Nigerian spy TV

Nigerian spy TV information is power ever one want power stay with Nigerian spy tv
(1)

Dambarwar masarautar Kano: A Kotun Ƙoli ma Sarki Sanusi ne zai yi nasara, in ji FalanaFitaccen lauyan nan mai rajin kare...
15/01/2025

Dambarwar masarautar Kano: A Kotun Ƙoli ma Sarki Sanusi ne zai yi nasara, in ji Falana

Fitaccen lauyan nan mai rajin kare ƴancin bil'adama , Femi Falana, SAN, ya tabbatar da cewa ko da an je Kotun Ƙoli, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi ll ne zai yi nasara a shari'ar dambarwar masarautar Kano.

Femi Falana ya yi bayanin hakan ne a taron tunawa da Chief Gani Fewehini karo na 21 da aka gudanar a yau Laraba a Legas.

Taron dai ya samu halartar lauyoyi da dama da masu ruwa da tsaki a fannin shari'a.

Da ya ke gabatar da maƙala a taron, Falana ya ce "Ina so na taya Mai Martaba murna bisa nasarar da ya samu a Kotun Ɗaukaka Ƙara , naji wanda ke Shari'a da shi na cewa zai tafi kotun koli, to ko an je can din ma Sanusi ne zai nasara, kai ko ina ma za a je kai ne da nasara.

"Mai Martaba zama daram, kowa yasan kotun tarayya bata da hurumi kan sha'anin masarauta.

"Yakamata kungiyar lauyoyi ta kasa ta dau mataki kan yadda wasu lauyoyi ke yaudarar wadanda su ke karewa a kotu, ya kamata mu ceto mutuncin wannan tsarin", inji Falana.

15/01/2025

Wato Shi Jirjin Sama Sai Ka Shiga An Rufe Ruf Za'a Ma Bayani.

14/01/2025

Gwamnatin Kwankwasiyya babu abinda take sai aikin gadar sama

14/01/2025

IAN UBANAN

Idan ku ka amince a ƙaro mana tamkar yaƙi 50 to a wata biyu za mu gama da ƴan ta'adda - Ministan tsaroMinistan Tsaro, Mo...
14/01/2025

Idan ku ka amince a ƙaro mana tamkar yaƙi 50 to a wata biyu za mu gama da ƴan ta'adda - Ministan tsaro

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya nemi Majalisar Wakilai ta saka kuɗaɗen karin tamkar yaƙi guda 50 a kasafin kudin 2025 don magance matsalar ƴan ta'adda a kasar.

Badaru Abubakar ya yi wannan roƙon ne a yau Talata yayin zaman kare kasafin kudin 2025 da kwamitin tsaro na majalisar ya shirya a Abuja.

Ya bayyana cewa, tare da wannan kayan aiki, za a kawo karshen matsalar ƴan ta'adda a cikin watanni biyu.

“Ma’aikatar Tsaro na da alhakin samar da wasu kayan aiki a wasu yankuna, amma ba mu da damar yin hakan.

“Daga abin da mu ka samu a 2024, mun iya samar da Motoci Masu Sulke guda 20 kawai, amma me za su iya yi?

“Idan mu ka samu karin motocin guda 50 da za su shiga dazuzzuka don fatattakar ‘yan ta’adda, ina tabbatar muku, cikin wata biyu za mu kawo karshen matsalar 'yan bindiga, amma babu tanadin hakan a kasafin kudin 2025.

“Ina fatan wannan Majalisa za ta kara wa Ma’aikatar Tsaro kudi, domin mu iya samar da kayan aiki a wuraren da ke bukata,” in ji shi.0

14/01/2025

Amarya da Ango

14/01/2025

Ga Crush din Mommie Niger

14/01/2025

Allah jikan malam Jafar

12/01/2025

Idan Kinsan Mijin Ɗan Madrid Ne Ki Rifawa Kanki Asiri Ki Kwanta Kiyi Bacci Kafun Yadawo.

Barcelona ta doke Real Madrid da ci 5-2 a gaban dubban magoya da ke filin wasa na King Abdullah da ke birnin Jeddah.Wann...
12/01/2025

Barcelona ta doke Real Madrid da ci 5-2 a gaban dubban magoya da ke filin wasa na King Abdullah da ke birnin Jeddah.

Wannan ce babbar nasara ta biyu da Barca ta yi a kan abokiyar hamayyarta cikin 'yan watanni.

Yaya kuka ga wasan?

12/01/2025

Inde Kinsan Mijinki Ɗan Real Madrid Ne Yau Inya Dawo Ransa A Ɓace Yau Karki Tambayeshi Meye Faru.

12/01/2025

Aminu Babba Dan,Agundi : Rigimar Sarautar Kano yanzu aka fara ba gudu ba Ja da Baya

Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero CFR,CNOL,JP.
11/01/2025

Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Aminu Ado Bayero CFR,CNOL,JP.

10/01/2025

Shigowar Abbas Sani Abbas Jam,iyyar APC daga NNPP ''Sunan,sa Abba kaci Taliyar Karshe ''

10/01/2025

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Alfaharin Kanawa

Kotun Ɗaukaka ƙara ta yi watsi da umarnin kotun taraiya na soke dawo da Sarki Sanusi Kotun daukaka kara ta Kano a yau Ju...
10/01/2025

Kotun Ɗaukaka ƙara ta yi watsi da umarnin kotun taraiya na soke dawo da Sarki Sanusi

Kotun daukaka kara ta Kano a yau Juma’a, ta yi watsi da umarnin babbar kotun da ta soke nadin Sanusi Lamido Sanusi a matsayin Sarkin Kano na 16.

Wani kwamitin mutane uku na kotun daukaka kara, a hukuncin da ta yanke, karkashin jagorancin mai shari’a Mohammed Mustapha, ya yi watsi da hukuncin da kotun tarayya ta yanke a ranar 20 ga watan Yuni, 2024, ƙarƙashin mai shari’a Abubakar Liman, na babbar kotun tarayya, wanda ya soke dokar masarautar Kano ta 2024 da ta sake nada Sanusi.

A cewar kotun daukaka kara, Mai shari’a Liman ya yi watsi da hurumin soke matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka bisa dokar majalisar masarautu ta 2024.

Ta kara da cewa, karar da wani basarake a jihar, Alhaji Aminu Babba Dan Agundi ya shigar, wanda alkalin babbar kotun ya dogara da ita wajen bayar da wannan umarni, ba ta da sahihanci.

Kotun daukaka karar ta ci gaba da cewa, tun da ba a bi ka’ida ba wajen shigar da ƙarar, hakan ne ya sanya ta rasa hurumin yin shari'ar.

A daya bangaren kuma, kotun daukaka karar ta bayar da umarnin sake zaman sauraron karar da Sarki Aminu Bayero ya shigar na kalubalantar hukuncin da gwamna Yusuf ya yanke na tsige shi.

Kotun daukaka karar ta bayyana cewa, shaidun da ke gabanta sun tabbatar da cewa ba a bai wa Bayero damar jin ɓangaren sa ba daga babbar kotun jihar Kano wadda, hakan ya sanya kotun daukaka karar ta ce kotun ta jiha ta gudanar da shari’ar rashin gaskiya a kansa.

Mai shari’a Mustapha, wanda ya yanke hukuncin, ya ce an gudanar da shari’ar ne ba tare da sanarwar sauraro ga Bayero ba domin ya iya gabatar da nasa bangaren.

09/01/2025

An hangi Tsohon Gwamnan Kaduna Malam Nasiru El,rufai na motsa jiki a Murtala Square

Gwamna Yusuf fara biyan  mataki na uku na biyan fanshoGwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Yusuf, fara biyan mataki na uku na...
09/01/2025

Gwamna Yusuf fara biyan mataki na uku na biyan fansho

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Yusuf, fara biyan mataki na uku na biyan fansho ranar Alhamis, wanda ya kai kimanin Naira biliyan 5, a wani yunkuri na rage wahalhalun da tsoffin ma’aikata ke fuskanta.

Wannan bayani ya fito ne daga wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Tofa, ya fitar a ranar Laraba. Ya bayyana cewa za a gudanar da bikin biyan fanshon ne a Fadar Gwamnati da ke Kano.

Sanarwar ta bayyana matakan da Yusuf ya dauka a baya don magance matsalar rashin biyan fansho. “Tun bayan hawansa mulki, wannan gwamnati ta biya sama da Naira biliyan 11 daga cikin bashin fansho na Naira biliyan 43 da ba a biya ba, a matakai biyu,” in ji sanarwar.

A mataki na farko, an ware Naira biliyan 6 ga Asusun Ajiya na Fansho na Jiha don tsoffin ma’aikata masu mukamin kasa da mataki na 10, sannan aka saki Naira biliyan 5 a mataki na biyu don tsoffin ma

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nigerian spy TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nigerian spy TV:

Videos

Share