Rana24

Rana24 Rana24 Is An Independent And Unbiased Online Newspaper Outlet Under RANA24 MULTIMEDIA AND COMMUNICATION SERVICES. PRODUCTS:
Rana24
Rana24. Katsina Facts.
(1)

WHATSAPP|https://chat.whatsapp.com/I9O0N9NtoDIFetNclKdjxA CALL | 07032340606 JARIDAR RANA24 MULTIMEDIA AND COMMUNICATION SERVICES:
_______________________________________
Rana24 is an independent online newspaper which is outlet of RANA24 MULTIMEDIA AND COMMUNICATION SERVICES. We conduct research and investigations before publish the news in order to develope,promote peace, and report fearlessly

on insecurity and terrorism in Nigeria and Africa. VISION:
To be a best print and online world newspaper. MISSION:
Always to disseminate credible information to the general public. Supreme News. Arewa Plus

E-MAIL:
[email protected]
[email protected]
[email protected]
[email protected]. TEL:
07032340606

15/01/2025

ADDU'AR RANA24
Muna Rokon Ubangiji Ya Dora Mu Kan Tafarkin Gaskiya

ZAƁEN 2027:  Ƴan Nijeriya da kansu za su roƙi Tinubu ya ci gaba da mulki har zuwa 2031 – Jigo a APCAbdulhakeem Alawuje, ...
15/01/2025

ZAƁEN 2027: Ƴan Nijeriya da kansu za su roƙi Tinubu ya ci gaba da mulki har zuwa 2031 – Jigo a APC

Abdulhakeem Alawuje, jigo a jam'iyyar APC, ya bayyana cikakken kwarin gwiwa cewa shugabancin Shugaba Bola Tinubu zai burge ƴan Najeriya har su nemi ya tsawaita wa'adin mulkinsa bayan 2027.

A wata sanarwa ga manema labarai, Alawuje ya yi kira ga 'yan Najeriya da su kasance masu hakuri, yana tabbatar musu cewa wahalhalun da ake fuskanta a yanzu na wucin gadi ne kuma za su sauya zuwa alheri nan ba da jimawa ba.

Ya ƙara da cewa shugabancin Shugaba Tinubu zai kawo gagarumin canji mai kyau, wanda zai sa ƴan Nijeriya su bukaci ya ci gaba da mulki.

"Wannan hasashen ya ta'allaka ne da kyakkyawan sak**akon da manufofin shugaban za su haifar, wanda zai sa ya samu goyon baya da yabo daga kowa.

"Ya k**ata a fahimta cewa maganganu na ka iya zama k**ar hasashe, saboda sun dogara ne da ra'ayi na na kaina da kuma aminta a kan gwamnatin Shugaba Tinubu."

Ba za mu lamunci cin zàrafin bil-adama a jihar Katsina ba --inji Kwamishinan shari'a Barr. Fadila Muhammad |Rana24 Newsp...
15/01/2025

Ba za mu lamunci cin zàrafin bil-adama a jihar Katsina ba --inji Kwamishinan shari'a Barr. Fadila Muhammad |Rana24 Newspaper

Ma'aikatar shari'a ta Jihar Katsina ta fara gurfanar da wadan da aka k**a ana zarginsu da cin zara-fin kananan yara gaban kotu domin su fuskanci hukunci.

Kwamishinar shari'a ta Jihar Katsina Barrister Fadila Kurfi ta bayyana ma 'yan jarida haka jim kadan bayan fitowa daga kotun a babbar kotun Jiha, a ranar talata 14 ga watan Janairu 2024.

Wanda cin za-rafin kànanàn yaran ya shafi yima mata fyade, luwadi da kuma azabtar dasu, kuma wannan mataki da aka dauka a karkashin wani kwamiti na ko ta kwana da Gwamnatin Jihar Katsina ta kafa karkashin ma'aikatar shari'a zai bada damar dakile jan lokaci da shar'un cin zarafin kananan yara keyi ba tare da yanke hukunci cikin lokaci ba, ga wan da ake zargi da laifin aikata irin wannan laifi.

Barrister Fadila Kurfi ta bayyana cewa ya zuwa yanzu sun gabatar da korafin laifin cin za-rafin kànanan yara gaban kotu sama da guda 40.

Kwamitin na kota kwana shi ne zai rika bibiyar shari'ar cikin sauri tare da hukunta duk wanda aka samu da aikata laifin cin zarafin kananan yara ta hanyar fyade, ko luwadi ko azabtar dasu.

Wannan mataki na Gwamnatin Jihar Katsina ya biyo bayan yawaitar samun cin za-rafin kananan yara musamman marasa gata, aci zara-finsu ta hanyar fya-de ko luwa-di.

'Yan ta'addar Boko Haram Sun shiga ChiBok sun Kashe mutane da yawa, ƙone gidaje da coci | Rana24 Newspaper
14/01/2025

'Yan ta'addar Boko Haram Sun shiga ChiBok sun Kashe mutane da yawa, ƙone gidaje da coci | Rana24 Newspaper

Wutar dajin Los Angeles ta haddasa asarar dala biliyan 150 a CaliforniaWasu alƙaluman ƙwararru da ke sanya idanu kan wut...
14/01/2025

Wutar dajin Los Angeles ta haddasa asarar dala biliyan 150 a California

Wasu alƙaluman ƙwararru da ke sanya idanu kan wutar dajin Los Angeles can a jihar California ta Amurka sun nuna yadda adadin ɓarnar da wutar ta haifar kawo yanzu ya iya zarta dala biliyan 150, ninki 3 na asarar da a farko aka yi hasashen wutar za ta haddasa.

Wutar dajin ta fiye da mako guda wadda a baya masana su ka ƙiyasin za ta haddasa asarar dala biliyan 50, tuni s**a sauya matsaya inda ƙwararrun ke cewa tun a yanzu wutar dajin ta haddasa asarar da ka iya zarta dala biliyan 150 a wani yanayi da har yanzun ba a iya shawo kanta ba, lura da yadda ƙaƙƙarfar iskar Santa Ana da ke rarraba wutar zuwa sassa daban-daban ke barazana ga ƙoƙarin da ake na kashe wutar.

Masu aikin kashe gobarar sun bayyana cewa zai iya kai aƙalla kwanaki 3 a nan gaba gabanin iya shawo kan wutar lura da yadda iskar ke mayar da aikinsu baya.

Zuwa yanzu wutar dajin ta hallaka mutane 24 baya ga ƙone kadada dubu 40 a iya yankunan birnin na Los Angeles yayinda ta ƙone kadada dubu 23 a Palisades a wani yanayi da kuma wutar ke barazana ga Brentwood da Encino da kuma Westwood.

A gefe guda mahukuntan na Los Angeles sun ce zuwa yanzu wutar ta ƙone gine-ginen da s**a kai dubu 12 da 300, a wani yanayi da aka kwashe mutanen da yawansu ya kai dubu 92 ake kuma kan hanyar kwashe wasu ƙarin dubu 89.

Ƙwararru a ɓangaren kiwon lafiya na ci gaba da kiraye-kiraye wajen ganin al’ummomin da ke kusa da yankunan da wannan wuta ke ci gaba da ci kan su kaucewa shaƙar hayaƙinta saboda illar hakan ga lafiya.

Tuni da aka samar da asusun tallafawa waɗanda wannan ibtila’i ya shafa, galibinsu waɗanda s**a rasa muhallansu da dukkanin abin da s**a mallaka.
Rfi

Katsina Ta Gudanar da Taron Tattaunawa Don Bunkasa Fitar da Kayan kasuwanci zuwa kasashen Ketare Katsina City News Gwamn...
14/01/2025

Katsina Ta Gudanar da Taron Tattaunawa Don Bunkasa Fitar da Kayan kasuwanci zuwa kasashen Ketare

Katsina City News

Gwamnatin Jihar Katsina, ta hannun Hukumar Kula da Zuba Jari ta Jihar Katsina (KIPA), karkashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umar Radda, ta shirya taron yini guda domin karfafa masu fitar da kaya zuwa kasashen waje. Taron ya gudana a Babban dakin taro ta Munaj Event Center, inda aka tara manyan baki, masana harkar kasuwanci, da shugabanni na hukumomi domin duba hanyoyin bunkasa tattalin arziki mai dorewa.

Taron ya samu halartar manyan mutane da s**a hada da Kwamishinan 'Yan Sanda na Jihar Katsina, Shugaban Hukumar Kwastam ta Najeriya reshen Katsina, Shugaban Hukumar Shige da Fice ta Najeriya reshen Katsina, tsohon Gwamnan jihar Barno Abdulmumini Aminu Mai ritaya, shugabannin yan kasuwa masana, da wakilan hukumomi daban-daban.

A jawabinsa, Darakta Janar na KIPA, Ibrahim Tukur Jikamshi, ya bayyana muhimmancin tallafawa 'yan kasuwa na gida don samun damar shiga kasuwannin duniya. Ya ce, “Jihar Katsina tana da albarkatu masu tarin yawa k**ar amfanin gona, ma’adinai, da masana’antu. Wannan shirin zai ba da karin ilmi da dabaru na magance kalubalen da suke fuskanta k**ar karancin iya aiki, kasuwanni, da kudade.”

Jikamshi ya gode wa hukumomin da s**a tallafa wajen ganin taron ya samu nasara, ciki har da Hukumar Bunkasa Fitar da Kaya ta Najeriya (NEPC), Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Najeriya (NAFDAC), da hukumar Fitar da Kaya da Shigo da Kaya ta Najeriya (NEXIM). Ya ce, “Hadin gwiwarsu ta taka muhimmiyar rawa wajen ganin wannan shiri ya yi tasiri.”

Gwamna Malam Dikko Umar Radda, a jawabinsa, ya bayyana irin kokarin da gwamnatinsa ke yi wajen tabbatar da cewa Jihar Katsina ta kasance a sahun gaba wajen fitar da kaya zuwa kasashen waje. Ya ce, “Noma shi ne ginshikin manufofin tattalin arzikinmu. Mun zuba jari mai yawa wajen tallafawa manoma ta hanyar raba kayan noma, raya noman rani, da bunkasa darajar auduga da kiwo.”

Gwamnan ya kuma bayyana wasu manyan sauye-sauyen da gwamnatinsa ta kawo, k**ar kafa Hukumar Nauyin Kudi, aiwatar da tsarin fansho, da kara inganta al’amuran ilimi da lafiya. Ya kuma yi bayani kan gyaran hanyoyi, samar da ruwan sha, da bayar da tallafi ga masu 'yan gudun hijira.

A jawabinsa, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Katsina ya yaba da shirin, yana mai cewa zai rage rashin aikin yi da kara tsaro a jihar. Shugabannin Hukumar Kwastam da ta Shige da Fice suma sun yi alkawarin tallafawa wajen magance matsalolin da masu fitar da kaya ke fuskanta.

Taron ya kunshi gabatarwar masana da hukumomi k**ar Hukumar Kula da Inganci ta Najeriya (SON), Hukumar Bunkasa Fitar da Kaya, da Bridge Shipment Inspection Agency, inda aka tattauna kan dabarun shiga kasuwannin duniya da kuma bunkasa tattalin arziki.

Daya daga cikin mahalarta taron ya bayyana cewa, “Wannan shiri ya ba mu dabaru masu mahimmanci don bunkasa fitar da kayayyakinmu.”

Gwamna Radda ya kammala taron da kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su hada kai don bunkasa fitar da kaya daga Jihar Katsina. Ya ce, “Tare, za mu iya kara yawa da kuma darajar kayan da muke fitarwa, ta yadda za mu kirkiri ayyukan yi da habaka masana’antu.”

Manyan abubuwan da s**a ja hankali da habaka taron sun hada da: Halartar manyan jami’an tsaro, shugabannin hukumomi, da masana harkar kasuwanci.
Mayar da hankali kan fitar da kayayyakin gona, Ma’adinai da sauran su, zuwa kasuwannin duniya.
Gyaran tsare-tsaren gwamnati don inganta harkokin kasuwanci.
Karfafa masu fitar da kaya da kayan aiki da dabarun da za su inganta harkokinsu.

Wannan rahoto ya nuna muhimmancin taron wajen bunkasa tattalin arzikin Jihar Katsina da kuma himmatuwar gwamnati wajen cimma burin ci gaba mai dorewa.

Tsohon gwamnan Sokoto Alh. Attahiru Bafarawa ya fice daga Jam'iyyar PDP.Bafarawa ya sanarda hakan a cikin wata takardar ...
14/01/2025

Tsohon gwamnan Sokoto Alh. Attahiru Bafarawa ya fice daga Jam'iyyar PDP.

Bafarawa ya sanarda hakan a cikin wata takardar wasika da ya aikewa Shugaban Jam'iyyar PDP na ƙasa.

2027: Seyi Tinubu ya cancanci zama gwamnan Legas, in ji Ministan MatasaMinistan Cigaban Matasa, Ayodele Olawande, ya goy...
14/01/2025

2027: Seyi Tinubu ya cancanci zama gwamnan Legas, in ji Ministan Matasa

Ministan Cigaban Matasa, Ayodele Olawande, ya goyi bayan Seyi Tinubu, ɗan Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da ya zama gwamnan Jihar Legas a zaɓe na gaba.

Olawande ya bayyana cewa Seyi ya cancanci jagorantar Jihar Lagos.

Yayin wata tattaunawa a shirin Mic On tare da Seun Okinbaloye, ministan ya yi tsokaci kan jita-jitar da ke yawo game da yiwuwar takarar Seyi a zaben gwamna na 2027.

Ya ce Seyi mutum ne mai jajircewa wanda ya riga ya nuna kwarewarsa wajen taimakon matasa tun kafin mahaifinsa ya zama Shugaban Ƙasa.

“Seyi ba shi ne ke yi wa kan sa yakin neman zabe don zama gwamna ba. Kungiyoyi irin su Coalition of Nigerian Youth Leaders (CONYL) da wasu sun nuna goyon bayansu ga Seyi domin ya maye gurbin Babajide Sanwo-Olu a 2027," in ji Ministan.

Jadawalin Kamfanonin da s**a amfana da kashin farko, na Lamunin kuɗaɗe daga Gwamnatin Jihar Katsina, a karkashin shirin ...
14/01/2025

Jadawalin Kamfanonin da s**a amfana da kashin farko, na Lamunin kuɗaɗe daga Gwamnatin Jihar Katsina, a karkashin shirin Gwamnatin Jihar na bunƙasa Kamfanoni, da matsakaitan Sana'o'i a Jihar.

Gwamnatin Jihar Katsina zata sake maido da shirin bada tallafin Littattafan rubutu ga Ɗalibai a Jihar.
14/01/2025

Gwamnatin Jihar Katsina zata sake maido da shirin bada tallafin Littattafan rubutu ga Ɗalibai a Jihar.

Ɗan takarar Sanata a jam'iyyar NNPP a Borno ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar SDP Tsohon dan takarar Sanata na jam’iyyar NNP...
14/01/2025

Ɗan takarar Sanata a jam'iyyar NNPP a Borno ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar SDP

Tsohon dan takarar Sanata na jam’iyyar NNPP a jihar Borno, Atom Magira ya fice daga jam’iyyar zuwa ta Social Democratic Party, SDP.

Magira wanda tsohon dan takarar gwamna ne a karkashin jam’iyyar APC, shi ake ganin s matsayin jagoran jam'iyyun adawa a jihar, inda a kwananan aka k**a shi kuma aka tsare shi a gidan yari saboda kiran da ya yi na neman ‘yan siyasa da su yi hadaka (Maja) a jam’iyyar adawa daya a jihar da kuma zarginsa da s**ar Gwamna Babagana Umara Zulum.

Amurka ta yi tayin dawo da makuden kudaden da aka karkatar da su zuwa kasar ta hanyar halasta kudin haram daga Najeriya,...
14/01/2025

Amurka ta yi tayin dawo da makuden kudaden da aka karkatar da su zuwa kasar ta hanyar halasta kudin haram daga Najeriya, ciki har da na Diezani Alison-Madueke da mukarrabanta. Amurka dai ta gindaya sharuda ta ce "kudi a kashe su ta hanya mai kyau".

"Na dawo goyon bayan dokar haraji ne saboda an magance korafina" - Gwamna Abdullahi Sule
14/01/2025

"Na dawo goyon bayan dokar haraji ne saboda an magance korafina" - Gwamna Abdullahi Sule

Babban mai gabatar da kara na gwamnatin Mali Boubacar Moussa Diarra, ya ce ko a kwanakin bayan an cafke wasu mutane hudu...
14/01/2025

Babban mai gabatar da kara na gwamnatin Mali Boubacar Moussa Diarra, ya ce ko a kwanakin bayan an cafke wasu mutane hudu 'yan kasar Canada da suke hada-hadar zinariya ta haramtacciyar hanya. Mali na daya daga cikin kasashen da ke kan gaba a wajen fitar da zinare a kasuwannin duniya.

Gwamna Dikko Radda ya ƙaddamar da raba manyan wayoyin hannu dubu ashirin 20,000 da za a raba wa malaman makaranta, da ku...
14/01/2025

Gwamna Dikko Radda ya ƙaddamar da raba manyan wayoyin hannu dubu ashirin 20,000 da za a raba wa malaman makaranta, da kuma motoci 70 na zirga-zirga duba Malaman makarantu a duk fadin jihar Katsina

Bazamu ce ga Ranar da matsalar wutar lantarki ne Arewacin Najeriya zata zo karshe ba, inji gwamnatin tarayya.
14/01/2025

Bazamu ce ga Ranar da matsalar wutar lantarki ne Arewacin Najeriya zata zo karshe ba, inji gwamnatin tarayya.

Babu Wani Mahaifi Da Yazo Yanuna Akwai Yaronshi Daga Ciki Sama Da Yara 230 Da Aka Yiwa Tattara Suna Gararanba A Titin Ka...
14/01/2025

Babu Wani Mahaifi Da Yazo Yanuna Akwai Yaronshi Daga Ciki Sama Da Yara 230 Da Aka Yiwa Tattara Suna Gararanba A Titin Kano - Hisbah | Rana24 Newspaper

Ko Bola Tunibu da Ganduje Basu isa Su Koreni daga APC ba duk da kulle kullen Kamani da ake - 'Dan Bilki | Rana24 Newspap...
14/01/2025

Ko Bola Tunibu da Ganduje Basu isa Su Koreni daga APC ba duk da kulle kullen Kamani da ake - 'Dan Bilki | Rana24 Newspaper

Kuma bazan taɓa goyuwa da zaluncin Gwamnatin APC ba ina tare da Bala Muhammad Gwamnan Bauchi Jagoran tsage gaskiya.

Cewar Abdulmajid 'Dan Bilki Kwamanda Na Jam'iyyar APC

Address

Katsina
KATSINA

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rana24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rana24:

Videos

Share