani da baiwar da Allah ya bata ne ta rubutu tana taimakawa wajen rubuta halin da wani ko wata ke ciki game da rashin lafiya da kuma yawan kudin da ake buqata a wajen sayen magani Bayan rubutu kuma tana bin mutane masu hali wadanda suke da zuciyar tausayi tana kai musu koken talakawa Cikin ikon Allah sai ka ga duk yawan kudin da ake buqata an dace Babban kuma abin da ke birgeni da tsarin aikinta shine duk wani tallafi da ta samo ko adadin kudin da aka samu tana yin posting tare da sunayen wadanda s**a bayar din dan cire shakka ko zargi A takaice dai komai dai ana yinshi a bisa tsari da kuma dacewa.

Da irin wannan zamu fahimci cewa taimakon mabuqata ba sai mai kudi ba Ni da kai duka zamu iya yinsa ta hanyar yin amfani da irin baiwar da Allah ya bamu Kuma irin wannan aikin shine za kayi ko bayan ranka mutane ba zasu manta da alkhairyn da kayi musu ba Kuma uwa uba ka tarar da tarin ladan ka a cen lahira yana jiranka.

Muna rokon Allah (SWT) ya saka mata da mafificin alkhairinsa ya cigaba da daga kima da mutuncinta, Allah (SWT) ya kara mata Imani, lafiya, arziki da daukaka alfarmar Annabi Muhammad (SAW) Allah (SWT) ya yi mata tsari daga kowane irin sharri na duniya, Allah (SWT) ya yi ma gabanta da bayanta albarka saboda Alfarmar Annabi Muhammad (SAW).

YA ALLAH KA TALLAFAWA DUK MAI TALLAFAWA AL'UMMAH 🙏🙏🙏

Rubutawa ✍️ Abubakar S Malumfashi

Ko ka san cewa ƙasar FALASƊIN ita ce ƙasar da aka kira ta da ƙasar ANNABAWA!??👇01: Falasɗin ta kasance ƙasar Annabawan A...
21/10/2023

Ko ka san cewa ƙasar FALASƊIN ita ce ƙasar da aka kira ta da ƙasar ANNABAWA!??👇

01: Falasɗin ta kasance ƙasar Annabawan Allah, amincin Allah ya tabbata a garesu baki ɗaya.

02: Annabi Ibrahim (a.s) shine ya fara yin hijira zuwa ƙasar Falasɗin.

03: Allah Ta’ala ya tseratar da Annabi Lut (a.s) daga azabar da ta afkawa Mutanensa a ƙasar Falasɗin.

04: Annabi Dawud (a.s) ya rayu a wannan ƙasar, kuma ya gina masallaci a nan.

05: Annabi Sulaiman (AS) ya kasance yana zaune a ƙasar nan, kuma yana mulkin duniya baki ɗaya.

06: Annabi Musa (A.S) ya gaya wa sahabbansa game da wannan ƙasa da kuma shiga wannan gari mai tsarki (Falasɗin). Ya kira wannan gari da mai tsarki saboda kasancewarsa ya barranta daga shirka da kuma kasancewarsa ƙasar Annabawa.

07: Mu'ujizozi da dama sun faru a wannan gari, ciki har da haihuwar Annabi Isah ɗan Maryam amincin Allah su tabbata a garesu.

08: A lokacin da Mutanen Annabi Isa (AS) s**a so su kashe shi sai Allah Ta’ala ya dauke shi zuwa sama daga Qudus (watau Jerusalem).

09: Ɗaya daga cikin alamomin tashin ƙiyama shine dawowar Annabi Isa (AS) duniya a wannan ƙasar.

10: Annabi Isa (AS) zai kashe Dajjal a wani waje da ake kira (Bab Lud) a wannan ƙasar.

11: Falasɗin ita ce ƙasar da za a tashe kowa, Allah ya yi masa hisabi.

12: Daga wannan birnin ne Yajuju da Majuju za su fito su yaƙi Mutanen duniya da hargitsa duniyar.

13: Bayan haka ƙasar Falasɗin tana da darajar kasancewarta ALQIBLA ta farko ta Musulmi bayan an wajabta salloli biyar. Daga baya aka umurci Annabi Muhammad (ﷺ) da ya juya fuskarsa daga Masallacin Aqsa na (Jerusalem) zuwa Ka’aba na (Makkah) yayin Sallah. Masallacin da wannan lamari ya faru har yanzu ana kiransa da sunan Masallacin (Al-Qibla).

14: Bayan haka kuma anzo da Manzon Allah (ﷺ) daga Makka zuwa BAITUL-MAQDIS (Jerusalem) kafin a dauke shi zuwa sama a daren Mi'iraji.

15: Dukan Annabawa sun yi sallah anan, bayan da Annabi Muhammad ﷺ ya jagorance su sallah. Shine dalilin da yasa Falasɗin ta zama ƙasar dukkan Annabawan Allah.

HADISI👇
16: Sayyidina Abu Zarr yana cewa: "Na tambayi Manzon Allah ﷺ, wane Masallaci ne aka fara ginawa a doron ƙasa? Sai ya ce: Masjidul Haram (wato Ka'aba). Yace sai wanne kuma sai Mazon Allah ﷺ ya ce: Sai Masallacin Al-Aqsa (wato BAITUL-MAQDIS). Sai nace shekara nawa tsakanin su biyun? Sai Annabi (ﷺ) ya ce: Shekaru Arba'in ne, (40yrs) kuma duk lokacin da ku ka samu dama, ku yi salla a can"

17: A zamanin mulki na Musulunci, Sayyidina Umar na matsayin Khalifa, ya bar duk sauran yaƙuƙuwan da Musulmi suke yi a faɗin duniya, don ƙwato Falasɗin, da kansa ya fita daga Madina yaje ya yi sallah a a wurin, yana mai bayyana mahimmanci da girman wannan ƙasar.

18: Sake ƙwato wannan ƙasar da (SULTAN) SALAHUDDEEN AL-AYYUBI ya yi a ranar Juma’a 27 ga watan Rajab 583 Hijira, shi ma alama ce ta izzar Allah.

19: Sunan Jerusalem shi ne (Baitul Maqdis) saboda tsarkin wannan birni wanda shine ya bambanta shi da sauran garuruwa, sama da Sahabban Manzon Allah (ﷺ) 5000 ne s**a sadaukar da rayuwarsu wajen mallakar wannan gari da kuma ceto shi daga zaluncin Romawa Kirista.

20: Musulmi su sani cewa: ba a rufe babin shahada ba wajen dawo da martabar wannan wuri (Qudus) daga hannun YAHUDAWA maƙiya Allah da Manzonsa ba. Kuma wannan birni na Qudus ana kiransa da suna birnin (SHAHIDAI)

Allah ya taimaki Addinin Musulunci da Musulmi Allahumma Ameen!! 🇵🇰🕌🕋☪️🤲

Nazir Umar (naxeer_kaoje)

Engr. Muntari Sagir Yaba  mahaddatan makarantar sheik Dahiru Usman Bauchi, dubu biyar biyar su 42 tare da Alkawarin zaga...
21/10/2023

Engr. Muntari Sagir Yaba mahaddatan makarantar sheik Dahiru Usman Bauchi, dubu biyar biyar su 42 tare da Alkawarin zagaye makarantar da kuma gyara ajujuwa 4.

Allah ya saka masa da alkhairi Aameen.

HOTO:Lokacin da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da Gwamna Abba Kabir Yusuf suke raba dollar Amurka $200 kwatankaacin ku'din...
21/10/2023

HOTO:

Lokacin da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da Gwamna Abba Kabir Yusuf suke raba dollar Amurka $200 kwatankaacin ku'din naira N200,000 ga ko wanne dalibi cikin daliban da Gwamnatin Jihar Kano ta dauki nauyin turasu Zuwa kasar India domin karo karatu.

An rabawa daliban ku'din ne amatsayin ku'din Shan ruwa a hanya koda zasu ga Wani Abu a hanya suyi sha'awa.

MÚHAWARA: A Cìkìn Manyan Ƴan Síyasar Nájeriya, Wanéné Kuké Túnanìn Céwa Zai Iya Tara Irín Waɗannan Mútanen Haka, Ba Tare...
21/10/2023

MÚHAWARA: A Cìkìn Manyan Ƴan Síyasar Nájeriya, Wanéné Kuké Túnanìn Céwa Zai Iya Tara Irín Waɗannan Mútanen Haka, Ba Tare Da Ya Basu Kó Sisin Kwabó Ba, Saí Dan Sabóda Ƙaunar Da Súké Masa ?

Ku ida mana kirarin da ake yi ma garin MalumfashiMalumfashi garin...
21/10/2023

Ku ida mana kirarin da ake yi ma garin Malumfashi

Malumfashi garin...

28-August- 2023BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI GIRMA GWAMNAN JIHAR KATSINA (DR) UMAR DIKKO RADDA, DANGANE DA MATSALAR TSAR...
29/08/2023

28-August- 2023

BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI GIRMA GWAMNAN JIHAR KATSINA (DR) UMAR DIKKO RADDA, DANGANE DA MATSALAR TSARO DA TAKAITA HAWA BABUR DA KEKE NAPEP A WASU SASSAN JIHAR KATSINA.

(The governor of Kastina state)

Assalamu alaikum-warahamatullahi’ta’alah’ wabarakatuhu, bayan gaisuwa irin ta Addinin Musulunci tare da girmamawa a gare ka a matsayinka na tsanin al’ummar jihar Kastina a ciki har da ni mai wannan rubutu, ina mai anfani da wannan dama a wannan kafar sadarwa ta zamani na isar ma ka da tawa shawara a matsayi na Wanda kake wakilta a karkashin jagorancinka, wanda ni din ba kowa ba ne face Dan jihar Kastina mai kishi da fatan ganin wannan jihar tamu ta samu maslaha

Tare da girmamawa da mutuntawa a gare ka a matsayinka na wanda Allah (SWT) ya dorawa amanar al’ummar wannan jihar, ina rokon Allah (SWT) ya cigaba da shiga cikin wannan Jagoranci na ka, Allah (SWT) ya yi ma ka gudunmuwa gurin sauke nauyin da Allah (SWT) ya dora ma ka na al’ummar wannan jihar.

A matsayinka na gwamana, mai gaskiya da rikon amana, Dan-kishin jihar Kastina Jagoran wannan jihar ta katsina, wanda Allah (SWT) ya baiwa cikakkiyar amanar kula da tsaro da rayuwar al’ummar jihar Kastina da daukacin jihohi (36) da Babban Birnin jihar Kastina.

Mai girma gwamna, tsokaci akan dokar hana hawa mashin da Keke napep a wasu
Sassan jihar Kastina
domin yin kira da nuni akan sake dawo da dokar takaita hawa mashin da Keke napep a wasu sassa na jihar ita dai wannan doka anyi ta a baya amma ba ta yi tasiri ba illa ma kara jefa masu amfani da wannan lokutan dan samun abinci cikin kunci da wahala

Mai Girma gwamna, mutane suna ganin cewa koda yake saka dokar dalilin tsaro yanada amfani, amma kuma lokachin da aka sanya yayi kadan, da haka Muke rokon gwamnati ta sake duba wannan dokar ta maida ta zuwa Karfe goma (10) maimakon karfe bakwai (6) da dokar ta ayyana
Ko kuma a janye dokar baki daya a lalubo wata sabuwar hanya domin magance matsalar tsaro
Muna fatan gwamnati zata duba korafe korafen Al'umma wajen sake nazari akan wannan sabuwar dokar

A matsayi na haifaffen garin malumfashi, Dan asalin jihar Kastina, Almajiri, talaka da ba kowa ba, ina mai anfani da wannan dama na bayar da tawa shawara zuwa gare ka, akan matsalar tsaron jiharmu ta Kastina, k**ar yadda Sashe na talatin da tara (Section 39) na Kundin Tsarin Mulkin wannan Kasa 🇳🇬 ya ba ni iko da damar tofa albarkacin baki na akan al’amurran da s**a shafi jiha ta, ko kuma wannan kasa ta mu.

Ya mai girma gwamna, da son samu na ne na isar da wannan muhimmin sako zuwa gare ka daga ni sai kai, amma ba ni da irin wannan damar a yanzu, shi ya sa na zabi wannan hanyar ta rubutu a wannan kafa, domin isar da sako na gare ka.
duk wata Gwamnati da ta tabbatar da cewa tana kishi da tausayin talakawa, to tana fara yin tunani ne akan halin da su talakawan za su kasance, kafin ta zartar da wata doka a kan su
Sometimes na kan tambayi kaina, shin wai shuwagabanninmu basu da labarin halin da mu talakawa masu qaramin qarfi muke ciki ne? kawai ku saka doka ba tare da kun san irin abin da dokar zata janyo ba babu laifi ku saka doka amma is good ace kun fito da wasu hanyoyin da talakawa zasu samu sauki.

Tabbas harkar tsaro a qasa ko a jaha babban barazana ce ga al'umma, to amma bai dace a mayar da hanyoyin kawo gyara masu tsauri irin haka ba, ku duba waccen tsohuwar gwamnati a karkashin Jagoranci Mai girma tsohon gwamnan jihar Kastina His excellency, hon Aminu bello masari har network na kusan tsawon sati biyu ko watanni aka yanke mana, ta dalilin haka mutane da yawa sun shiga wani hali na qunci, musamman 'yan kasuwa, amma bayan dawowar network din harkar tsaro Babu Wani Cigaba da aka samu 😭

Mai girma gwamna, ina mai anfani da wannan dama na bayar da tawa shawara zuwa gare ka akan matsalar tsaron da ta addabi wannan jihar Kastina a matsayi na ba kowa ba, Dan Kasa na gari mai kwanciya da tashi da bakin cikin halin da al’ummar wannan Kasa musamman mutanen Karkara suke ciki.

Mai Girma gwamna, ina ganin matsalar tsaron wannan jihar ba karancin mak**ai ba ne ke haifar da chikas ba, a nawa tinani a da karamar fahimta, manyan matsalolin da ke haifar da tangarda a fagen aikin Jami’an Tsaron Nijeriya bai fi k**ar haka ba.

• Karancin Jami’an Tsaro ba.
• Karancin hanyoyin sadarwa ba.
• Rashin baiwa Jami’an Tsaro cikakkun hakkokinsu.

1• Mai girma gwamna, a cikin wannan jihar tamu ba ko ina ke da (Network) din kiran wayar hannu ba, galibin guraren da yan ta’adda ke fakewa a cikin wannan jihar babu (Network) na kiran waya, galibin al’ummar da suke kaiwa farmaki mutanen Karkara ne da babu (Network) din kiran waya a garuruwansu, saboda haka akwai bukatar a samar ma Jami’an Tsaron Yan-sandan ingantattun hanyoyin sadarwa irin na zamani wadan da kowane Jami’in Dan sanda zai iya magana da Dan-uwansa a katsina misali:

• A jiha ya zama kowane (CP) idan ya yi magana 📱 ya zama kowane (DPO) yana karbar sakon (CP) kai tsaye musamman umurnin ko ta kwana.

• (DPOs) idan su ka yi magana a yankunan da suke kula da su, kowane Jami’in tsaron Dan-sanda dake karkashin Jagorancinsu yana rike da wayar hannu 📱 da zai ji wannan umurnin kai tsaye.

2• Mai girma gwamna akwai bukatar a inganta rayuwar Jami’an Tsaron wannan jihar da Iyalansu, domin mutane ne k**ar kowa, amma s**a aminta s**a yarda su bayar da lokacinsu, lafiyarsu da rayuwarsu domin kare kima da mutuncin wannan jihar ta mu da al’ummar cikinta.

Mai girma gwamna, da an dauki wadannan matakai ina ganin babu maganar cin hanci a wannan jihar, babu maganar gudu ko ja da baya a fagen yaki da yan ta’adda masu yinkurin kawo ma wannan jihar tangarda.

Mai girma gwamna, wallahi al’ummar jihar Kastina muna cikin mawuyacin hali na rashin tsaro, domin babu ranar da ba a yi masu kisan gilla a gidajensu, a gonakinsu, akan hanyarsu ta zuwa neman abinci, al’amarin kullum kara rinchabewa yake yi, Jami’an Tsaro suna yi iya bakin kokarinsu, domin su ma mutane ne k**ar kowa, na san kana samun rahotannin dik halin da al’ummar wannan jiha ta Kastina suke ciki, kuma a matsayinka na (gwamna) mai gaskiya da rikon amana na san ka san abunda ake kira da tsaro.

Mai girma gwamna, babu shakka na san kana iya bakin kokarin ka na daukar matakan da s**a dace, domin magance wannan musiba ta rashin tsaron jihar Kastina baki dayanta, amma akwai bukatar ka chanza salon yaki da wadannan mutane masu yinkurin rusa wannan jihar ta mu.

Mai girma gwamna, a tarihin yake yake na duniya, babu inda wata Kasa ko al’umma su ka taba shiga yaki, s**a samu cikakkiyar nasara ba tare da sun hada kawunansu a guri daya ba, haka zalika babu inda wata Kasa ko al’umma ta shiga yaki a cikin gidanta akwai matsalar rashin hadin kai kuma ta samu nasara.

Mai Girma gwamna, akwai bukatar ka kira taron gaggawa na masu ruwa da tsaki daga jihar Kastina, k**a daga Dattawa, Shuwagabanni, Malaman Addinin Musulunci, Sarakuna, yan-siyasa, yan kasuwa, Mata da Matasa babu maganar Jam’iyyar APC ko PDP, domin sai al’umma na zaune lafiya, rayuwa tare da dukiyoyin su ake maganar siyasa ko Jam’iyyar siyasa, ka nemi su hada kawunansu a guri daya, ka roke su wanda ke gaba da wani kowa ya yafewa kowa, kowa ya bayar da shawararsa, domin yakar wannan musiba ta rashin tsaro a jihar Kastina.

Mai girma gwamna, ina mai ba ka tabbacin idan Allah (SWT) ya ba ka ikon anfani da wannan shawara ta wa, babu shakka za ka ga alfanunta, kuma da izinin Allah (SWT) za a samu cikakkiyar nasarar yakar wannan musiba ta rashin tsaro a wannan jiha ta katsina.

Mai girma gwamna, ina yi ma ka fatan alkhairin samun cikakkiyar nasarar ganin bayan dikkanin matsalolin tsaron wannan jihar mu, Allah (SWT) ya cigaba da k**a ma ka, Allah (SWT) ya kara ma ka lafiyar da za ka sauke dikkanin nauyin da Allah (SWT) ya dora ma ka, Allah (SWT) ya zaunar da wannan jihar Kastina da Nijeriya 🇳🇬 lafiya alfarmar Annabi Muhammad (SAW).

Mai girma gwamna, ba ni da wata hanyar da zan iya anfani da ita na ba ka tawa gudunmuwa sai wannan ta rubutu a wannan Kafar Sadarwa ta Zamani, shi ya sa kullum idan na fahimci wani abu dake bukatar kulawar gaggawa ni ke anfani da wannan hanya mafi sauki a guri na domin ba da tawa shawara gare ka, ina mai fatan wannan wasika ta wa ta isa gare ka, ka kuma duba ta da idon basira domin kawo sauyi na alkhairi a cikin Hukumomin Tsaron wannan jihar

To k**ar yanda na sani, tabbas mai Girma Gwamna koda yaushe ƙofar sa a buɗe take wajen sauraron koken al’umma, to muna kira ga mai Girma Gwamna da yayi dukkanin mai yiwuwa wajen tausayawa talakawa, ta hanyar bin duk wata hanya da ta dace

A ƙarshe ina roƙon Allah (S.W.T) Ya albarkaci wannan Jiha tamu, ya kuma cigaba da azurta mu da shugabanni nagari, masu ilimi da dattako.

Nagode

Daga:
Abubakar S Malumfashi

BUƊADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI GIRMA CHAIRMAN NA KARAMAR HUKUMAR MALUMFASHI ALH. (HON). MAHARAZU ADAMU DAYI (WAZIRIN AIYU...
08/08/2023

BUƊADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI GIRMA CHAIRMAN NA KARAMAR HUKUMAR MALUMFASHI ALH. (HON). MAHARAZU ADAMU DAYI (WAZIRIN AIYUKAN GALADIMAN KATSINA)

Assalamu Alaikum Warahamatullah Wabarakatuh.

Zan fara buɗe wannan wasiƙa tawa da kalamai na yabo da kuma godiya ga Allah (S.W.T), tsira da amincin da ɗaukaka su ƙara tabbata ga shugaban manzanni, cik**akin Annabawa, wato fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (S.A.W) da ahalinsa da sahabban sa, da kuma mu sauran al'ummar sa da muka biyo bayan
Ina shaidawa babu abin bautawa bisa cancanta sai ALLAH, kuma Annabi Muhammad (S.A.W) BawanSa ne, kuma ManzonSa ne.

Bayan gaisuwa mai cike da karamci da girmamawa zuwa gareka ya mai girma chairman na karamar hukumar malumfashi.

Ranka ya dade, a koda yaushe mukan yi kokari mu sanar da gwamnati cewar akwai matsala da take addabar mutane domin a dauki mataki, Wanda ya shafi al'ummar mu, don yanzu haka mutane na cikin wani hali bayan tsadar rayuwa da tsadar kayan Masarufi wanda jiki baya samun isasshen kayan gina jiki.

Ranka ya dade, sai kuma gashi an wayi gari da wani rashin lafiya da ya zama hantsi leka Gidan kowa, duk inda ka leka k**a daga asibiti zuwa chemist duk al'ummar mu ce ke layi don neman magani, wanda rashin lafiyar nan cashi 70 cikin 100 bata wuce citar cizon sauro, yanzu sauro ya yawaita wanda bai fiye jin magani ba.

Ranka ya dade, muna kira da a tallafawa mutane wajen yin feshin maganin sauro da raba gidan sauro don magance wannan lamari na fama da cutar malaria. Wanda ya shafi kowa da kowa k**a daga kananan yara, mata masu juna biyu, tsofaffi da matasa duk wannan cutar bata bar kowa ba, kuma mun san yadda gwamnati tasan illar cizon sauro da abin da yake haifarwa, feshin maganin sauron nan zai taimaka ya rage ko ya kashe
sauron da wasu kananan kwari da suma suke cizon mutane
sannan su sanya wa yara kuraje da Zarar sun Sosa.

Ranka ya dade wallahi Al'umma mu na cikin wani hali na rashin lafiya wanda mafi yawa cutar cizon sauro ce kowanne asibiti a cike yake da mutane ba lafiya daga yara, Maza, Mata, tsofaffi ta shafi kowa, haka kowanne gida dai-dai ne wanda bayi wannan rashin lafiya ba ga magani tsada, ga yunwa, ga rashin kudi.

Ranka ya dade lallai akwai bukatar gwamnati ta bada gudunmawa wajen yin feshin maganin sauro a karamar hukumar malumfashi lungu da Sako ko an samu Saukin wannan zazzabi, alhakin kune ku taimakawa jama'a.

Ranka ya daɗe, na rubuta maka wannan wasika ne a matsayina na ɗaya daga cikin wanda kake wakilta, akoda yaushe muna kasancewa cikin masu yi maka addu'a da kuma fatan alkhairi. Allah (S.W.T) shaida ne, mu kanmu al'ummar Kamar hukumar malumfashi shaida ne, sannan kuma duniya ma gaba-ɗaya ta shaida da irin namijin ƙoƙarinka da hazaƙarka da kuma yanda kayi aiki tukuru domin dawo da martaba da kuma ƙimar wannan gari namu a idon duniya, tabbas kana daya daga cikin mutanen da wannan gari namu yake alfahari da su a koda yaushe.

To ina fata zaka duba wannan wasika tawa da idanun basira ba tare da duba ƙanƙantar shekaruna ba, sannan kuma a ɗauki duk irin matakin daya k**ata a ɗauka, domin kawo ƙarshen wannan matsala.

Ranka ya dade, haƙƙinku ne a matsayinku na shugabanni ku zama hadimai ga al'ummar ku wajen bayar da kulawa ta musamman da dukkanin wasu buƙatun al’umma na rayuwa. To a yanzu a wannan lokaci da muke ciki al’ummar ƙaramar hukumar ka suna da buƙata ta feshin maganin sauro.

To k**ar yanda na sani, tabbas mai Girma chairman koda yaushe ƙofar sa a buɗe take wajen sauraron koken al’umma, to muna kira ga mai Girma chairman da yayi dukkanin mai yiwuwa wajen tausayawa talakawa, ta hanyar bin duk wata hanya da ta dace.

To muna fatan Allah (S.W.T) Ya sa mai girma chairman zai ji wannan kira, ya kuma ɗauki mataki wajen inganta rayuwar al’ummar ƙaramar hukumar malumfashi.

Allah (S.W.T) ya kawo mana ingantaccen zaman lafiya da kwanciyar hankali mai ɗorewa a wannan yanki namu na katsina da arewa da ma ƙasar mu baki ɗaya.

Nagode

Daga: Abubakar S Malumfashi
08-08-2023-

Maharazu Adamu Dayi
Maharazu Adamu Dayi

Abubakar S Malumfashi ne yayi Wannan Rubutun

BUƊADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI GIRMA GWAMNAN JIHAR KATSINA JAGORAN TALAKAWA ALH. (DR). UMAR DIKKO RADDAAssalamu Alaikum W...
08/08/2023

BUƊADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI GIRMA GWAMNAN JIHAR KATSINA JAGORAN TALAKAWA ALH. (DR). UMAR DIKKO RADDA

Assalamu Alaikum Warahamatullah Wabarakatuh.

Zan fara buɗe wannan wasiƙa tawa da kalamai na yabo da kuma godiya ga Allah (S.W.T) tsira da amincin da ɗaukaka su ƙara tabbata ga shugaban manzanni, cik**akin Annabawa, wato fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S.A.W) da ahalinsa da sahabban sa, da kuma mu sauran al'ummar sa da muka biyo bayan su
Ina shaidawa babu abin bautawa bisa cancanta sai ALLAH, kuma Annabi Muhammad (S.A.W) BawanSa ne, kuma ManzonSa ne.

haƙiƙa siyasa tana nufin zamantakewar al'umma cikin ƴanci da adalci, siyasa wikilci ce na zaɓi a tsakanin al'umma domin samar da yarda da amana Duk wani shugaba da aka zaɓa a siyasa a matsayin jagora ko wakili, to fa ba zaman kansa yake yi ba, tun da ba shi ya zaɓi kansa ba, yardar al'ummarsa ce ta zaɓe sa.

Wannan makaranta Federal University of Health Science and Technology Malumfashi, Tabbas idan har aka gina wannan makarantar a cikin garin malumfashi hakan zai ba garin gagarumin cigaba, tabbas Ilimi shine gishiri na rayuwa kuma shine harsashi na gina duk wata al'umma.

Ranka ya dade, haƙƙinku ne a matsayinku na shugabanni ku zama hadimai ga al'ummar ku wajen bayar da kulawa ta musamman da dukkanin wasu buƙatun al’umma na rayuwa. To a yanzu a wannan lokaci da muke ciki al’ummar ƙaramar hukumar malumfashi ba su da wata buƙata ta gaggawa da ta wuce a ajiye kwarya a gurbinta ma'ana dai a gina wannan Makaranta a cikin garin malumfashi, Federal University of Health Science and Technology Malumfashi, Kamar yadda bayanai s**a fito daga gwamnatin tarayya, cewa wannan makarantar za'a ginata ne a funtua zone ne, kuma a cikin garin malumfashi k**ar yadda bayanai s**a fito daga gwamnatin tarayya.

Ranka ya daɗe, na rubuta maka wannan wasika ne a matsayina na ɗaya daga cikin wanda kake wakilta, akoda yaushe muna kasancewa cikin masu yi maka addu'a da kuma fatan alkhairi. Allah (S.W.T) shaida ne, mu kanmu al'ummar Kamar hukumar malumfashi shaida ne, sannan kuma duniya ma gaba-ɗaya ta shaida da irin namijin ƙoƙarinka da hazaƙar da wasu daga cikin wakilai masu kishin wannan gari da s**a tsaya-tsayin daka babu dare babu rana domin ganin cewa malumfashi ta Samu wannan makaranta kuma idan akayi aiki tukuru domin kawo mana wannan makaranta a cikin garin malumfashi hakan zai dawo da martabar da kuma ƙimar wannan gari namu a idon duniya.

Ranka ya dade to ina fata zaka duba wannan wasika tawa da idanun basira ba tare da duba ƙanƙantar shekaruna ba, sannan kuma a ɗauki duk irin matakin daya k**ata a ɗauka, domin kawo ƙarshen wannan matsala.

To muna fatan Allah (S.W.T) Ya sa mai girma gwamna zai ji wannan kira, ya kuma ɗauki mataki na gaggawa wajen inganta rayuwar al’ummar ƙaramar hukumar malumfashi.

Allah (S.W.T) ya kawo mana ingantaccen zaman lafiya da kwanciyar hankali mai ɗorewa a wannan yanki namu na Kastina da arewa da ma ƙasar mu baki ɗaya.

A ƙarshe ina yi maka addu'a da fatan alkhairi, Allah (S.W.T) Ya kara maka lafiya da ingantacciyar rayuwa mai albarka.

Nagode.

Daga: Abubakar S Malumfashi
07-08-2023.

Abubakar S Malumfashi ne yayi Wannan Rubutun

09/07/2023

RUNDUNAR YAKIN KARE HAKKIN GARIN MALUMFASHI NA A AJE JAMI'AR TARAIYA A MALUMFASHI ZUWA WAJEN GWAMNA RADDA

1. Senator Bello Mandiya
2. Fmr Rep Babangida Talau
3. Chairman Maharazu Dayi
4. Galadima Justice Sadiq Mahuta
5. Malumfashi Foundation
6. Dan' Iya Shehu Musa Dankano
7. Alh Yakubu Jibrin
8. Alh Zaiyana Mahuta
9. Alh Hussaini Mahuta
10. Wakillin Kunguyoyin Dalibai ta Mfashi
11. Shugaban Yan Kasuwa Mfashi
12. Engr Muntari Sagir
13. Danejin Katsina
14. DuklanTsoffin Chairmen na Mfashi; Andaje, Danyari, Ammani, Shawai, Ibrahim Sallama
15. Shugaban Majalisar Kansilomi mai ci Mfashi
16. Wakilin Tsoffin Kansulolin Mfashi
17. Shuwagabannin Siyasar Malumfashi

NB:

A). Malunfashi Foundation (Akh Yakubu Wada) ta fara yunkurin shirya wannan ziyara zuwa wajen Gwamna cikin satin nan (Asabar ko Lahadi) - domin Gwamna na shirin zai rubuta takarda Federal Ministry of Education bukatar relocating Jami'ar zuwa garin Funtua

B). Masu son kwace Jami'ar sunyi alkawarin zasu bada matsugunni na wuccin gadi ma Jami'ar a garin Funtua, saboda haka sai mun matsa kaimi.

ABUN FADAWA GWAMNA:

* Roko ga Gwamna Radda yayi adalci , ya kiyaye abinda doka ta zartar

* Abar mana hakkin mu na kafa Jami'ar Medical Science and Bio Medical Technolgy a Malumfashi k**ar yadda dokar Majalisar kasa ta zartar a shekarar 2022- (SB 678)

* Funtua su jira tasu Jam'iar wadda Senator Bello Mandiya ya nema University of Science and Technology - itama na nan take.

* Malumfashi ce fuska, kuma hedikwata ta Masarautar Katsina a Katsina ta Kudu. Galadima na cikkn manyan Hakimai guda 4 masu nada Sarkin Katsina

* Akwai issassun wurare a Mamumfashi da za'afara karatu kafin samun mazaunin na dindin ma Jami'ar - misali ; Day Danrimi ko Unity School ko Midwifery ko Tunau Primary ko Tsohuwar LG Sakatariya - na wuccin gadi kafin gina wuri na din din din
Shehu Musa Shera

18/06/2023

*KWANAKI GOMAN FARKO NA ZHUL HIJJAH*

🔗 Manzon Allah SAW ya ce; "Babu wasu ranaku da aikata wani aiki mai kyau ya fi soyuwa a wurin Allah sama da wadannan kwanaki goman, sai sahabbai s**a ce ya Manzon Allah har jihadi bai kai suba?? Sai manzon Allah ya ce eh har jihadi bai kai su ba, sai dai kadai mutumin da ya fita shi da dukiyarsa sannan ba abunda ya dawo daga cikinsu (dukiyar ta kare shima an kasheshi a filin yaƙi) -Sahih Tirmizi

🌾Tanbihi:

Kada ka/ki wasa cikin wannan kwanaki 10 masu zuwa, wajen yawaita ayyukan da'a ma Allah.

Mu yawaita karanta Al-qurani da sauran zikiri, da azumi da Sadaka da tausayawa masu rauni da Ciyarwa da Sallan dare, da sada zumunta (ziyara)da watsa ilmi tsakanin mutane da sauran ayyuka alkhairi.

Allah Ta'ala ya taimake mu.

Sauran   2 da Wasu mintuna ya rage Faduwar Rana a  , inda za mu ji Labarin Sanar da Ganin   Watan  .Ga Hoton yadda Jinji...
18/06/2023

Sauran 2 da Wasu mintuna ya rage Faduwar Rana a , inda za mu ji Labarin Sanar da Ganin Watan .

Ga Hoton yadda Jinjirin Watan din zai Kasance Bayan Faduwar Rana a Saudiyya.

JAMI’AR KIMIYAR LAFIYA TA GWAMNATIN TARAYYA.Yankin funtua zone yanki ne Wanda ya kunshi kananan hukumomi guda goma shada...
18/06/2023

JAMI’AR KIMIYAR LAFIYA TA GWAMNATIN TARAYYA.

Yankin funtua zone yanki ne Wanda ya kunshi kananan hukumomi guda goma shadaya ;Funtua,dandume,bakori,danja,malumfashi,kafur,faskari,kankara,sabua,Musawa da matazu.

Duk fadin kananan hukumomin nan babu karamar hukuma data mallaki ordinary national diploma ballantane A*o maganaar jami’a Dukda irin gudumuwar da yankin ya dade yanabayarwa wajen kafa gwamnatoci da dama Tunda aka kirkiri jihar katsina.

Yankin katsina central ya mallaki makarantu k**ar haka;
1)yar’adua university✅
2)Alqalam uni katsina ✅
3)Federal university dutsinma✅
4)Isa kaita college of education ✅
5)Hassan usman polytechnic katsina✅

Yankin Daura zone ya mallaki makarantu k**ar haka;
1)uni of transport Daura✅
2)federal polytechnic Daura ✅
3)Iro kankia scool of health kankia✅
4)school of legal nd islamic studies Daura ✅
Dss

Yankin funtua zone
1)university 0❎❎
2)polytechnic 0❎❎
3)College of education 0❎❎

Tabbas idan anaso ayi adalchi yak**ata akawo wannan jami’ar a yanki funtua zone.

Shin ko FUNTUA ZONE BATA ACIKIN JIHAR KATSINA NE?

TAMBAYA DAGA
SANI YARO TSIGA

KATSINA STATE Justice For KARADUA ZONE In Dai Ba Kabilanci Da Sonkai Da Son Zuciya Za'a Nunawa Funtua Zone Ba To Maganar...
18/06/2023

KATSINA STATE

Justice For KARADUA ZONE In Dai Ba Kabilanci Da Sonkai Da Son Zuciya Za'a Nunawa Funtua Zone Ba To Maganar Gaskiya Wannan Makaranta Funtua Zone Yak**ata Akawota Don Duk Wanda Yakaita Inda Ba Funtua Zone Ba Billahillazi Shi Makiyin Allah Ne Kowaye Shi Kuma Baison Cigaban Talakawa.

GABAYANIN MAKARANTA KU MASU RUWA DA TSAKI INMA BAKUSANIBA ATUNATAR DAKU MANYAN FUNTUA ZONE YANZU ZAMU GANE CEWA INKUNA KISHINMU

Akwai sabuwar jam'iar gwamnatin tarayya mai suna FEDERAL UNIVERSITY OF HEALTH SCIENCES da akayi approving zaayi a jihar Katsina har an fara bada appointment letters ga non academic staff.

Muna kira ga manyan mu, da duk wanda zai iya bada gudunmuwa da mu tashi tsaye wajen ganin Funtua ta samu wannan cigaba. Mudai a matakin mu, muna iya abinda zamu iya, dafatan Allah yai mana jagoranchi, Ya bamu nasara.

G Fresh Allah Ya Baku Zuri'a Ɗayyiba ku haifo Mutane k**ar Adam A Zango da Ado Gwanja ~ Abokin Ango Babban Abokin Ango G...
18/06/2023

G Fresh Allah Ya Baku Zuri'a Ɗayyiba ku haifo Mutane k**ar Adam A Zango da Ado Gwanja ~ Abokin Ango

Babban Abokin Ango G Fresh Al'Amin Kano State Material Aminu G Town ya bayyana jin dadin sa game da Auren G Fresh da Sadiya Haruna.

A cewar sa Auren Sadiya da Ga Fresh yayi Ni gani nake k**ar jihadi ne kuma ya k**ata a bashi babbar kyauta.

Roƙona a gare ku shine ku rike juna da amana, Allah ya baku zaman lafiya, ku haifo mutane irin su Adam A Zango, da Ado Gwanja, da Hamisu Breaker da Mustapha Naburaska, ina nufin kwarya tabi kwarya.

Sannan ina rokon Sadiya Haruna tunda itace mai gidan, dan Allah kada ta sakar mana aboki, ta rike shi da kyau su zauna lafiya.

~ Cewar Abokin G Fresh Aminu G Town

© AMINTACCIYA

Address

Malumfashi

Telephone

+2348137180558

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Malumfashi Reporters:

Videos

Share


Other Media/News Companies in Malumfashi

Show All