03/04/2024
Tahajjud: Duk Malamin Da Ya Fito Ya Kashe Wa Mutane Gwiwa Akan Sallar Tahajjud Ko Sallar Turawi, To Ya Tanadi Abinda Zai Fadawa Allah, Domin Yana Batar Da Mutane, Saboda Duk Duniya Ana Yin Tuhajju, Inji Sheikh Abdallah Gadon Kaya.
Ku kasance da jaridar ZangonLabarai domin samun sahahin labarai da Dumi-Duminsu
(1)
Tahajjud: Duk Malamin Da Ya Fito Ya Kashe Wa Mutane Gwiwa Akan Sallar Tahajjud Ko Sallar Turawi, To Ya Tanadi Abinda Zai Fadawa Allah, Domin Yana Batar Da Mutane, Saboda Duk Duniya Ana Yin Tuhajju, Inji Sheikh Abdallah Gadon Kaya.
Daga yankin Arewacin Najeriya an samu wani matashi mai suna Iliyasu ɗaya daga cikin mai yunƙurin sauya halittarsa zuwa mace.
SIYASA:- A Daren Jiya Talata ne dai Dan Takarar Gwamnan Jihar Katsina a Jam'iyyar PDP Sanata Lado Dan Marke Ya Dira Gidan Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam'iyyar NNPP Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a Birnin Tarayya.
Shin me kuke Tinani zai faru?
Hukuncin tsokanar marasa lafiyar ƙwaƙwalwa ya kai shekara ɗaya a gidan yari ko tarar N500,000. Jama’a mu kiyaye. -Abba Hikima
Babu ranar da mutane baza suyi tagging ɗina akan abunda ake yiwa wannan bawan Allahn ba. Yau wani likita ya biyo ni har inbox ya ɓuƙaci a ƙara jan hankalin masu tsokanarsa saboda lafiyarsa.
Kwanakin baya nayi magana akan sa inda na roki masu tsokanarsa su daina duba da cewa akwai rashin lafiya a tare da shi, kuma ashariyar da ake sawa yana yi domin saka wasu nishaɗi ba abun so bane, amma sai masu amfana da rashin lafiyarsa s**a sa shi yayi min video yana cewa “shi video yanzu ma aka fara yi masa”. Saboda na lura daga shi har masu tsokanar tasa suna amfana da rashin lafiyarsa.
To har yanzu dai ina kara kira a gare mu baki ɗaya. Na tabbataba idan ɗan’uwanmu ne baza muso abunda ke faruwa ba.
Idan zamu taimake shi saboda Allah muyi. Amma wannan abun bai dace ba. Sannan ya saɓawa dokokin Nigeria.
Daga Abba Hikima
Sabon shugaban Senegal ke nan Bassirou Faye tare da uwar gidansa Marie (dama) da amarya Absa (hagu) a lokacin rantsar da shi.
Wace ce kuke ganin za ta zama uwar gidan shugaban ƙasa?
POTUNA;-Majalisar dokokin jihar Kano ta tantance Mustapha Rabi'u Kwankwaso a matsayin kwamishina.
Tunda fari dai, gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya aikewa majalisar da sunansa domin a tantance shi don ya bashi kujerar kwamishina.
Daga farkon watan Azumin Ramada zuwa wannan lokaci mutum kusan miliyan biyu ne ke halartar sallar Tahajjud a ko wace rana a masallacin manzon Allah SAW da ke birnin Madina.
Shin ta wace hanya kuke kara matsa kaimi don samun kusanci da ubangiji yayin da Ramadan ke bankwana?
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya taya Faye murnar rantsar da shi a matsayin sabon shugaban kasar Senegal a yau Talata.
DA DUMI-DUMI: Farfadowar darajar Naira, an samu sauƙin hauhawar farashin kayayyaki Inji kungiyar yan canji a Najeriya
Ya farashin kayan masarufi yake a yankunan ku??
ALJANNAR DUNIYA: Ku dubi muhallin masallacin Annur Abuja inda Farfesa, Isah Ali Pantami yake gudanar da Tafsirin Alqur'ani na watan Ramadan.
"Banci bashin Sisin Kwabon Kowa Ba, Kuma Ba'azamu Karba Ba lnsha Allah,
Gwamnan jihar Sokoto Dr Ahmad aliyu ya musanta wasu rahotanni masu cewa gwamnatin Jihar Sokoto Karkashin Jagorancin Gwamna Ahmad aliyu ta ciyo bashi daga bankin duniya har kimanin Dala dubu dari 499 da 472.
Babbar Hanyar dazaka hana kawar matar shigowa gidan ka, matukar baka yarda da tarbiyyar ta ba. -Daurawa
"Idan kana so ka hana ƙawar matar ka zuwa gidan ka kasancewar baka yadda da ita ba, ga hanya mai sauki.
Duk sanda ka shigo gidan kaga tazo, sai ka tambayi matar ka kace, Nikam uwar gida wannan ƙawar taki tana da saurayi kuwa?
In tace me yasa ka tambaya sai kace, naga kuna son juna, dan Allah in ba damuwa tayi min, mai zai hana ki shige min gaba na Auro ta, Kinga shikenan ko yaushe kuna tare ba sai kin sha wahalar neman ta ba.
To in Sha Allahu daga wannan ranar, ka fara bankwana da ganin ta a gidan ka kenan ~ Malam Aminu Daurawa
Rahotanni daga jihar Katsina, na cewa ‘yan bindiga sun sace dalibai 30 a kauyen Kasai na karamar hukumar Batsarin jihar Katsina.
Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi (RTA) yana ɗan fama da rashin lafiya, duba da ga shekaru, inda aka nema da al'ummar Musulmi su yi masa addu'a.”
Barka da Shan ruwa
Daga Wace jaha kuke Bibiyarmu?
Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya tattauna da masu unguwanni na yankin unguwar Dorayi kan rikicin daba da ya kunno kai a baya-bayan nan.
HOTO: 📸: Masarautar Kano
DA DUMI-DUMI: Wani Kansila a kano yaɗauki nauyin karatun yara marayu daga primary zuwa jami'a.
Kansila a Kano ya kudiri aniyar daukar nauyin karatun yara Marayu tun daga Firamare har matakin karshe.
Sabon kansilan riƙo na mazaɓar Achika da ke ƙaramar Hukumar Wudil a jihar Kano, Hon. Bashir Shehu Aliyu Achika, ya samar da kudirin na sa lokacin da yake rabawa marayu 100 tallafin kayan Sallah.
Ya ƙara da cewa " kamar yadda Allah ya bamu ikon dinkawa marayu 100 kayan sallah Allah ya bamu ikon ɗaukar nauyin karatunsu tun daga matakin farko har zuwa ƙarshe".
Yayin taron bada tallafin ga marayu, Bashir Shehu ya ce sun bijiro da tsarin ne domin tallafawa yaran da iyayensu su ka rasu saboda halin rayuwa.
Daga karshe Kansilan ya ce ya sadaukar da aikin ga mai gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, domin Allah ya ƙarfafi gwiwarsa akan manufofin cigaban jihar Kano.
DA ƊUMI ƊUMI: Yadda Wani Matashi Ya Gartsawa Bobrisky Cizo A Ɗan Yatsa.
“An samu wani matashi mai ƙarfin hali daya Gartsawa Bobrisky cizo a ɗan yatsa ana tsaka da shiga ɗakin taro don karramasa wurin miƙa masa babban sakamako na “Award” na zamtowarsa tauraro wurin iya ado, da kyau, wanda ya ci, Tare da doke sauran mata duk a wuri wannan taron a makon data gabata da aka gudanar birnin Ekeja, Jihar Legas, ƙarƙashin wani babban kamfanin shirya fina-finai na Nijeriya fim wanda ya shirya.”
“An hango tauraron kuma fitaccen ɗan daudun yana kokawa kan haka “inda yake nuni cewa; ya samu rauni mafi muni daga wani matashi a cikin tur-mu-tsi-stin mutane dayake zargin ya Gartsa masa cizo a bisa ɗan yatsarsa.”
Mutuwar Zuciya Ce Ta Jefa Matasa da dama Harkar crypto.
Ra'ayin Salisu Idris Waziri
Komai da lokacinsa,
Da wanne kafi amfani a wannan shekarar a azumin bana ?
Gwamnatin Jihar Kebbi ta tabbatar da cewa, rumbun adana abinci da wasu bata gari s**a daka wa wawa mallakin kamfanin Dangote ne, ba na gwamnati ko na 'yan kasuwa ba ne kamar yadda aka ruwaito tun da fari.
Sakataren yada labarai na gwamnan jihar, ya bayyana wa DW cewa yanzu haka ana gudanar da taron gaggawa domin shawo kan lamarin.
SUBHANALLAH: Wani Musulmi ya koma addini Kirista.
Tinubu yayi gwanjon jiragen fadar shugaban kasa 3
Fadar shugaban kasa tayi gwanjon jiragen samanta uku bisa ga rashin kulawa da kashe kuɗi da jiragen ke samu a kullum.
A cewar jaridar The Nation za'a sayar da jiragen fadar shugaban kasa guda 3 cikin bakwai da ake da su.
BABBAN MAGANA; Wannan Shine Mr. Johnathan Lee Mutumin Da Yafi Kowa Kai Kara a Duniya.
Daga: Tahir Muhamoud Saleh
Jonathan har mahaifiyarsa ya shigar da kara a Kotu, inda ya fada ma kotu cewa mahaifiyar ta sa bata bashi kulawa yadda ya kamata ba, akarshe dai Mr Jonathan ya samu nasara akan mahaifiyarsa inda ta biyashi $20, 000.
Bayan wannan nasara ce Mr.Jonathan ya shigar da amininsa, da makocinsa, da wasu daga cikin yan uwansa, da budurwarsa, da yan sanda, sannan ya shigar da karar wani alkali, da wani company karshe har tsohon shugaban Amuruka George Bush ya shigar kara kuma duk ya sami nasara, a takaice dai ya shigar da kara sau 2600.
Daga baya aka sanya sunan Mr. Jonathan Lee a matsayin wanda yafi kowa shigar da kara a littafin tarihin nan na World Guinness Book Record, ganin sunansa acikin wannan tarihi Mr.Jonathan ya shigar da karar Guinness Book of Record gaban kotu bisa rubuta rayuwarsa acikin littafin ba tare da amincewarsa ba, kuma ya samu nasara da kudi har $8, 000, 000
Bayan samun wannan nasara ne wani gidan tv ya nemi Mr Jonathan domin tattaunawa ta musamman, s**a tambaye shi mai yasa yake rayuwa shi kadai bashi da masoyi ko daya, nan take Mr. Jonathan ya fara dariya ya mike tsaye ya fice, yayiwa kotu tsinke inda ya shigar da karar gidan TV bisa cin mutuncinsa akan yi masa tambayoyin da s**a shafi rayuwarsa domin tozartashi inda kotu ta ci tarar gidan TV $50, 000.
Matasa sun fasa rumbunan kayan abinci na gwamnati da ‘yan kasuwa a birnin Kebbi.
Sule Lamido shine ya shafe shekaru 8 a kujerar gwamna jigawa ba tare da cin bashin sisin kwabo ba.
Duk da haka ya mayar da jihar Jigawa tamkar Landan a lokacinsa. Ga wasu muhimman ayyuka da sule Lamiɗo yayi a lokacin yana Gwmna jihar Jigawa.
Ya samar da Network na waya a dukkan kananan hukumomi jihar Jigawa 27
Ya samar da fitilun kan t**i a dukkan kananan hukumomi 27
Ya samar da babbar Jami'ar Tarayya dakedake Dutse
Ya samar da Jami'ar Sule Lamido dake kafin Hausa
Ya samar da filin tashi da saukar jiragen sama a jihar Jigawa
Ya samar da Aminu Kano Treangle
Ya samar da babbar sakateriyar Gwamnati ta jihar Jigawa
Ya samar da sakateriya a dukkan kananan hukumomi 27 na jihar Jigawa
Ya gina asibitoci da dama
Ya gidana makarantun Firamare da sakandare da dama
Ya samar da Damar karatu kyauta ga Ɗalibai a kasashen ketare da gida Najeriya
Ya samar da Ruwan sha a kananan hukumomi 27
Ya samar da sansanin NYSC
Sule Lamido ya rantawa jihar Jigawa bashin Naira biliyan 12 a wanchan lokacin..
Wannan kaɗan ne daga ayyukan Sule Lamido na jihar Jigawa, duk da haka baici bashin ko sisi ba
Daga matashi : Abiyos Roni / X
Jam'iyyar APC ta dakatar da shugaban mata na jam'iyyar APC na jihar Kaduna, biyo bayan nuna goyon bayanta ga Malam Nasiru El-Rufai da s**ar Uba Sani Gwamna jihar Kaduna.
an dakatar da Hajiya Maryam mai rusau ne bayan kalubalantar Uba Sani da Matashiyar yar siyasar tayi. Idan baku manta ba Uba sani ya koka da irin bashin da tsohuwar Gwamnatin Kaduna ta Malam Nasiru El-Rufai.
Ko ya makomar siyasar Uban gida a Najeriya?
Mace ta ƙara girman mazaunai da albarkatun shanu - Halas ne babu laifi - Sheikh Ibrahim Khalil malamin addinin Musulunci a jihar Kano.
Tarihi baya gogewa : Kowa ya san cewa, Malam Nasiru El-Rufai ya juyawa babban ubangidansa a siyasance Obasanjo, da Atiku Abubakar da Sanata Shehu Sani. Baya adede lokacin da su masa rana.
Babban abinda ya haɗa Shehu sani da El-Rufai shine akan ciyo bashi daga babban Bankin Duniya, inda a wanchan lokacin sanata Shehu Sani da Hunkuyi suki amincewa da ciyo bashi don kar aƙakabawa Jihar Kaduna bashin ba gaira ba dalili.
A wanchan lokacin malam Nasiru El-Rufai ya kafa sansanin adawa da Sanata Shehu sani tare da goyon bayan Uba Sani. Yau Allah ya nunawa duniya jajircewar Sanata Shehu sani da hunkuyi. Tun tafiya ba tayi nisa ba ga yaron gidansa ya bijire masa.
Tabbas jajircewar su ba zai tafi a banza ba inji fitaccen mawallafi a shafin X wato Comrd. Abiyos Roni
An yi ruwan sama mai karfi da ƙanƙara a ƙaramar hukumar Gembu sardauna da ke jihar Taraba.
Nasarawa
Kano
3166
Be the first to know and let us send you an email when ZangonLabarai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.
Send a message to ZangonLabarai:
Cikin Sautin Murya A Cikin Hoto Maimotsi: Yadda Dantakarar Neman Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar da Gwamna Tambuwal da Gwamna Okowa Suke Shirya Yadda Za suyi Maguɗin Zaɓe Gobe. Ku saurara a wannan sautin muryar za ku ji har yadda suka shiryar yadda suka haɗa kai da Gwamnan Babban Bankin Najeriya don biyan buƙatar kan su...
Masoyan Attiku ga saƙon waƙarsa nan mai taken "Mucanza Canjin Ƙasa" Duk mai buƙatar cikakkiyar Audio ɗin waƙar yayi magana ta WhatsApp a tura ma shi: +2348160181446 Daga Basiru Gandu
Malamin Da Ya Musuluntar Da Dattijo Mai Shekaru 74 Ya Bayyana Musabbabin Musuluntarsa Bayan Mafarkinsa Da Mala'iku. -Ƙatsina Online
Kwammared Musa Garba Augie, Ya Kira Company MTN Da Suyi Mai Aure.!!! Kwammared, Wai ya batun Auren danaji kana neman Company MTN suyimaka???
Wata Amarya Ta Kashe Mijinta, Yayin Da Yazo Saduwar Aure Da Ita. Wata amarya yar shekara 18 ta kashe mijin ta har lahira, saboda ya kusanceta da niyyar yin saduwar aure da ita. Inda wannan mummunan al’amari ya faru a jihar Bauchi Najeriya, kamar yadda W-Tv ta rawaito. Amaryar mai suna Salma wadda auren nasu bai kai sati biyu da daurawa ba, da bakin ta ta amsa wannan laifi da ake tuhumar ta da shi na kashe mijinta, wanda aka haɗa su auren zumunci tare. Haƙiƙa wannan lamari akwai abin duba a cikin sa, sai dai ba lallai a fahimci asalin maganar ba, tunda shi dai mijin nata ya riga ya mutu balle aji ta bakinsa kamar yanda akaji daga bakinta. Sai dai ita wannan amarya ta faɗa cewa ta daɓa masa wuƙa a kirjinsa ne, a lokacin da yazo gurinta zai raya sunna da ita, wanda kafin aje asibiti yace ga garin ku nan. Yanzu haka zaku iya buɗe bidiyon da ke ƙasa, domin jin cikakken bayanin daga bakin wannan amarya yayin da 'yan jaridu ke fira da ita a cikin bidiyo: