29/08/2023
28-August- 2023
BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI GIRMA GWAMNAN JIHAR KATSINA (DR) UMAR DIKKO RADDA, DANGANE DA MATSALAR TSARO DA TAKAITA HAWA BABUR DA KEKE NAPEP A WASU SASSAN JIHAR KATSINA.
(The governor of Kastina state)
Assalamu alaikum-warahamatullahi’ta’alah’ wabarakatuhu, bayan gaisuwa irin ta Addinin Musulunci tare da girmamawa a gare ka a matsayinka na tsanin al’ummar jihar Kastina a ciki har da ni mai wannan rubutu, ina mai anfani da wannan dama a wannan kafar sadarwa ta zamani na isar ma ka da tawa shawara a matsayi na Wanda kake wakilta a karkashin jagorancinka, wanda ni din ba kowa ba ne face Dan jihar Kastina mai kishi da fatan ganin wannan jihar tamu ta samu maslaha
Tare da girmamawa da mutuntawa a gare ka a matsayinka na wanda Allah (SWT) ya dorawa amanar al’ummar wannan jihar, ina rokon Allah (SWT) ya cigaba da shiga cikin wannan Jagoranci na ka, Allah (SWT) ya yi ma ka gudunmuwa gurin sauke nauyin da Allah (SWT) ya dora ma ka na al’ummar wannan jihar.
A matsayinka na gwamana, mai gaskiya da rikon amana, Dan-kishin jihar Kastina Jagoran wannan jihar ta katsina, wanda Allah (SWT) ya baiwa cikakkiyar amanar kula da tsaro da rayuwar al’ummar jihar Kastina da daukacin jihohi (36) da Babban Birnin jihar Kastina.
Mai girma gwamna, tsokaci akan dokar hana hawa mashin da Keke napep a wasu
Sassan jihar Kastina
domin yin kira da nuni akan sake dawo da dokar takaita hawa mashin da Keke napep a wasu sassa na jihar ita dai wannan doka anyi ta a baya amma ba ta yi tasiri ba illa ma kara jefa masu amfani da wannan lokutan dan samun abinci cikin kunci da wahala
Mai Girma gwamna, mutane suna ganin cewa koda yake saka dokar dalilin tsaro yanada amfani, amma kuma lokachin da aka sanya yayi kadan, da haka Muke rokon gwamnati ta sake duba wannan dokar ta maida ta zuwa Karfe goma (10) maimakon karfe bakwai (6) da dokar ta ayyana
Ko kuma a janye dokar baki daya a lalubo wata sabuwar hanya domin magance matsalar tsaro
Muna fatan gwamnati zata duba korafe korafen Al'umma wajen sake nazari akan wannan sabuwar dokar
A matsayi na haifaffen garin malumfashi, Dan asalin jihar Kastina, Almajiri, talaka da ba kowa ba, ina mai anfani da wannan dama na bayar da tawa shawara zuwa gare ka, akan matsalar tsaron jiharmu ta Kastina, k**ar yadda Sashe na talatin da tara (Section 39) na Kundin Tsarin Mulkin wannan Kasa 🇳🇬 ya ba ni iko da damar tofa albarkacin baki na akan al’amurran da s**a shafi jiha ta, ko kuma wannan kasa ta mu.
Ya mai girma gwamna, da son samu na ne na isar da wannan muhimmin sako zuwa gare ka daga ni sai kai, amma ba ni da irin wannan damar a yanzu, shi ya sa na zabi wannan hanyar ta rubutu a wannan kafa, domin isar da sako na gare ka.
duk wata Gwamnati da ta tabbatar da cewa tana kishi da tausayin talakawa, to tana fara yin tunani ne akan halin da su talakawan za su kasance, kafin ta zartar da wata doka a kan su
Sometimes na kan tambayi kaina, shin wai shuwagabanninmu basu da labarin halin da mu talakawa masu qaramin qarfi muke ciki ne? kawai ku saka doka ba tare da kun san irin abin da dokar zata janyo ba babu laifi ku saka doka amma is good ace kun fito da wasu hanyoyin da talakawa zasu samu sauki.
Tabbas harkar tsaro a qasa ko a jaha babban barazana ce ga al'umma, to amma bai dace a mayar da hanyoyin kawo gyara masu tsauri irin haka ba, ku duba waccen tsohuwar gwamnati a karkashin Jagoranci Mai girma tsohon gwamnan jihar Kastina His excellency, hon Aminu bello masari har network na kusan tsawon sati biyu ko watanni aka yanke mana, ta dalilin haka mutane da yawa sun shiga wani hali na qunci, musamman 'yan kasuwa, amma bayan dawowar network din harkar tsaro Babu Wani Cigaba da aka samu 😭
Mai girma gwamna, ina mai anfani da wannan dama na bayar da tawa shawara zuwa gare ka akan matsalar tsaron da ta addabi wannan jihar Kastina a matsayi na ba kowa ba, Dan Kasa na gari mai kwanciya da tashi da bakin cikin halin da al’ummar wannan Kasa musamman mutanen Karkara suke ciki.
Mai Girma gwamna, ina ganin matsalar tsaron wannan jihar ba karancin mak**ai ba ne ke haifar da chikas ba, a nawa tinani a da karamar fahimta, manyan matsalolin da ke haifar da tangarda a fagen aikin Jami’an Tsaron Nijeriya bai fi k**ar haka ba.
• Karancin Jami’an Tsaro ba.
• Karancin hanyoyin sadarwa ba.
• Rashin baiwa Jami’an Tsaro cikakkun hakkokinsu.
1• Mai girma gwamna, a cikin wannan jihar tamu ba ko ina ke da (Network) din kiran wayar hannu ba, galibin guraren da yan ta’adda ke fakewa a cikin wannan jihar babu (Network) na kiran waya, galibin al’ummar da suke kaiwa farmaki mutanen Karkara ne da babu (Network) din kiran waya a garuruwansu, saboda haka akwai bukatar a samar ma Jami’an Tsaron Yan-sandan ingantattun hanyoyin sadarwa irin na zamani wadan da kowane Jami’in Dan sanda zai iya magana da Dan-uwansa a katsina misali:
• A jiha ya zama kowane (CP) idan ya yi magana 📱 ya zama kowane (DPO) yana karbar sakon (CP) kai tsaye musamman umurnin ko ta kwana.
• (DPOs) idan su ka yi magana a yankunan da suke kula da su, kowane Jami’in tsaron Dan-sanda dake karkashin Jagorancinsu yana rike da wayar hannu 📱 da zai ji wannan umurnin kai tsaye.
2• Mai girma gwamna akwai bukatar a inganta rayuwar Jami’an Tsaron wannan jihar da Iyalansu, domin mutane ne k**ar kowa, amma s**a aminta s**a yarda su bayar da lokacinsu, lafiyarsu da rayuwarsu domin kare kima da mutuncin wannan jihar ta mu da al’ummar cikinta.
Mai girma gwamna, da an dauki wadannan matakai ina ganin babu maganar cin hanci a wannan jihar, babu maganar gudu ko ja da baya a fagen yaki da yan ta’adda masu yinkurin kawo ma wannan jihar tangarda.
Mai girma gwamna, wallahi al’ummar jihar Kastina muna cikin mawuyacin hali na rashin tsaro, domin babu ranar da ba a yi masu kisan gilla a gidajensu, a gonakinsu, akan hanyarsu ta zuwa neman abinci, al’amarin kullum kara rinchabewa yake yi, Jami’an Tsaro suna yi iya bakin kokarinsu, domin su ma mutane ne k**ar kowa, na san kana samun rahotannin dik halin da al’ummar wannan jiha ta Kastina suke ciki, kuma a matsayinka na (gwamna) mai gaskiya da rikon amana na san ka san abunda ake kira da tsaro.
Mai girma gwamna, babu shakka na san kana iya bakin kokarin ka na daukar matakan da s**a dace, domin magance wannan musiba ta rashin tsaron jihar Kastina baki dayanta, amma akwai bukatar ka chanza salon yaki da wadannan mutane masu yinkurin rusa wannan jihar ta mu.
Mai girma gwamna, a tarihin yake yake na duniya, babu inda wata Kasa ko al’umma su ka taba shiga yaki, s**a samu cikakkiyar nasara ba tare da sun hada kawunansu a guri daya ba, haka zalika babu inda wata Kasa ko al’umma ta shiga yaki a cikin gidanta akwai matsalar rashin hadin kai kuma ta samu nasara.
Mai Girma gwamna, akwai bukatar ka kira taron gaggawa na masu ruwa da tsaki daga jihar Kastina, k**a daga Dattawa, Shuwagabanni, Malaman Addinin Musulunci, Sarakuna, yan-siyasa, yan kasuwa, Mata da Matasa babu maganar Jam’iyyar APC ko PDP, domin sai al’umma na zaune lafiya, rayuwa tare da dukiyoyin su ake maganar siyasa ko Jam’iyyar siyasa, ka nemi su hada kawunansu a guri daya, ka roke su wanda ke gaba da wani kowa ya yafewa kowa, kowa ya bayar da shawararsa, domin yakar wannan musiba ta rashin tsaro a jihar Kastina.
Mai girma gwamna, ina mai ba ka tabbacin idan Allah (SWT) ya ba ka ikon anfani da wannan shawara ta wa, babu shakka za ka ga alfanunta, kuma da izinin Allah (SWT) za a samu cikakkiyar nasarar yakar wannan musiba ta rashin tsaro a wannan jiha ta katsina.
Mai girma gwamna, ina yi ma ka fatan alkhairin samun cikakkiyar nasarar ganin bayan dikkanin matsalolin tsaron wannan jihar mu, Allah (SWT) ya cigaba da k**a ma ka, Allah (SWT) ya kara ma ka lafiyar da za ka sauke dikkanin nauyin da Allah (SWT) ya dora ma ka, Allah (SWT) ya zaunar da wannan jihar Kastina da Nijeriya 🇳🇬 lafiya alfarmar Annabi Muhammad (SAW).
Mai girma gwamna, ba ni da wata hanyar da zan iya anfani da ita na ba ka tawa gudunmuwa sai wannan ta rubutu a wannan Kafar Sadarwa ta Zamani, shi ya sa kullum idan na fahimci wani abu dake bukatar kulawar gaggawa ni ke anfani da wannan hanya mafi sauki a guri na domin ba da tawa shawara gare ka, ina mai fatan wannan wasika ta wa ta isa gare ka, ka kuma duba ta da idon basira domin kawo sauyi na alkhairi a cikin Hukumomin Tsaron wannan jihar
To k**ar yanda na sani, tabbas mai Girma Gwamna koda yaushe ƙofar sa a buɗe take wajen sauraron koken al’umma, to muna kira ga mai Girma Gwamna da yayi dukkanin mai yiwuwa wajen tausayawa talakawa, ta hanyar bin duk wata hanya da ta dace
A ƙarshe ina roƙon Allah (S.W.T) Ya albarkaci wannan Jiha tamu, ya kuma cigaba da azurta mu da shugabanni nagari, masu ilimi da dattako.
Nagode
Daga:
Abubakar S Malumfashi