Katsina Reporters

Katsina Reporters Shafin Katsina Reporters jarida ce da ke kokarin kawo maku ingantattun labarai na gaskiya ciki da wajen Katsina.
(2)

An kaddamar da shuwagabannin kungiyar Ƴan Jarida ta NOMF masu amfani da kafafen sadarwa na zamani a KatsinaƘungiyar masu...
04/02/2025

An kaddamar da shuwagabannin kungiyar Ƴan Jarida ta NOMF masu amfani da kafafen sadarwa na zamani a Katsina

Ƙungiyar masu amfani da kafafen sadarwa na zamani mai suna National Online Media Forum (NOMF) reshen jihar Katsina ta gudanar da taronta na farko tare da zaɓar shugaban riƙon ƙwarya na ƙungiyar.

Taron wanda aka gudanar a wannan Lahadin a ofishin kafar sadarwar Reality New TV da ke Mangal Plaza Ƙofar Ƙaura a jihar ta Katsina.

A yayin jawabin manufar taron, Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Umar Lawal Funtua, ya bayyana cewa, dalilin kafa ƙungiyar shi ne, inganta aikin jarida a tsakanin kafafen sadarwar zamani da kuma ceto aikin daga hannun ɓata garin mutane da ke tashi rana tsaka su k**a aikin ba tare da sanin mak**arsa ba.

Shi ma a yayin jawabinsa, jim kaɗan bayan karɓar takardarsa a matsayin shugaban riƙo na jihar, Abubakar Shafi'i Alolo, shugabn kamfanin kafar sadarwa ta Mobile Media Crew wanda Nasiru Umar ya amsa a madadinsa, ya bayyana cewa zai gudanar da aiki tare da ƴaƴan ƙungiyar cikin adalci da kuma kawo ci gaba mai ɗorewa.

Waɗanda s**a halarci taron sun haɗa da shugabannin kafafen yaɗa labaran da wakilansu Inda aka tattauna muhimman batutuwa tare da karɓar shawarwari daga mahalarta taron kan yadda tafiyar za ta kasance. Haka zalika s**a lashi takobin kawo gyara da kare martabar aikin jarida ta amfani da kafafen sadarwar na zamani.

Jerin kafafen sadarwar na zamani da s**a halarci taron, sun haɗa da;

Jadawali TV, Fitila, Online, Popular News, Reality News TV, Salwa RTV, Jakadiya Online Media, Xsound Media, Albishir Media, Verified Mews, Mobile Media Crew, FBC, Danmasani Online Radio, Katsina Post, Hikaya News Paper da Katsina Times.

A ƙarshen taron an ƙawata shi da miƙa takardar k**a aikin jagorancin ƙungiyar a matakin jiha ga Abubakar Shafi'i Alolo.

Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma Tayi Alƙawarin Kawo Ƙarshen Matsalar Rashin Zuwan Yara Makaranta, Kawar Da Talauci, ...
03/02/2025

Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma Tayi Alƙawarin Kawo Ƙarshen Matsalar Rashin Zuwan Yara Makaranta, Kawar Da Talauci, Da Kuma Samar Wa Matasa Abun Yi

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa maso yamma kuma gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ne ya tabbatar da haka a lokacin da yake ganawa da manema labarai a ranar Litinin 3 ga watan Fabrairun 2025, jim kaɗan bayan fitowa daga wani zama da ya jagoran ta tare da sauran gwamnonin na arewa maso yamma.

Zaman kuma an yi shi ne tare da mataimakiyar sakataren majalissar ɗinki duniya Amina J Muhammad, da wasu wakillan majalissar, da na bankin cigaban ƙasashen Afirika "African Development Bank AfDB"

A lokacin da yake magana da manema labaran shugaban ƙungiyar gwamnonin ta arewa maso yamma Malam Dikko Umaru Radda PhD, ya bayyana dalilin zaman nasu da mataimakiyar sakataren majalissar ɗinkin duniyar sabo da muhimmanci alaƙar da ke tsakanin ƙungiyar da majalissar da kuma irin jagorancin da take yi a yankin na arewa maso yamma.

Mambobin ƙungiyar sun amince da ɗaukar matakin gaggawa domin magance matsalolin da ke addabar ilimi, da kuma ƙarancin abinci, inji gwamna Raɗɗa.

Ya kuma ce dalilin zaman da jami'an Bankin cigaban ƙasashen Afirika shine sabo da shirin NAG 2.0 watau shirin bunƙasa noma a Najeriya "Nigerian Agricultural Growth Scheme" wanda za'ayi a jihohin na arewa maso yamma, ya ce ƙungiyar zata fara wannan shiri ne domin bunƙasa noma da kiwo a yankin.

Gwamnan ya cigaba da cewa zaman nasu da Bankin cigaban ƙasashen Afirika "AfDB" ya shafi aiwatar da shirin bankin na musamman domin bunƙasa noma a karkara "Special Agro-Processing Zones SAPZ" kashi na biyu, tsare-tsaren shi da kuma bunƙasa kiwo a sauran jihohi biyar na yankin sak**akon jihar Kano da Kaduna sun amfana da shirin kashi na farko.

Ya cigaba da cewa ƙungiyar kuma ta tattauna batun da ya shafi haɗaka da kamfanin IRS mai samar da kayan amfanin yau da kullum masu amfani da mak**ashi na zamani musamman masu amfani da hasken rana domin bunƙasa tattalin arzikin yankin, sai kuma abun da ya shafi bashin biyan ɗalibai domin biyan kuɗin makaranta na gwamnatin tarayya (NELFUND) domin amfanar al'ummar yankin.

Domin inganta shirin a yankin, ƙungiyar ta tabbatar da Mista Maryam Musa Yahya a matsayin darakta janar da zata kula da shirin, Maryam Musa tana da ilimi da ƙwarewa wajen alaƙar ta da ƙungiyoyin cigaba da kuma aiki da tayi a ofishin ƙungiyar gwamnoni (NGF) zai taimaka wajen samun nasarar shirin.

Mun kuma amince da tafiya tare domin bunƙasa tattalin arziki, bunƙasa noma, kawar da ƙaruwar yara masu dai na zuwa makaranta, rage talauci, da kuma samar da abun yi ga matasan jihohin mu, wannan shi ne babban ƙudirin gwamnatocin mu na arewa maso yamma.

Daga ƙarshe Gwamnan ya nuna goyon bayan gwamnatin shugaban ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu akan tsare-tsaren ta da za su ciyar da tattalin arzikin ƙasar gaba.

Wanda s**a halarci taron akwai gwamnan jihar Kaduna Uba Sani, Dauda Lawal na Zamfara, Ahmed Aliyu na Sokoto, Umar Namadi na Jigawa, Kodinetan majalisar ɗinkin duniya Malick Fall, da sauran su.

Kafa jam'iyyar hadaka ba zai kayar da jam'iyyar APC ba a zaɓen 2027 --MasariTsohon Gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Mas...
03/02/2025

Kafa jam'iyyar hadaka ba zai kayar da jam'iyyar APC ba a zaɓen 2027 --Masari

Tsohon Gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari, ya ce babu wata mafita da ta zarce goyawa jam'iyyar su ta APC, baya a yanayin da Nigeria ke ciki a yanzu

A cewar Masari, masu fafutikar kafa sabuwar jam'iyyar haɗaka suna yi saboda basu samu muk**ai a gwamnatin APC ba. Ya kuma ce ba za su yi nasara ba.

Masari, ya fadi hakan a lokacin da yake yin jawabi a wajen kaddamar da yakin neman zaben kananun hukumomin jihar Katsina a karamar hukumar Kafur.

Gwamnatin jihar ta sanar da cewa za'a gudanar da zaɓukan kananun hukumomin a ranar 15, ga watan Fabrairu 2025.

Yanzu-Yanzu: Gwamna jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD yana jagorantar taron ƙungiyar gwamnonin arewa maso yamma ...
03/02/2025

Yanzu-Yanzu: Gwamna jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD yana jagorantar taron ƙungiyar gwamnonin arewa maso yamma a gidan gwamnatin jihar Katsina da ke birnin tarayya Abuja.

📸 -Gwamnatin jihar Katsina.

03/02/2025

Jami'an tsaro na C-Wartch sun k**a wani ƙasurgumin mai garkuwa da mutane a Katsina.

Jam'iyyar APC Ita ce mafita ga al'ummar Najeriya, duk da mawuyacin halin da ake ci --Inji Tsohon Gwamnan jihar Katsina, ...
02/02/2025

Jam'iyyar APC Ita ce mafita ga al'ummar Najeriya, duk da mawuyacin halin da ake ci --Inji Tsohon Gwamnan jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari

Me za ku ce?

An fara yunkurin wargaza shirin jam'iyyun adawa na ƙulla alaƙar siyasa da SDP a Najeriya Shugaban majalisar Dattawan Naj...
02/02/2025

An fara yunkurin wargaza shirin jam'iyyun adawa na ƙulla alaƙar siyasa da SDP a Najeriya

Shugaban majalisar Dattawan Najeriya Sen. Godwin Akfabio da mataimakinsa Sen. Barau Jibrin da wasu jiga-jigan jam'iyyar APC mai mulki a matakin gwamnatin tarayya ma sun ziyarci shugaban jam'iyyar SDP a hedikwatar jam'iyyar da ke babban birnin tarayya, Abuja.

Wannan dai na nuni ne da irin karbuwa da kuma farin jinin da jam'iyyar ta SDP ke da shi kuma take cigaba da samu a zukatan yan Najeriya musamman ma masu kawo sahihin canji da cigaba mai anfani a faɗin ƙasar.

Dama dai ko a kwanakin baya, an ga wasu jiga-jigan jam'iyyun adawa a fadin Najeriya na kai ziyara mai k**a da ta roƙon iri a hedikwatar jam'iyyar ta SDP tare da gudanar da taruka a jahohi da dama na Najeriya duk domin ganin yadda za su hade wuri daya tare da tunkarar zaben 2027 da ke tafe.

Tunda aka kafa jihar Katsina daga mulkin soja har na farar hula ba a taɓa Gwamnan da a shekarar shi ta farko yayi ayyuka...
02/02/2025

Tunda aka kafa jihar Katsina daga mulkin soja har na farar hula ba a taɓa Gwamnan da a shekarar shi ta farko yayi ayyukan da Gwamna Radda ya yi ba --Inji shugaban kungiyar “Dikko Project Movement Hon. Musa Gafai

Al'ummar jihar Katsina ya kuke kallon wannan batun?

Tsohon shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari, ya karɓi bakuncin Honourable Aisha Jibril Dikku 'yar majalisar wakilan ...
02/02/2025

Tsohon shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari, ya karɓi bakuncin Honourable Aisha Jibril Dikku 'yar majalisar wakilan Najeriya daga 2019 zuwa 2023 wacce ta gabatar da kudirin kafa hukumar kula da Almajirai ta ƙasa, a gidansa na Daura da ke jihar Katsina.

A yayin ziyarar Hon. A'isha Jibrin Dukku ta samu rakiyar Hon. Dakta Balarabe Shehu, a ranar Asabar 1 ga watan Fabrairu 2025.

Labari Cikin Hotuna:Yadda aka gudanar da bikin liyafar cin abincin dare domin taya sabuwar shugabar jami'ar Abuja, 'yar ...
01/02/2025

Labari Cikin Hotuna:

Yadda aka gudanar da bikin liyafar cin abincin dare domin taya sabuwar shugabar jami'ar Abuja, 'yar asalin jihar Katsina, Farfesa Aisha Sani Maikuɗi murnar zama shugabar jami'ar Abuja.

Gwamnan Katsina Dikko Umar Radda PhD, yana daga cikin mahalarta taron liyafar cin abincin.

Shugaban Kungiyar “Dikko Project Movement Hon Musa Yusuf Gafai Ya Fice Daga Jam'iyyar Adawa Ta PDP Tare Da Magoya Bayans...
01/02/2025

Shugaban Kungiyar “Dikko Project Movement Hon Musa Yusuf Gafai Ya Fice Daga Jam'iyyar Adawa Ta PDP Tare Da Magoya Bayansa Inda Ya Amshi Katin Shiga Jam'iyyar APC A Mazaɓarsa Ta Wakilin Yamma II A Katsina

Shugaban gidauniyar "Gafai Charitable Foundation" kuma shugaban ƙungiyar Dikko Project matashin dan siyasa, Hon. Musa Gafai, ya amshi katin shiga jam'iyyar APC bayan ficewar shi daga jam'iyyar adawa ta PDP a mazaɓar shi ta yamma II, a farfajiyar makarantar firamare ta Gafai da ke Ƙofar Ƴan-ɗaka, a jihar Katsina.

Bayan kammala karɓar katin jam'iyyar Hon. Musa Gafai, ya yi ma Allah SWT godiya da ya nuna mashi wannan rana wacce ya dawo jam'iyyar shi ta asali domin bada gudummuwa ga mai gidan shi gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda PhD.

Ya ƙara da cewa ganin irin ayyukan alkhairin da Gwamna Radda ya ke shimfiɗawa a faɗin jihar Katsina shiyasa yaga ya dace ya dawo wannan jam'iyya sabo da k**a mashi wajen gudanar da wannan ayyuka, sabo da idan ka duba irin tsare-tsaren gwamnan a fannin ilimi, ginawa gami da gyara asibitoci, da kuma ɗaukar ma'aikata sama da mutum 12,000.

Waɗan nan ayyuka kaɗai sun isa su gamsar da al'umma cewa Malam Dikko Radda aiki yazo ba aika-aika ba, ita adawa dama sabo da cigaban al'umma ake yin ta, kuma yanzu cigaban ya samu shiyasa muka ga babu amfanin zaman mu a cikin waccen jam'iyya.

A tarihin jihar Katsina tun daga mulkin soja har na farar hula ba'a taɓa gwamnan da a shekarar shi ta farko akan mulki yayi ayyukan da gwamna Mal Dikko Umaru Radda ya yi ba.

Gafai ya ci gaba da cewa rashin adalci da k**a karya ya sa ya bar jam'iyyar PDP domin taimaka wa Malam Dikko Radda PhD don ganin ya sauke nauyin al'ummar jihar Katsina.

Shi ma ɗan takarar shugaban karamar hukumar Katsina Hon. Isa Miqdad AD Saude, ya nuna jindadinsa da farincikinsa kan dawowar Hon. Musa Gafai a cikin jam'iyyar APC domin bada ta shi gudummuwar.

Daga ƙarshe yayi fatan alkhairi ga al'ummar da s**a halarci wurin da kuma wanda s**a yi mashi fatan alkahairi.

An Ɗaura Auran Ɗan Gidan Tsohon Shugaban Jam'iyyar APC na jihar Katsina A ranar Juma'a 31-01-2025 aka ɗaura auren Ɗan gi...
01/02/2025

An Ɗaura Auran Ɗan Gidan Tsohon Shugaban Jam'iyyar APC na jihar Katsina

A ranar Juma'a 31-01-2025 aka ɗaura auren Ɗan gidan tsohon Shugaban Jam'iyyar APC na jihar Katsina mai kamfanin Maslaha Motors Alhaji Sh*tu S. Sh*tu, wato Hanif Sh*tu Maslaha da amaryarsa Amina, a masallacin Sautus Sunnah Dake Kofar Kaura Layout, Katsina.

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina Dr. Mustapha da shugaban Hisba Sheikh Abu-Ammar da shugaban jam'iyyar APC na jihar Hon. Sani Aliyu JB da yan uwa da abokan arziki s**a halarci ɗaurin auren.

Yadda ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare ta Jihar Katsina ta Shirya Bikin Ranar Ilimi ta Duniya na Shekarar 2025 a ...
01/02/2025

Yadda ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare ta Jihar Katsina ta Shirya Bikin Ranar Ilimi ta Duniya na Shekarar 2025 a Katsina.

📸 -Zainab Musa Musawa.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UNAllah Ya yiwa hazaƙin matashi Kabir Muhammad Tanko, rasuwa sak**akon hatsarin mota da ...
31/01/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah Ya yiwa hazaƙin matashi Kabir Muhammad Tanko, rasuwa sak**akon hatsarin mota da ya rutsa da shi akan hanyar Zaria zuwa Funtua ta jihar Katsina.

Allah Ya gafarta masa.

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Radda ya halarci bikin rufe baje kolin kasuwanci da Kamfanin “Nigerian Exchange Group ...
31/01/2025

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Radda ya halarci bikin rufe baje kolin kasuwanci da Kamfanin “Nigerian Exchange Group NGX" s**a shirya a birnin Lagos.

📸 -Gwamnatin jihar Katsina.

30/01/2025

Shugaban "Brekete Family Ordinary Ahmad Isa, ya koyar da Mata sana'o'in hannu.



゚viralシ

Matashin Ɗan gwagwarmaya Kwamarad Suleiman Rabo ya sayi tikitin tsayawa takarar shugabancin kungiyar Matasa NYCN ta kasa...
30/01/2025

Matashin Ɗan gwagwarmaya Kwamarad Suleiman Rabo ya sayi tikitin tsayawa takarar shugabancin kungiyar Matasa NYCN ta kasa reshen jihar Katsina

Matashin dan gwagwarmaya Comrade Sulaiman Rabo Sule wanda tsohon PRO na NAKATSS NATIONAL BODY, ne kuma tsohon Shugaban Kungiyar KASTEBOSA ya sayi tikitin shedar tsayawa takarar shugabancin kungiyar matasa ta kasa reshen jihar katsina (NYCN).

Kamar yadda dokokin kungiyar ya tanadar babu wanda zai shiga neman shugabancin kungiyar batare da ya yanki tikitin shedar tsayawa takarar ba daga wajen kwamitin dazai jagoranci zaben kungiyar dake tafe

Hakan ne yabawa Comr. Sulaiman Rabo Sule dama a ranar Alhamis 30 /1/2025 ya garzaya ma'aikatar matasa ta jihar katsina domin karbar shedar tsayawa takarar shugabancin kungiyar matasa (NYCN) a Matsayin Chairman

Bayan karbar shidar shiga zabe daga wajen kwamitin gudanar da zaben, Dan Takara ya bama kwamitin tabbacin bin kowace ƙa'ida domin ganin an gudanar da zaben lafiya haka zalika, Dan Takarar ya tabbatar cewa mulki na Allah ne yana bada shi ga wanda yaso, daga bisani yayi kira ga magoya bayansa da kada suci mutuncin kowa idan Allah ya yarda sukeda nasara.

Bayan haka Shugaban Committeen yakin Neman zaben Comr. Mustapha Uba Mashi yayi kira ga committee gudanar da zabe da suyi adalci wajan yin sahihin zabe Kuma a shirye muke da mukarbi duk wani sak**ako bayan gudanar da zabe.

Yace kuma an tabbatar da cewa gwamnati ba tada wani Dan takara kowa na tane, Kuma za'ai sahihin zabe insha Allah.

Sarkin Daura Ya Ziyarci Buhari A Gidansa Na Daura A Jihar Katsina Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Farouk Umar, ya z...
30/01/2025

Sarkin Daura Ya Ziyarci Buhari A Gidansa Na Daura A Jihar Katsina

Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Farouk Umar, ya ziyarci tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, a gidansa na Daura dake jihar Katsina, a ranar Alhamis 30 ga watan Janairu 2025.

📸 -Buhari Sallau.

Address

No. 12, Ramadan Plaza Ƙwaɗo Ring Road Katsina
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share