Abba Gida Gida Tv

Abba Gida Gida Tv Abba Gida Gida tv
kwankwasiyya

Mai Girma Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bayan kammala taron Masu ruwa da tsaki akan Harkokin tsaro awannan ...
06/08/2024

Mai Girma Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bayan kammala taron Masu ruwa da tsaki akan Harkokin tsaro awannan jiha, tuni kuma Mai Girma Gwamnan yafara jagorantar Babban zama na Majalisar zartarwa ta jihar Kano awannan yammaci.

Dafatan Allah ubangiji yacigaba da taimakawa jihar Kano da Gwamnatin jihar Kano Ameen summa Ameen
6-8-2024

Abba Tukur Karaye shugaban kungiyar abba Gida Gida tv

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba K Yusuf ya bada umarnin fara daukan dalibai da kuma yi musu rajista a Makaratun g...
05/08/2024

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba K Yusuf ya bada umarnin fara daukan dalibai da kuma yi musu rajista a Makaratun gana da sakandare na Koyan Sana’o’i na Musamman guda ashirin da shida (26) wanda ke fadin Jihar Kano.

Wannan Makarantu/Cibiyoyin koyar da sana’o’i an samar dasu neh tun zamanin Mulkin Mai Girma Sen Rabiu Musa Kwankwaso. Sai dai Gwamnatin Ganduje (shekara 8 data shude tayi watsi da wannan Cibiyoyi masu muhimmanci, tare da kulle su, wanda yayi sanadiyyar korar dalibai da kuma lalacewar gine gine a wannan makarantu.

Ganin haka yasa Gwamnan Jihar Kano Alh Abba Kabir Yusuf ya bada umarnin fara gyara da kuma sabunta wannan Cibiyoyi da zasu taimaki matasan mu wurin dogaro da kai da kuma tabbatar da al’umma mai inganci a fadin Jihar Kano.

Tuni dai aikin sabunta wannan Cobiyoyi yayi nisa, inda an kammala wasu, sauran kuma sun kusa kammaluwa, tare da samar da kayan aiki na zamani. Dalibai zasu amfana wurin koyan sana’o’i kamar noman zamani, kimiyya da fasaha, harkan tsaro, wasannin zamani, kere kere da dai sauran su.

Bisa wannan kuduri na Mai Girman Gwamna, daya daga cikin wannan cibiyoyi da aka kammala, wato “Kano Reformatory Institute, Kiru” zai fara aiki nan take.

SAI JAM’IYYARKA TA KORE KA IDAN NA FALLASA WANI SIRRINKA, HON Abdulmumin Jibrin YA SAKE MAYAR WA DOGUWA MARTANI..YA BUKA...
05/08/2024

SAI JAM’IYYARKA TA KORE KA IDAN NA FALLASA WANI SIRRINKA, HON Abdulmumin Jibrin YA SAKE MAYAR WA DOGUWA MARTANI
..YA BUKACE SHI YA ƘYALE KWANKWASO

An jawo hankalina a kan wasu kamalai da ake alaƙanta su da Hon Alhassan Ado Doguwa a matsayin martaninsa kan gargaɗin da na yi masa a baya kan ya bar kalamansa na rashin kan gado, inda yake s**ar lamirin Jagoran NNPP/Kwankwasiyya na ƙasa da ma duniya baki ɗaya, ya mayar da hankalinsa kan ayyukansa na majalisa saboda akwai jan aiki da gabansa da yake jiran shi a can.

Kodayake abin da na yi tsammani daga wajensa shi ne ya ba jagoranmu haƙuri kuma ya ja bakinsa ya yi shiru, domin kare mutuncinsa a bainar jama’a da kuma la’akari da yanayin zaman ɗar-ɗar din da ake ciki a Kano, sai dai ban yi mamaki ba kan yadda Alhassan ya mayar da kansa kamar wani ɗan wasan kwaikwayo inda ya koma soki-burutsun da ya saba da jin ya fi kowa. Kallon da ya kamata jama’a su yi wa kalaman Alhassan ke nan sannan su yi watsi da su a ƙaton kwandon shara.

Har yanzu ina nan a kan kalamaina na baya, kuma bugu da ƙari, zan so in yi ƙarin haske da waɗannan bayanan a matsayin ƙarin martani ga Alhassan.

1- Na yi murna da yadda Hon Alhassan Doguwa ya yi amfani da wani ɓangare na Gargaɗina inda ya ba ni amsa BA Kwankwaso ba. A martanina na baya, na ƙalubalance shi da cewa ni zai soka, saboda ni ne sa’ansa, ba Kwankwaso ba. Martanin da ya yi min ya tabbatar da cewa tabbas ni ne sa’an nasa, ba Kwankwaso ba. Na gode wa Alhassan a kan haka, kuma ina mai tabbatar masa da cewa na shirya masa mu ci gaba da fafatawa. Ina so ya ɗan tsaya ya yi nazari a kan dalilin da ya sa Kwankwaso bai TAƁA tsayawaya mayar masa da martani ba. Zai fahimci cewa Kwankwaso ya shi Alhassan sa'an sa bane. Mune sao'in Alhassan.

2- Martanin da Alhassan ya yi ya daɗa tabbatar da raunin da yake da shi na shugabanci, musamman idan aka yi la’akari da shekarunsa. Da a ce shekarunsa ba su kai haka ba, da an yi masa uzuri. Duk da cewa Kwankwaso ya shafe tsawon shekaru yana kawar da kai ga zagi da cin zarafin da Alhassan yake masa, amma Alhassan ya ƙasa jurewa ko na tsahon kwana daya gargaɗi kawai da nayi masa kan ya ƙaurace wa ci gaba da zagin mutumin da ya fi shi ta kowanne fanni na rayuwa na b***e inna aika masa da zagi. Wancan ba ma zaginsa aka yi ba, gargaɗi aka yi masa, amma ya kasa natsuwa. Idan aka fara musayar zage-zage, wataƙila ya tsinci kansa a gadon asibiti. Ina fatan ya yi amfani da hikima a maimakon haka.

3- Gaskiya ne, ni dalibi ne a 1992, to amma shi ma Alhassan yana kammala karatu ya tsinci kansa a Majalisar Wakilai. Amma ni lokacin da na shiga majalisar, na kammala karatuna na digirin digir-gir kuma na yi karatu a Jami’ar kasuwanci na Havard da London, kuma gogaggen ɗan kasuwa ne sannan mai taimakon al’umma, a lokacin da Kwankwaso ya raine ni har na shiga majalisar. Bugu da ƙari, Kwankwaso, saɓanin Alhassan, sai da ya yi aikin gwamnati na tsawon shekaru 17 sannan ya yi digirinsa na biyu a Ingila, sannan ya yi wasu karance-karancen kafin ya lashe zaɓen majalisa sa kuma mataimakin Shugaban Majalisar mai wakilai mutane wajen dari shida 600.

4- Yayin da bayan shekaru 32, har yanzu Alhassan yana cikin majalisar a matsayin mamba, ba tare da ya yi wani hoɓɓasa na matsawa gaba saboda dalilan da kowa ya san su,
b***e ya zama Mataimakin Shugaban Majalisar, matsayin da Kwankwaso ya taka, kuma shi Kwankwason ya matsa daga majalisar inda ya lashe zaɓen zama mamba a kwamitin rubuta kundin tsarin mulki, ya yi Gwamnan Kano har sau biyu, ya yi Ministan Tsaro, ya yi Jakada na musamman a yankin Darfur na Sudan, mamba a kwamitin gudanarwa na hukumar NDDC, Sanata, mai neman takarar Shugaban Kasa har karo biyu, kuma ɗan takarar Shugaban Kasa sannan jagoran NNPP kuma Jagoran babbar aƙidar Kwankwasiyya a Najeriya da ma duniya baki ɗaya, wacce daga bisani ta haifi Gwamnnoni da ’yan majalisu da ministoci da jakadu da shugabannin hukumomin gwamnati da ma wasu da dama. Dole mu ci gaba da girmama shi saboda a lokuta daban-daban duk mun ci moriyarsa, musamman ma shi Alhassan da Kwankwason ya cetoshi ya koma Majalisar Wakilai a shekara ta 2007, bayan ya shafe shekaru 15 yana ƙoƙarin ganin hakan amma ya gaza, inda daga bisani ya canji wanda ya ke kan kujerar.

5- Ko da sau shurin masaƙi ne, ya kamata Alhassan da ma sauran jama’a su san cewa a kullum Kwankwaso mutum ne mai son zaman lafiya, uba ne, fitila ne, mai gina jama’a ne kuma ɗan siyasa ne da ya fi kowa tasiri a Arewacin Najeriya a yau, kuma yana da tarin magoya baya, musamman talakawa. Kwankwaso ba ya yi, kuma bai taba zuga matasa ko ma kowanne mutum ya tayar da zaune tsaye ba. Ya kamata mutane su kalli kalaman Alhassan a matsayin da suke - na ƙoƙarin neman suna ta hanyar saka Kwankwaso a surutanshi da neman ganin ido na birge wasu a Abuja cewa shi ne jagoran jam’iyyarsu a Kano. Wannan ba sabon abu ba ne, kuma ba zai yi nasara ba. Burinsa shi ne “Gwara kan Kwankwaso da na Tinubu” a matsayin hanya ɗaya tilo da zai sami gindin zama a matakin tarayya. Abin da yake ƙoƙarin faruwa ke nan a Kano a yau da muke ganin alamunsa. Za mu yi iya bakin ƙoƙarinmu mu kuma yi amfani da doka wajen daƙile wannan ɓatancin.

6- Ina ƙara ba Alhassan shawara da ya girmama tsufansa. Ya kamata ya taƙaita fadace-fadacensa da zage-zagensa da kalaman soki-burutsunsa ga iya jam’iyyarsa, inda a cikinta ya yi fada kuma yake ci gaba da yin faɗan da kowa. Maganar gaskiya ita ce idan wasu daga cikin shugabannin jam’iyyarsa, musamman waɗanda suke Abuja, waɗanda yake ƙoƙarin burgewa, s**a san irin kalaman da yake yi a kansu, sai sun kore shi daga jam’iyyar. Amma mu jira lokaci.

Daga ƙarshe, ina jajanta wa Alhassan, wanda bisa ga dukkan alamu yake fama da matsananciyar damuwa, musamman kasancewarsa mai rawani babu sarauta. Amma a matsayin danna-ƙirji, zai iya karbar sarautar “Sardaunan Rawani”. Allah ya ja zamanin Sardaunan Rawani.

Sani Ibrahim P**i
Hadimin:
Hon Abdulmumin Jibrin, MSc SEP PLD, MBA, PhD (Jarman Bebeji)
Ɗan Majalisa mai hawa huɗu, tsohon shugaban kwamitocin Kuɗi, Kasafin Kudi, Sufuri, Harkokin Waje, kuma yanzu haka Shugaban Kwamitin Gidaje da Muhalli na Majalisar Wakilai

Rev’d. Dr Henry C Ndukuba. Madugu Mai Allah
05/08/2024

Rev’d. Dr Henry C Ndukuba. Madugu Mai Allah

Yanzu Haka Mai Girma Mataimakin Gwamnan Jahar Kano Comr Aminu Abdussalam Gwarzo Ya Karaso Fadar Gwamnatin Kano.
05/08/2024

Yanzu Haka Mai Girma Mataimakin Gwamnan Jahar Kano Comr Aminu Abdussalam Gwarzo Ya Karaso Fadar Gwamnatin Kano.

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, Yayi Maganin Dan Tasha😀
05/08/2024

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, Yayi Maganin Dan Tasha😀

05/08/2024

Naji dadin yadda Gwamnan Gombe ya musanta sharrin da aka karanto jiya. Kayi daidai kar a hada maku koko da giya. Nifa ina wani zargi anya ba Ganduje ne ya rubutawa Tinubu Speech din jiya ba

His Excellency Governor Alhaji Abba Kabir Yusuf Allah karamaka lafiya Mai girma governor
05/08/2024

His Excellency Governor Alhaji Abba Kabir Yusuf Allah karamaka lafiya Mai girma governor

Earlier today, I paid a condolence visit to my Chief Personal Security Officer (CPSO), SP Bala Shehu Albasu, over the pa...
05/08/2024

Earlier today, I paid a condolence visit to my Chief Personal Security Officer (CPSO), SP Bala Shehu Albasu, over the passing of his wife, Zainab.

May the Almighty Allah grant her Jannatul Firdaus. - AKY

04/08/2024

Musulim musulim ticket da taliya sune Sanadi😭

04/08/2024

Alhamdulillah Masha Allah

Ku tafawa Mojo Kantoman Gwale Namijin Duniya da Tarauni da Nasarawa, k.m.c🙌🙌🙌Haka Mukeso Jami an Gwamnati Su Zama 👌
04/08/2024

Ku tafawa Mojo Kantoman Gwale Namijin Duniya da Tarauni da Nasarawa, k.m.c🙌🙌🙌

Haka Mukeso Jami an Gwamnati Su Zama 👌

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abba Gida Gida Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category