Funtua Zone Media

Funtua Zone Media Muna Maku Barka da zuwa shafinmu Domin samun labaran Duniya kasance da jaridar Funtua Zone Media
(3)

ABIN ALHERI: Shugaban Karamar Hukuma Ya Gina Asibiti Mai Daukar Gadajen Majinyata 60 A Jihar KatsinaDaga: Shamsu Wapa Da...
29/04/2024

ABIN ALHERI: Shugaban Karamar Hukuma Ya Gina Asibiti Mai Daukar Gadajen Majinyata 60 A Jihar Katsina

Daga: Shamsu Wapa Dandume

Hon. Dr. Habibu Abdulkadir Shugaban Karamar Hukumar Musawa Jihar Katsina, Ya Shimfida Karamin Asibiti Mai Daukar Gadajen Majinyata Sittin 60 A Garin 'Yar-'Kirgi Dake Karamar Hukumar Musawa, A Kokarinshi Na Ganin Ya Inganta Harkar Lapiya A Karamar Hukumarsa.

K**ar Yadda Wakilinmu Ya Gano Mana, Shugaban Karamar Hukumar Musawa, Yana Daya Daga Cikin, Shuwagabannin Da S**a Shimfida Ayyukan Alkhairi Raya Kasa Masu Tarin Yawa A Jagorancinshi Na Shekara Biyu,

Wakilin Mu Ya Labarta Mana Akwai Wasu Ayyukan Raya Kasa Masu Tarin Tawa Da Ya Aiwatar K**ar:-

(1) Ya Gyara Kwata Dake A Kasuwar Garin Musawa, Musawa (A) Ward

(2) Ya Gyara Asibitin Yar-Awala Kurkujan (A) Ward

(3) Ya Gina Hanyar Ruwa Mai Tsayin Gaske A Marabar Musawa, Kurkujan (B) Ward

(4) Yayi Salaf Garin Kurkujan, Kukujan (A) Ward.

(5) Yayi Hanyar Ruwa Mai Tsayin Gaske A Garin Mangafi, Gingin Ward

(6) Yayi Hanyar Ruwa A Tabani/Yar-Raddau Ward

(7) Yayi Salaf A Unguwar Chakaro, Gingin Ward

(8) Yayi Salaf A Garin Kurkujan, Kurkujan (A) Ward.

Wadanan Kadan Kenan Daga Cikin Ayyukan Alkhairin Da Ya Shimfidawa Al'ummarsa Wadanda Maku Kawo Maku A Karon Farko, Zamu Kawo Maku Wasu Anan Gaba.

Dafatan Allah Yayi Mashi Jagora, Allah Yasaka Mashi Da Alkhairi Ameen.

~Karaduwa Post

HUKUNCIN ƊAURIN SHEKARU 15 NE GA DUK WANDA AKA K**A DA LAIFIN YIN AUREN JINSI A NAJERIYA - SHEIKH DAURAWAFitaccen malami...
07/03/2024

HUKUNCIN ƊAURIN SHEKARU 15 NE GA DUK WANDA AKA K**A DA LAIFIN YIN AUREN JINSI A NAJERIYA - SHEIKH DAURAWA

Fitaccen malamin addinin musulunci a Najeriya, kana kuma babban kwamandan hukumar (HISBAH) a Jihar Kano, Sheíkh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana cewa haramun ne namiji ya auri namiji, ko mace ta auri mace a Najeriya. Kuma ko da wasu sun yi haka a wata ƙasar da ta ba su lasisi in sun shigo Najeriya lasisinsu ya tashi a aiki.

Daurawa ya bayyana haka ne ta cikin wani bidiyo da Jaridar Dokin Ƙarfe TV ta samu, k**ar yadda ya ce "hukuncin shekara 15 ne ga duk wanda aka k**a da laifin yin auren jinsi a Najeriya batare da zaɓin biyan tara ba. Haka zalika duk wani masallaci ko wata coci ko wata ƙungiya da aka k**a da yi wa wasu auren jinsi to hukuncin shekaru goma ne a gidan yari".

Daurawa ya kuma ƙara da cewa wajibi ne su tsarkake al'ummarsu daga aikata dukkan wata ɓaɗala. "ba mu ne muke yin hukunci ba, mukan kamo masu laifi ne mu gabatar da su a gaban kotu bayan mun bincika a duk lokacin da mutanen unguwa s**a kawo mana ƙorafi, alƙali shi kuma shi ne yake tabbatar da hukunci idan ya gamsu da hujjojinmu". Cewar Sheíkh Daurawa.

Shekh AbdulLahi Shekh Balarabe Zawiyya Shine Ya Jagoranci Sallahar Janazar Hajiya Amina Matar Shekh AbdulLahi Dan Dume A...
07/03/2024

Shekh AbdulLahi Shekh Balarabe Zawiyya Shine Ya Jagoranci Sallahar Janazar Hajiya Amina Matar Shekh AbdulLahi Dan Dume

Allah Yajiqanta Da Rahamarsa
Allah Ya Hadata Da Annabi S,a,w

Abba Ahmad Siddiq Tafkitara
Mak**an Zawiyya

Zanga-zanga Ta Barke A Katsina.Rahotanni daga jihar Katsina nuni da cewar, wata zanga-zanga ta 6arke ta nuna alhini bisa...
01/03/2024

Zanga-zanga Ta Barke A Katsina.

Rahotanni daga jihar Katsina nuni da cewar, wata zanga-zanga ta 6arke ta nuna alhini bisa ga kara ta'azzarar hare-haren 'yan bindiga a fadin jihar Katsina.

Dandazon al'umma ne s**a taru a garin Birchi da ke karamar hukumar Kurfi, inda s**a hau T**i suna nuna alhininsu tare da jan hankalin gwamnatin jihar kan yawaitar ayyukan ta'adanci da 'yan bindiga ke ci gaba da yi a karamar hukumar.

Jihar Katsina dai na daya daga cikin jihohin Arewacin Nijeriya da ke fama da yawaitar hare-haren 'yan bindiga wanda da yawan a'umma ke rasa rayuwakansu, sace al'umma, ci masu zafi musamman ga mata, asarar dukiyoyi da dabbobi.

Daurawa ya sauka daga shugabancin hukumar Hisbah a KanoFitaccen malamin addinin Musulunci a Kano, Sheikh AminuIbrahim Da...
01/03/2024

Daurawa ya sauka daga shugabancin hukumar Hisbah a Kano

Fitaccen malamin addinin Musulunci a Kano, Sheikh Aminu
Ibrahim Daurawa, ya yi murabus daga muƙaminsa nabshugaban hukumar Hisbah a jihar.

Murabus ɗin malamin na zuwa kwana guda bayan da gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya nuna damuwarsa kan salon da hukumar Hisbah ke bi wajen yaƙi da masu aikata baɗala a Kano.

A wani bidiyo mai tsawon ƙasa da minti uku da Sheikh Daurawa ya wallafa a shafinsa na Facebook, malamin ya bayyana cewa kalaman gwamnan sun kashe masa gwiwa kuma a don haka ya ajiye muƙaminsa na jagora a hukumar ta Hisbah.

Daurawa ya ce "Mun yi iya ƙoƙarinmu domin yin abin da ya k**ata, to amma ina bai wa mai girma gwamna haƙuri bisa fushi da ya yi da maganganu da ya faɗa.

Kuma ina roƙon ya yi
mani afuwa na sauka daga wannan muƙami da ya bani na shugabancin Hisbah."

A ƴan kwanakin da s**a gabata ne, Hisbah ta k**a shahararriyar ƴar tiktok ɗin nan, Murja Ibrahim Kunya bisa zargin aikata baɗala a jihar Kano lamarin da hukumar ta ce ke lalata tarbiyyar matasa.

Hukumar ta kuma aika ta zuwa kotu wadda kuma ta tura ta gidan gyaran hali.

Bayan an aika ta gidan gyaran hali ne kuma aka wayi gari dablabarin sakinta daga kurkuku, abin da ya yi ta tayar da ƙura a tsakanin al'ummar jihar inda wasu ke ganin da hannun gwamnati a sakin nata - zargin da gwamnatin ta musanta.

A yanzu dai Murja Kunya na asibitin masu larurar ƙwaƙwalwa bisa umarnin kotu domin gwada lafiyar ƙwaƙwalwarta.

Kotun ta ce ƴar Tiktok ɗin za ta yi wata uku a can.

Abba Gida-gida ya gargadi jami'an Hisbah game da cakuɗa maza da mata idan sun yi laifiinda ya ce "ban ji daɗi ba yadda y...
29/02/2024

Abba Gida-gida ya gargadi jami'an Hisbah game da cakuɗa maza da mata idan sun yi laifi

inda ya ce "ban ji daɗi ba yadda yan Hisbah ke kwakumo maza da mata su cakuɗasu a mota daya ba"

Hisbah Hukuma ce mai albarka wadda muka dauka da martaba, kuma muka ɗauko bayin Allah wanda muka san za su iya muka ce ga amanar al'ummar jihar Kano.

Amma ma'anar Hukuma shi ne ta yi abin da ya ke daidai kuma a bai wa Gwamnatin shawara sannan a samu hadin kai tsakanin Gwamnati da masu ruwa da tsaki.

Na ga wani bidiyo da ya tayar min da hankali, kira nake da jan hankali gyara muke so.

An ɗebi motoci, an je inda wasu matasa ke ɓarna maza da mata, amma yadda aka riƙa debo su ana duka da gora suna gudu ana bi, ana tadile kafafunsu, ana debo su k**ar awaki haka a jefa su a cikin Hilux.

Wani ma Allah ya kiyaye in kashin bayansa ya karya Spinal Cord dinsa ya gama yawo har abada.

Wannan muna ganin kuskure ne babba, ka rungumo matashiya ko matashi ka jefa shi k**ar akuya a cikin Hilux.

Na ga bidiyo da aka je inda ɗalibai a Bayero suke har inda suke har dakunansu ana duka ana rungumosu, ana jefa su a cikin mota.

Mu muna ganin akwai gyara.

- Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf

Ba ku isa ku yi yaki da ni ba, martanin Tinubu ga kungiyar NLC.
29/02/2024

Ba ku isa ku yi yaki da ni ba, martanin Tinubu ga kungiyar NLC.

29/02/2024

FADA A TSAKANIN JAGORORIN YAN BINDIGA DADI NA JIHAR ZAMFARA. DA KATSINA YAYI, AJALIN ALHAJI BALDI K**AR YADDA RAHOTON BBC HAUSA YA BAYYANA

Hon Murtala Muhammad Malamiyya ya bayyana a niyarsa na tsayawa takarar kujerar Chairman na ƙaramar hukumar Funtua,Hon. M...
25/02/2024

Hon Murtala Muhammad Malamiyya ya bayyana a niyarsa na tsayawa takarar kujerar Chairman na ƙaramar hukumar Funtua,

Hon. Murtala Muhammad Malamiyya, wanda ya taba tsayawa takarar kujerar Majalissar Dokokin ƙaramar hukumar Funtua, ya kuma tsaya takarar Chairman na karamar hukumar, a wancan lokacin da ya gabata.

A wannan karan Tsayawa takarar ta Malam Murtala Muhammad Malamiyya ta samo asaline, bisa kiraye kirayen da Al'ummar karamar hukumar Funtua, s**ai tayi mashi, akan ya sake fitowa neman wannan kujerar, Bisa Yadda s**a gamsu da nagartarshi, da kuma Cancantarshi da s**a gani, a zaɓen da a gudanar a 15/2/2025, dake tafe.

Muna Fatan Alkairi Hon Murtala Muhammad Malamiyya, Allah ya bada nasarar a zaben fitar da gwanin. Da za a gudanar Nan bada jumawaba.

An Daura Auren Diyar Dan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Funtua DandumeA ranar Juma'a 23/February 2023, a ka gudanar da D...
23/02/2024

An Daura Auren Diyar Dan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Funtua Dandume

A ranar Juma'a 23/February 2023, a ka gudanar da Daurin Auren Maryam Diyar Hon. Abubakar Muhammad Dan majalisa mai Wakiltar Funtua Dandume, da Angonta Abubakar Muhammed, Daurin Auren da aka daura a masallacin Juma'a na Jama'a na (JIBWIS) dake cikin Garin Dandume, Ya samu Halartar 'yan siyasa, da ma'aikatan Gwamnati, masu rike da muk**an siyasa, 'yan kasuwa, 'yan uwa da abokan arziki. Dadai sauransu.

Maigirma Sanator Muntari Dandutse sanata mai Wakiltar Shiyar Katsina ta Kudu, shine ya bada auren Diyar Hon barister Abubakar Mohammed, Dan Majalisa Tarayya mai Wakiltar Funtua Dandume.

Daga cikin mahalarta daurin auren sun hada da, Wasu daga cikin yan Majalisa Tarayya da da sauransu

Katsina Media Reporters

Majalisar Dattawa Ta Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tsohon Shugaban ƙasa Buhari.Majalisar dattawan Nijeriya ta kafa wani k...
21/02/2024

Majalisar Dattawa Ta Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tsohon Shugaban ƙasa Buhari.

Majalisar dattawan Nijeriya ta kafa wani kwamiti da zai binciki tsohon shugaban ƙasa Buhari kan hanyoyin da ya kashe Naira tiriliyan 30, bisani kuma za su kuma su binciki Nera tiriliyan 10 da aka kashe a shirin Anchor “Borrowers Programme.”

Rahoto Mikiya.

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana jajircewar sa na kawo sauyi a harkar noma, da kai wa Nijeriya dogaro da kai w...
12/02/2024

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana jajircewar sa na kawo sauyi a harkar noma, da kai wa Nijeriya dogaro da kai wajen samar da abinci da kuma fitowa a matsayin mai fitar da kayan noma a duniya.

A wani gagarumin taro da ya gudana a fadar shugaban kasa da ke Abuja, shugaba Tinubu ya yi maraba da wata fitacciyar tawaga daga babbar kungiyar Tijjaniyya ta duniya, ƙarƙashin jagorancin Khalifa Muhammad Mahe Niass, a Yau Lahadi. Tinubu ya jaddada kudirin gwamnatinsa na na tallafa wa alhazai da bunkasa ayyukan ibada masu muhimmanci ga gina kasa.

Da yake karin haske kan alakar da ke tsakanin shugabannin siyasa da na Shugabannin addini Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmiyar rawar da hadin gwiwa ke takawa wajen ciyar da moriyar kasa gaba da samar da hadin kai a tsakanin 'yan Najeriya.

Shugaba Tinubu ya zayyana dabarun kawo sauyi a fannin noma, da s**a hada da fadada filayen noma, samar da lamuni mai rahusa ga manoma, da zuba jari mai tsoka a fannin noman rani.

Da yake nuna godiya ga kungiyar Tijjaniyya ta Duniya bisa hadin kai da addu’o’in da suke yi, Shugaba Tinubu ya jaddada cewa ya zama wajibi a yi aiki tare wajen ɗaukaka ƙasar Nijeriya mai albarka.

Sheikh Mahe Niass, Khalifan Tijjaniyya, ya yi na’am da wannan batu, inda ya yaba da jajircewar da Shugaba Tinubu ya yi wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba da zaman lafiya. Ya Gabatar da goyon baya da addu’o’in Darikar Tijjaniyya na Duniya, yana mai nuna hadin kan manufa wajen ciyar da Najeriya gaba.

KBC Hausa

Tsohon Gwamnar Jihar Kaduna Mukthar Ramadan Yero Ya Koma Jam'iyyar APC.Daga Shuaibu Abdullahi.Tsohon Gwamnan Jihar Kadun...
12/02/2024

Tsohon Gwamnar Jihar Kaduna Mukthar Ramadan Yero Ya Koma Jam'iyyar APC.

Daga Shuaibu Abdullahi.

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Muktar Ramalan Yaro ya koma Jam'iyyar Mai mulki ta APC.

Muktar Ramalan Yaro ya sanar da komawar sa Jam'iyya Mai mulki ta APC ne Jim kadan bayan ganawar sa da Shugaban ma'aikatan Gwamnatin Jihar Malam Liman Sani.

Idan baku manta ba Ramalan Yero ya riƙe matsayin gwamnan jihar Kaduna ne ƙarƙashin jam'iyyar PDP daga shekara ta 2012 zuwa 2015 bayan rasuwar tsohon gwamnan jihar Patrick Yakowa a wani hatsarin jirgin helikwafta.

Bayan cikar wa'adin riko ne daga nan ne ya yi takarar gwamnan jihar a ƙarƙashin inwar jam'iyyar ta PDP sai dai bai yi nasara ba, tun a zabukan fidda gwanayen Yan takara.

Tun cikin watan Oktoban shekarar 2023 Muktar Ramalan Yero ya bayyana ficewarsa daga jam'iyyar PDP.

LABARI DA ƊUMI-ƊUMI: Yanzu haka hukumar yaƙi da cin-hanci da rashawa ta Jihar Kano ta kai sumame ta bankaɗo wasu wurare ...
10/02/2024

LABARI DA ƊUMI-ƊUMI: Yanzu haka hukumar yaƙi da cin-hanci da rashawa ta Jihar Kano ta kai sumame ta bankaɗo wasu wurare da ake ɓoye kayan abinci k**ar yadda jaridar Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito a wannan rana ta Asabar.

(BMW02)ƳAN BINDIGA SUN KAI HARI KANDAWA TA BATSARIƳan bindiga sun kai hari garin Kandawa ta ƙaramar hukumar Batsari  ta ...
08/02/2024

(BMW02)

ƳAN BINDIGA SUN KAI HARI KANDAWA TA BATSARI

Ƴan bindiga sun kai hari garin Kandawa ta ƙaramar hukumar Batsari ta jihar Katsina. Lamarin ya faru a daren ranar laraba 07-02-2024.

K**ar yadda Jaridar Katsina Times ta wallafa a shafinta na facebook, tun da yammacin ranar larabar aka ga ayarin ɓarayin kan babura kimanin hamsin sun fito daga daji, sun tunkari ƙauyukan dake yankin arewa maso gabbacin Batsari. Wani basarake ya bayyana mana cewa "mun shaida ma masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, ɓarayi sun fito amma dai ba'a ɗauki mataki ba har s**a kai wannan hari"

Wani mazaunin garin ya bayyana ma jaridun Katsina Times, yadda abun ya faru, inda yace ɓarayin sun afka masu cikin shirin yaƙi, suna harba manyan bindigu k**ar za su ƙarar da garin. Sun kashe wata tsohuwa, kuma sun ƙona motar ƴansandar kwantar da tarzoma dake aikin bada tsaro a garin.
Sannan sun yi garkuwa da mutane 20 akasarin su mata ne. kuma sun kwashi dabbobi masu yawa.

Ƙungiyar Malamai Masana ilimin alkaluma ta ƙasa, ta kudiri aniyar marawa gwamnonin, sarakuna da duk wanda yake da kishin...
08/02/2024

Ƙungiyar Malamai Masana ilimin alkaluma ta ƙasa, ta kudiri aniyar marawa gwamnonin, sarakuna da duk wanda yake da kishin Arewa Baya, wajen ganin an shawo kan Matsalar tsaro dake addabar yankin arewa da kasa baki daya,

Shugaban kungiyar na kasa sheikh Habibi Abdallah Assufiyyu ne ya bayyana hakan lokacin da ya halarci taron Kungiyar Muryan Wakilan Matasan Najeriya, wanda ya gudana a garin Kano dake arewacin Nigeriya,

Kungiyar Malamai Masana ilimin Falaki ( Alkaluma) ta kasa, kungiya ce dake kunshe da zakakuren maluma amatsayin membobi afadin kasan nan, wanda s**a maida hankali wajen bada sadaukarwar lokacin su, saninsu da karfinsu wajen ganin sun hada malamai dangogin su daga ko wanne bangaren domin cimma manyan manufofi da s**a hada da ganin zaman lafiya da cigaban al'umma ya wanzu ta kowacce fuska kuma batare wariya na banbanci àdddini ko aqida ba.

A Jawabin shugaban kungiyar ya bayyana cewar" Ganin cewa gwamnoni, dattawa da sauran masu ruwa da tsaki na Arewa sunyi taro domin tattauna matsalar tsaro tare da shirin kawo mafita, babu shakka hakan yayi mana dadi matuka. Kuma Kungiyar mu tasamu kwarin gwuiwar da zamu goyi bayan wannan babban kudiri nasu kuma zamuyi amfani da yawan al'umma na mabiya da kungiyar ke dashi tare da hadin gwuiwar wasu kungiyoyi k**ar wannan babban kungiya na Muryan Wakilan Matasan Najeriya wajen ganin hakar mu ya cimma ruwa.

Domin a bisa alkalumar da muke dashi akan Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu suna bayyana mana akwai kyakkyawar atare dashi na ganin an samar da mafita dangane tsanani da al'ummar kasar nan ke ciki , wanda ya hada da matsalar tsaro, kuma muna kan shirya wani gagarumin addu'a a fadin kasa baki daya domin taimakawa fisabilillah.

Daga karshe yayi Kira gasu gwamnatoci da cewa ya zama wajibi su cire siyasa acikin lamarin matsin tattalin arzki dana matsalar tsaron kasar nan kafin nan asamu nasarar Samar da zaman lafiya da sauki, kuma ya zama wajibi dukkan shugaba yaji tsoron Allah, kuma yayi tunanin cewa mulkinsa mai karewa ne sannan dashi da dukkan abunda ya mallaka suma masu karewa ne, idan s**a fuskanci Allah acikin amanar al'umma da Allah yabasu da sannu Allah zai kawo mafita acikin alamuran kasar mu.

Jami'ian Tsaro Sun K**a Mutane 25 Daga Cikin Wadanda S**a Shirya Zanga-Zangar Yunwa Da Tsadar Rayuwa A Birnin Minna, Jih...
08/02/2024

Jami'ian Tsaro Sun K**a Mutane 25 Daga Cikin Wadanda S**a Shirya Zanga-Zangar Yunwa Da Tsadar Rayuwa A Birnin Minna, Jihar Neja.

Shin Yaya kuke lamarin ?

Sojoji sun bukatar da sama da mutum 30 da yan bindiga s**a sace a wani kauye dake karamar hukumar Batsari, yayin da gwam...
30/01/2024

Sojoji sun bukatar da sama da mutum 30 da yan bindiga s**a sace a wani kauye dake karamar hukumar Batsari, yayin da gwamna Dikko Radda ya gana da su bayan sun shaki iskar yanci

A lokacin da s**a ziyarci gwamnan a gidan gwamnatin jihar Katsina bayan an kubutar da su a hannun yan bindigar, gwamna Dikko Radda ya ba kowannensu naira dubu dari-dari har su 35 don su sami jalin da za su je su ci gaba da harkokin rayuwarsu cikin aminci

Bisa Ga Cancanta Hon.Murtala Mohammed Malamiyya Shine wanda ya Cancanci Zama shugaban ƙaramar hukumar FuntuaA kwanakin b...
29/01/2024

Bisa Ga Cancanta Hon.Murtala Mohammed Malamiyya Shine wanda ya Cancanci Zama shugaban ƙaramar hukumar Funtua

A kwanakin baya ne mai girma Gwamna jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, yasha alwashin gudanar da sahihin zaben kananan hukumomi a jihar Katsina.

Idan Allah ya kaimu za'ai zaben, to a Funtua muna fatan Hon. Murtala Mohammed Malamiyya ya sake fitowa takarar kujerar Chairman na karamar hukumar Funtua, Kasancewarsa Jajirtacce wanda yake da kwarewa ta Bangangarori Da'dama, tabbas yana da kwazon da zai kawowa funtua cigaba.

Ina fafan Hon. Zai sake fitowa ya tsaya takarar neman takarar kujerar chairman na garin funtua, Babu wanda ya cancanci zama Chairman na Funtua Local Govt, k**ar Hon. Murtala Muhammad Malamiyya Funtua.

Mafita ga Al-ummar Funtua da Kewayenta Hon Murtala Muhammad Malamiyya Shene Wakilin da Al-umma ke muradi a shekarar 2024 Insha Allah, Hon. Kayi barcinka cikin dad'in Rai. Allah ne zai baka Insha Allah.

Muna maka Fatan Alkairi

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta fitar da K**aru daga Gasar cin kofin nahiyar Afirka da ci 2-0 a wasan da s**a yi ran...
27/01/2024

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta fitar da K**aru daga Gasar cin kofin nahiyar Afirka da ci 2-0 a wasan da s**a yi ranar Asabar a Ivory Coast.
Mene ne ya fi burge ku a wasan?

Daga kashe dai shugaban rikon jam’iyyar APC mai mulki ta kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya gayyaci tsohon ubangidansa k...
25/01/2024

Daga kashe dai shugaban rikon jam’iyyar APC mai mulki ta kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya gayyaci tsohon ubangidansa kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP domin ya dawo da martabar jam’iyya mai mulki.

Gwamna Ganduje ya mika irin wannan gayyata ga Gwamna Abba Kabir Yusuf da tsohon Sanata mai wakiltar Kano ta tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau domin su koma APC.

Ganduje wanda ya yi wannan roko a yau Alhamis a karshen taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Kano, inda ya bayyana cewa jam’iyya mai mulki a shirye take ta dawo da daukacin ‘ya’yan jam’iyyar adawa zuwa APC.

Idan sulhu ya tabbata, shin ina makomar magoya bayan 'yan siyasar?

Yanzu yanzu: Shugaban riƙon jam'iyyar APC na ƙasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje, yana ganawa da jagororin jam'iyyar na jiha...
25/01/2024

Yanzu yanzu:

Shugaban riƙon jam'iyyar APC na ƙasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje, yana ganawa da jagororin jam'iyyar na jihar Kano, bayan ziyarar da kawo a daren jiya Laraba.

Arewa Za Su Yi Maraba Da Mayar Da Gidan Gwamnatin Tarayya Zuwa Legas - BashirƘarin bayani shiga na
25/01/2024

Arewa Za Su Yi Maraba Da Mayar Da Gidan Gwamnatin Tarayya Zuwa Legas - Bashir

Ƙarin bayani shiga na

Sanatocin Arewa Sunyi Wasti da Shirin Gwamnatin Tarayya na Mai da Wasu Hukumomi Daga Abuja Zuwa Legas Tare Da Zargin an ...
24/01/2024

Sanatocin Arewa Sunyi Wasti da Shirin Gwamnatin Tarayya na Mai da Wasu Hukumomi Daga Abuja Zuwa Legas Tare Da Zargin an tafka magudi a cikin kasafin kudin 2024 akan Arewa.

Sanatocin Arewa sun yi watsi da shirin mayar da wasu hukumomin Gwamnatin tarayya daga Abuja Zuwa Legas K**ar yadda s**a yi zargin cewa an tafka magudi a cikin kasafin kudin 2024 a kan Arewa.

Babban bankin Najeriya CBN a wata Sanarwa da ya fitar a makon jiya ya bayyana shirin mayar da wasu ma’aikatunsa Zuwa Jihar Legas, Saboda cunkoso a hedikwatarsa ​​da ke Abuja.

Bayan sanarwar CBN, Ministan Sufurin Jiragen Sama Festus Keyamo ya kuma bayar da umarnin mayar da hedkwatar Hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya FAAN daga Abuja zuwa Legas.

‘Yan Majalisar a Ƙarƙashin ƙungiyar Sanatocin Arewa, sun nuna Rashin Amincewarsu da matakin, Inda s**a Buƙaci al’ummar mazabar su da su yi hakuri, inda s**a ce za su shiga tattaunawa da bangaren zartaswa cikin lumana tare da samar da matakan da s**a dace don magance matsalar.

Sanatocin, a wata sanarwa da mai magana da yawun su, Sanata Suleiman Kawu Sumaila, ya fitar, yace: “A matsayinmu na wakilan jama’a a matakin kasa (Majalisar Dattawa), mun himmatu wajen ganin mun magance damuwa da jin dadin mazabarmu dangane da wasu shawarwari da manufofin da aka fitar. ta gwamnatin tarayya – jajircewa wajen rabo da rabon kayan aiki a cikin kasafin kudin 2024, mayar da wasu hukumomin tarayya daga Abuja zuwa Legas.

“A ƙarshe, mu a matsayinmu na wakilan jama’a, mun himmatu sosai wajen magance matsalolin dake addabar jama’a. Muna rokon ku ci gaba da bamu goyon baya, Amincewa, da hakuri yayin da muke ƙoƙarin samar da sak**ako mai kyau ga mazabarmu da kuma kiyaye dabi'un da kundin tsarin mulkinmu ya tanada."

KBC Hausa

Dikko Radda ya kara yin sabbin naɗe-naɗen masu muhimmanci ga al'ummar jihar Katsina, har majalisar dokoki ta tantance su...
23/01/2024

Dikko Radda ya kara yin sabbin naɗe-naɗen masu muhimmanci ga al'ummar jihar Katsina, har majalisar dokoki ta tantance su

Majalisar Dokokin Jihar Katsina ta tantance Alh. Sha'ibu Aliyu a matsayin babban mai binciken kudade na kananan Hukumomin Jihar nan (Auditor General for Local Governments.

Alh. Sha'ibu Aliyu kwararran ma'aikacin Gwamnati a harkar binciken kudade wanda yayi aiki a ma'aikatu da dama dake fadin jihar nan

Haka kuma Majalisar ta tantance Alh Badaru Ya'u Yan tumaki a matsayin Darakta Janar a Hukumar kula da sayo kayayyakin Gwamnati ( Bureau of Public Procurement).

Alh. Badamasi Ya'u dan asalin karamar Hukumar Danmusa ne kuma gogagge a harkar tafiyar da lamurran Gwamnati.

Bugu da kari Majalisar ta tantance gami da amincewa da Dr. Rahama Nasir a matsayin mamba ta dindindin a Hukumar taimakekeniyar lafiya ta Jihar Katsina.

Mabobin Majalisar a karkashin jagorancin Rt.Hon.Nasir Yahaya sun yi fatan alheri ga wadanda aka tantancan tare da yin kira gare su dasu sadaukar da kansu domin kawo cigaba ga al'ummar Jihar nan.

BAYANAN FARASHIN KAYAN GONA DAGA KASUWAR KAYAN HATSI TA GARIN DANDUME JIHAR KATSINA 20/01/20241. Farar Masara Buhu 100kg...
21/01/2024

BAYANAN FARASHIN KAYAN GONA DAGA KASUWAR KAYAN HATSI TA GARIN DANDUME JIHAR KATSINA 20/01/2024

1. Farar Masara Buhu 100kg N49,500 zuwa N51,500

2. Jar Masara Buhu 100kg N50,000 zuwa N51,500

3. Jar Dawa Buhu 100kg N43,500 zuwa N45,000

4. Farar Dawa Buhu 100kg N48,000 zuwa N50,000

5. Dauro/Gero Buhu 100kg N48,000 zuwa N50.000

6. Waken Hausa Buhu N68,000 zuwa N74,000.

7. Waken Soya Buhu 100kg N45,000 zuwa N47,000

8. Tsabar Shinkafa Buhu 100kg N90,000 zuwa N104,000

9. Barkono danminci Buhu 100kg N100,000 zuwa N115,000

10. Barkono dankuyelo 100kg N53,000 zuwa N55,000

11. Barkono danmiyare 100kg N40,000 zuwa N43,000

12. Samfarerar Shinkafa Buhu N34,000 zuwa N36,000

13. Kalwa Buhu 100kg N54,000 zuwa N56,000

14. Kashin Rogo (Dry Cassava) Buhu 100kg N35,000 zuwa N40,000

15. Alk**a Buhu 100kg N51,000 zuwa N55,000

16. Dankali Buhu 100kg Naira N13,000 N16,000

17. Makani Buhu 100kg N20,000 zuwa N24,000

18. Kubewa busassa 100kg N35,000 zuwa N50,000

Ku cigaba da following dina domin samun cikakken rahoton farashin kayan gona akoda yaushe Insha Allah 🙏

Domin neman karin bayani, ku tuntube ni a wannan lambar 08062122047

Labari mai sosa zuciya: 'Yan bindiga sun kashe farinsifal tare da sace matarsa da karamin dansaWani labari mai sosa zuci...
20/01/2024

Labari mai sosa zuciya: 'Yan bindiga sun kashe farinsifal tare da sace matarsa da karamin dansa

Wani labari mai sosa zuciya da ban tausai, da ya afku ga Mallam Idris Abu Sufyan wanda Farinsifal ne na makarantar GSS Kuriga, yankin karamar hukumar Chikun jihar Kaduna, da yan bindiga s**a shiga har cikin gidansa s**a harbe shi a ka har lahira tare da yin garkuwa da matarsa da wani yaro karami

Lamarin ya afku daran Alhamis wayewar garin Jumu'ah k**ar yadda majiyar Katsina Daily News ta rawaito.

K**ar yadda yan yankin garin suke nuna alhini game da rashwar Farinsifal din, sun ce ganin cewa Farinsifal din yana da damar da zai iya ficewa daga kauyen ya koma cikin gari da kwana, amma sai ya ce ya fi sha'awar zama cinin al'ummar da ya rayu a cikinta

18/01/2024

Tsakanin Fetur da Abinci da kuma Magunguna. Wanne kuka fi bukatar Gwamnati ta rage farashinshi a cikin su?

Duk Zancen Lefe Da Ake Yi Ba Zancen Rikici Ba Ne, Samun Mijin Shi Ne Babban Lamarin Saboda Babu Miji Da Zai Bar Matarsa ...
18/01/2024

Duk Zancen Lefe Da Ake Yi Ba Zancen Rikici Ba Ne, Samun Mijin Shi Ne Babban Lamarin Saboda Babu Miji Da Zai Bar Matarsa Tsirara, Cewar Saratu Hashim

Tsadar Rayuwa: Farashin buhun dankalin Hausa da aka rika sayarwa a lokutan baya Naira Dubu da dari biyar (N1500) a Nijer...
18/01/2024

Tsadar Rayuwa: Farashin buhun dankalin Hausa da aka rika sayarwa a lokutan baya Naira Dubu da dari biyar (N1500) a Nijeriya yanzu kudinsa sun koma Naira Dubu Goma Sha Hudu (N14,000) a wasu kasuwanin Arewacin kasar.

Me kuke ganin za a yi domin kawo karshen matsalar hauhawar farashin kayayyaki a Nijeriya?

Address

Katsina Ala

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Zone Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Zone Media:

Videos

Share