Arewa page

Arewa page arewapage

ilimantarwa

fadakarwa

nishadantarwa

03/08/2020

Mukoyi turanci kashi na (1)

Gwajin idoNumber nawa ne a nan
12/07/2020

Gwajin ido
Number nawa ne a nan

15/06/2020

FALALAR ZIKIRI

Allah Madaukakin Sarki ya ce:
فَاذْكُرُونِي أَذْكُرْكُمْ وَاشْكُرُواْ لِي وَلاَ تَكْفُرُونِ
Fazkuriniy Azkurkum Washkuruliy Wala Takfuruni.
Ku ambace ni zan ambace ku, ku gode mini kada ku butulce mini" [Bakara, aya ta 152].
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اذْكُرُوا اللَّهَ ذِكْراً كَثِيراً
Ya'ayyuhallazina Amanuzkurullaha Zikran Kathiran.
Ya ku wadanda s**a yi imani ku ambaci Allah ambato mai yawa". (Ahzab aya ta 41).
وَالذَّاكِرِينَ اللَّهَ كَثِيراً وَالذَّاكِرَاتِ أَعَدَّ اللَّهُ لَهُم مَّغْفِرَةً وَأَجْراً عَظِيماً
Wazzakirinallaha Kathiyran Wazzakirati A'addanlahu Lahum magfiratan Wa'ajran Aziyman.
Da masu ambaton Allah da yawa maza, da masu ambatonsa mata, Allah ya tanadar musu gafara da lada mai girma". [Ahzab, aya ta 35]
وَاذْكُر رَّبَّكَ فِي نَفْسِكَ تَضَرُّعاً وَخِيفَةً وَدُونَ الْجَهْرِ مِنَ الْقَوْلِ بِالْغُدُوِّ وَالآصَالِ وَلاَ تَكُن مِّنَ الْغَافِلِينَ
Wazkurrabbaka Fiy Nafsika Tadarru'an Wakhiyfatan waduwanaljahri Minal kawli Bil'guduwi Wal'asali Walatakun Minalgafiliyna.
Kuma ka ambaci Ubangijinka a cikin zuciyarka, kana mai kankan da kai da tsoro, ba da daukaka murya ba (saka-tsaki) tsakanin asirtawa, da bayyanawa, da safe da marece, kuma kada ka zamo daga cikin gafalallu". [A'araf, aya ta 205].
Kuma Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; "Misalin wanda yake ambaton Ubangijinsa da wanda ba ya ambaton Ubangijinsa, k**ar misalin rayayye da matacce ne". (Duba Sahihul Bukhari tare da Sharhinsa Fat'hul Bari (11/208). Muslim ya rawaito shi da lafazin; 'Misalin gida da ake ambaton Allah a cikinsa, da wanda ba a ambaton Allah a cikinsa k**ar misalin rayayye ne da matacce". (1/539).)
Kuma ya ce: "Shin ba na ba ku labarin mafi alherin ayyukanku ba, kuma mafi tsarkinsu a wajen Srkin da yake mallakar ku, kuma mafi daukakarsu ga darajojinku, kuma mafi alheri gare ku daga ciyar da zinariya da azurfa kuma mafi alheri gare ku da ku hadu da abokan gabanku ku rika dukan wuyayinsu, suna dukan wuyayinku? S**a ce ka ba mu labari. Ya ce: Ambaton Allah Madaukaki". (Tirmizi (5/459), da Ibn Majah (2/1245). Duba Sahih Ibn Majah (2/316). Da Sahihul Tirmizi (3/139).)
Kuma ya ce: "Allah madaukaki yana cewa: Ni ina tare da zaton bawana da ni, kuma ina tare da shi idan ya ambace ni idan ya ambace ni. Idan ya ambace ni a cikin ransa zan ambace shi a cikin raina, idan ya ambace ni a cikin jama'a zan ambace shi a cikin jama'ar da ta fi su alheri, in ya kusance ni taki daya zan kuance shi tsawon gaba guda, in ya zo min ya na tafiya zan zo masa ina gaggawa".( Bukhari (8/171), da Muslim (4/2061). Lafazin ruwayar na Bukharine.)
Daga Abdullahi Ibn Busr, Allah ya yarda da shi, ya ce; Ya Ma'aikin Allah! Shari'o'in Musulunci sun yi yawa a gare ni, saboda haka ka nuna wani abu da zan yi riko da shi. Ya ce: "Ku harshenka ya gushe face yana danye daga ambaton Allah". (Tirmizi (5/458). Da Ibn Majah (2/1246). Duba Sahihul Tirmizi (/139), da Sahih Ibn Majah (2/317).)
Kuma mai tsira da amincin Allah yace; "Wanda ya karanta harafi daya daga littafin Allah yana da (ladan) kyakkyawan aiki daya saboda shi, kuma dukkan kyakkyawan aiki daya yana da (ladan) misalinsa goma. Ba ina cew Alif Lam Mim harafi ba ne. A'a, Alif harafi ne, Lam harafi ne, Mim harafi ne".( Tirmizi (5/175) Duba Sahihul Tirmizi (3/9), da Sahihul Jami'us Sgir (5/340).)
Kuma daga Ukbata ibn Amir, Allah ya yarda da shi, ya ce; "Manzon Allah tsira da aminci su tabbata a gareshi, ya fito alhali muna cikin rumfa, sai yace; "Wane ne daga cikinku zai so ya fi kullum da safe zuwa koramar Budhan ko Akik, ya dawo da taguwa biyu masu manyan tozuna, ba tare da yin wani laifi ba ko yanke zumunta?" Muka ce: muna son haka. Ya ce; "Dayanku ya je masallaci ya nemi sani, ko ya karanta ayoyi biyu daga cikin littafin Allah Mabuwayi Mai Daukaka, ya fi masa taguwa biyu, ayoyi uku sun fi masa taguwa uku, ya fi masa taguwa biyu, ayoyi uku sun fi masa taguwa uku, ayoyi hudu sun fi masa taguwa hudu, da kwantankwacin adadinsu na rakuma". (Muslim (1/553)

04/06/2020
03/06/2020

Allah ya kara tona asirin azzalimai

NASIHA: Ba Zagin Shugabanni Ne Maslaha Gare Mu BaDaga Comr Abba Sani PantamiIna mamakin halayyarmu mu 'yan arewa, da zar...
23/05/2020

NASIHA: Ba Zagin Shugabanni Ne Maslaha Gare Mu Ba
Daga Comr Abba Sani Pantami
Ina mamakin halayyarmu mu 'yan arewa, da zaran an samu mas'ala guda shike nan sai ka yi ta jin ana ta zagin shugabanni, ba ma tsayawa mu duba menene ya jawo sanadin samun matsalar, ta wace hanya za a bi domin a samu a shawo kan matsalar, kada hakan ta sake faruwa!!
Amma duk babu wannan tunanin a ranmu, yawan cin sai yan kadan daga cikin mu, muna da karancin hakuri da zarbabiya kan al'ummar mu, mu tsaya mu yi ta zagin shugabanninmu hakan fa ba shine zai kawo mana mafita ba, illa ma ya jawo mana wata fitina ta daban da Allah ka iya jarabar mu kuma mu sha wahala cikinta.
Sanarwar rashin ganin wata an riga da anyi, duk da an samu rahotonnin ganin watan a wasu sassan arewa cin Nijeriya, hakan ba ya rasa nasaba da rashin Isar da sakon nin ganin watan zuwa ga Sarkin musulmi ta hanyar da ya dace, idan kuka yi duba da sanarwar da ya fitar a jiya da dare.
Idan kuskure aka yi ma an riga da anyi shi, idan daidai ma aka yi shima duk an riga da anyi, kawai abunda ya k**ata a gare mu muyi ta addua, Allah Ubangiji ya karbi ibadunmu bawai mu zo soshiyal midiya mu yi ta zage-zage ba, wannan ba tarbiyar koyarwar addinin musulunci ba ce, don Allah 'yan uwa na al'ummar musulmi mu kiyaye zagin shugabanninmu.
Muna rokon Allah Ya karba mana ibadunmu. Amin

DA DUMIDUMINSA: 'Yan Sanda Sun Gayyaci Sheik Sani Khalifa Zaria Bayan Ya Jagoranci Sallar IdiDaga Aliyu AhmadDuk da cewa...
23/05/2020

DA DUMIDUMINSA: 'Yan Sanda Sun Gayyaci Sheik Sani Khalifa Zaria Bayan Ya Jagoranci Sallar Idi
Daga Aliyu Ahmad
Duk da cewa Malamin ya bi umarnin da gwamnati ta bayar na cewa kowa ya yi sallah a gida, amma kasancewar Malamin yana da almajirai da iyalai da dama hakan ya sa jama'a sun samu halartar sallar duk da cewa a gidansa dake Zaria aka gudanar da sallar.
Rahotanni sun tabbatar da cewa bayan idar da sallar ne sai ga jami'an 'yan sanda sun dira gidan malamin, inda s**a ce masa ana gayyatarsa zuwa ofishinsu.
Saidai wasu daga cikin wadanda s**a halarci sallan sun fusata, inda s**a ki yarda a tafi da Malamin daga bisani aka fitar da malamin ta barauniyar hanya domin ya je amsa gayyarar da 'yan sandan s**a yi masa.
Saidai a yayin da 'yan sandan s**a zo, Sheik Sani Khalifa ya tambaye su ko an turo su ne su k**a shi, sai s**a ba shi amsa da cewa ai ya fi karfin su saka shi a mota su tafi da shi saidai ya zo da kansa.

Yadda Aka Cika Makil A Yayin Sallar Idin Da Sheik Dahiru Bauchi Ya Jagoranta A Safiyar Yau A Gidansa Dake Jihar Bauchi.m...
23/05/2020

Yadda Aka Cika Makil A Yayin Sallar Idin Da Sheik Dahiru Bauchi Ya Jagoranta A Safiyar Yau A Gidansa Dake Jihar Bauchi.
menene ra'ayin ku

Wata kotu a Abuja, babban birnin Najeriya, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya a kan Maryam Sanda, matar da ta kashe...
27/01/2020

Wata kotu a Abuja, babban birnin Najeriya, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya a kan Maryam Sanda, matar da ta kashe mijinta.

An yanke hukuncin ne bayan gurfanar da matar bisa laifin daba wa mijinta mai suna Bilyaminu Bello wuka a shekarar 2017, sak**akon rikici a tsakaninsu.

A ranar Litinin ne kotun ta yanke hukuncin bayan dage zamanta a ranar 25 ga watan Nuwamba.

Sanar da hukuncin ke da wuya, Maryam ta yi ta kuruwa a zauren kotu.

A baya ta musanta zargin inda ta ce mijin nata ya mutu ne sak**akon rauni da ya samu bayan ya fadi a kan kuttun sh**ha a gidansu.

02/12/2019
09/11/2019

Nigeria ta ba da sharudda kafin ta bude iyakokinta

Hakkin mallakar hotoPIUS UTOMI EKPEI

Gwamnatin Najeriya ta bai wa kasashen da ke kungiyar raya tattalin arzikin Afrika ta yamma, ECOWAS, wasu sharudda, wadanda ta ce dole su cika su, kafin ta bude bakin iyakokinta.

Ministan harkokin wajen kasar, Geoffrey Onyeama, ya bayyana sharuddan wadanda s**a shafi zirga zirgar mutane da kayayyaki ta bakin iyaka, a wajen wani taron kwamitin da ke sa ido kan rufe wasu iyakokin kasar da aka yi a Abuja. Sharuddan su ne:

Najeriya ba za ta yarda a rinka shigo da kayan da aka sauya wa mazubi a makwabtan kasashe ba.

Dole a rushe dukkanin wuraren ajiye kayayyakin da ke bakin iyaka ko kusa da iyakokin Najeriya.

Dole ne a yi wa kayayyakin da za a shigo da su daga makwaftan kasashe rakiya.

Mutanen da ke da fasfo ne kawai za a bari su ketaro cikin kasar.

09/11/2019

Pantami ya ba hukumar sadarwa wa'adin rage kudin data

Hakkin mallakar hotoTWITTER

Ministan sadarwa da harkokin intanet na Najeriya ya bai wa hukumar sadarwa ta Najeriya izinin ta lalubo hanyoyi da za a rage tsadar farashin data a kasar cikin kwana 5.

Ya bayar da wannan umurni ne a lokacin da ya karbi bakuncin tawagar gudanarwar hukumar ta NCC, karkashin jagorancin Senator Olabiyi Durojaiye.

Pantami ya ce yana karbar koke-koke da dama daga al'umma game da tsadar kudin sayen data na shiga intanet a kasar.

09/11/2019

Jihar Kano ta haramta ayyukan gidan-mari



Gwamnatin Kano ta bayar da umurnin rufe gidajen mari da ake da su a fadin jihar har zuwa lokacin da gwamnati ta fitar da tsarin da ya dace na tafiyar da irin wadanna cibiyoyi.

Shugaban kwamitin kula da makarantun tsangayu a jihar Dr Muhammad Tahir Adamu ne ya sanar da daukar matakin, kuma sanarwar da ya fitar ta ce matakin bai shafi makarantun islamiya da na allo ba.

09/11/2019

An zargi Buhari da mayar da Osinbajo saniyar-ware

Kungiyar kabilar Yarbawa ta Afinifere ta zargi shugaba Muhammadu Buhari da kokarin mayar da mataimakinsa Yemi Osinbajo gefe a ayyukan gwamnati, bayan da ya ki mika masa rikon shugabancin kasar a lokacin da zai yi tafiya zuwa Birtaniya.

Wannan zargi ya taso ne bayan da aka kai wa shugaba Buhari dokar hako mai na cikin teku da kan tudu har London domin sanya mata hannu bayan amincewar majalisar dokokin kasar.

An ruwaito mai magana da yawun kungiyar ta Afinifere Yinka Odumakin na cewa nuna wariya ga Yemi Osinbajo wani abu ne da aka tsara.

Sai dai daga baya fadar gwamnatin kasar ta musanta cewa akwai rashin jituwa tsakanin shugaban kasar da mataimakinsa.

Address

Lafia

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa page posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa page:

Videos

Share