SARAUNIYA NEWS

SARAUNIYA NEWS SARAUNIYA NEWS Sahihiyar Jarida Ce Da Take Kawo Ingantattun Labarai, Siyasa, Rahotanni, Wasanni, Nis

SERAP Ta Maka Gwamnatin Tarayya da NCC A Kotu Kan Ƙarin Kuɗin Waya Daga Yasir Kallah Kungiyar SERAP, mai fafutukar yaƙi ...
26/01/2025

SERAP Ta Maka Gwamnatin Tarayya da NCC A Kotu Kan Ƙarin Kuɗin Waya

Daga Yasir Kallah

Kungiyar SERAP, mai fafutukar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta maka gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya, NCC, a kotu kan ƙarin kashi 50 cikin ɗari na cajin waya, saƙon tes, da data a Nijeriya, inda ta yi zargin cewa ƙarin ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasar, da tsarin doka, kuma babu hankali da adalci a ciki.

A kwanakin nan ne hukumar NCC ta amince da ƙarin kuɗin, wanda ya ɗaga cajin minti ɗaya na waya daga ₦11 zuwa ₦16.5, farashin data 1GB daga ₦287.5 zuwa ₦431.25, sannan saƙon tes na SMS daga ₦4 zuwa ₦6.

Ƙarin kuɗin ya jawo ce-ce-ku-ce da s**a mai yawa ga hukumar NCC ɗin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, inda ita ma ƙungiyar SERAP ta ruga kotu domin a dakatar da ƙarin.

A ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/111/2025 wadda ta shigar a gaban Babbar Kotun Tarayya, SERAP ta koka a kan ƙarin kuɗin ya keta haƙƙin al'umma na ƴancin magana da samun bayanai k**ar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya da dokokin duniya s**a ƙunsa.

SERAP ɗin ta roƙi kotun da ta bayyana cewa ƙarin kuɗin ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Nijeriya da dokokin duniya na ƴancin ɗan'adam, sannan ta dakatar da aiwatar da ƙarin tare da soke shi baki ɗaya.

Boko Haram Ta Hallaka Sojoji 18 da Kwamanda Ɗaya A Borno Daga Yasir Kallah Aƙalla sojoji 19, ciki har da kwamanda ɗaya, ...
26/01/2025

Boko Haram Ta Hallaka Sojoji 18 da Kwamanda Ɗaya A Borno

Daga Yasir Kallah

Aƙalla sojoji 19, ciki har da kwamanda ɗaya, ne s**a rasa ransu a sa'ilin da mayaƙan Boko Haram s**a kai musu farmaki a sansanin sojin da ke Malam-Fatori, ƙaramar hukumar Abadam ta jihar Borno.

Malam-Fatori gari ne da ke kan iyakar Nijeriya da Nijar.

Majiyoyi masu tushe sun yi rahoton cewa maharan sun kai wa bataliyar ta 149 farmakin a ranar Juma'a, 24 ga Janairun 2025.

Majiyoyin sun tabbatar da cewa ƴan ta'addan sun isa sansanin a kan manyan motoci masu bindiga, inda s**a ƙone gine-gine da motocin sojojin a lokacin farmakin.

"Sojoji masu yawa sun samu mummunan rauni yayin da har yanzu ba a ga wasu ba," wata majiya ta bayyana wa gidan talabijin ɗin Channels.

"Kwamandan bataliyar, wanda Laftanal Kanal ne, da wasu manyan hafsoshi guda biyu, ciki har da daraktan lafiyar sansanin, na cikin waɗanda aka kashe a farmakin."

Wannan farmakin ya zo baya ƴan kwanaki kaɗan da ƙungiyar Boko Haram ɗin ta kai mummunan farmaki a kan wani sansanin sojin da ke Damboa, inda ta kashe tarin sojoji da ba a gama tantance yawansu ba.

Kotu Ta Hukunta Budurwa Da Ta Saɓa Alƙawarin Kai Wa Saurayinta Ziyara Wata kotun majistare a Ilesa, jihar Osun, ta umarc...
25/01/2025

Kotu Ta Hukunta Budurwa Da Ta Saɓa Alƙawarin Kai Wa Saurayinta Ziyara

Wata kotun majistare a Ilesa, jihar Osun, ta umarci wata budurwa mai suna Rhoda Audu da ta biya saurayinta mai suna Eru Dupe Naira 150,000 a matsayin diyya sak**akon karɓar Naira 3000 da ta yi a wajensa a matsayin kuɗin motar kai masa ziyara amma daga ƙarshe ta cinye kuɗin tare da saɓa alƙawarin zuwa.

An fara samun saɓanin a lokacin da Eru Dupe ya tura wa Rhoda kuɗin motar, inda ita kuma daga baya ta kashe wayarta tare da ƙin zuwa. Ganin cewa ta damfare shi ne ya ɓata masa rai, inda kai-tsaye ya kai ƙara ofishin ƴan sandan Ayeso, su kuma ƴan sanda ba su yi ƙasa a gwiwa ba s**a je s**a kamo Rhoda sannan s**a gurfanar da ita a kotu.

Yayin gabatar da shari'ar, Eru ya gabatar wa da kotun shaida, ciki har da shaidar tura kuɗin ta waya da kuma saƙonnin WhatsApp tsakanin shi da Rhoda.

A hukuncin da ta yanke, Mai Shari'a Okogun Oludare ta umarci Rhoda da ta biya Eru Naira dubu ukunsa da kuma ƙarin Naira 100,000 ta laifin saɓa yarjejeniya, da kuma ƙarin wata Naira 50,000 a matsayin diyyar sa shi a cikin damuwa.

Kotun ta kuma jaddada cewa ta yanke hukuncin domin ya zama izina ga masu irin wannan halin cin amanar.

– Yasir Kallah

TUNAWA DA GWARZO Daga Muhammad Saliadeen CisseA ranar 25 ga watan Junairu 2017. Yakubu Muhammad Fannami ɗan aji 1 wato S...
25/01/2025

TUNAWA DA GWARZO

Daga Muhammad Saliadeen Cisse

A ranar 25 ga watan Junairu 2017. Yakubu Muhammad Fannami ɗan aji 1 wato SS1 a makantar (Darussalam Science and Islamic Academy) ya ceci rayukan jama'a masu yawa a wani Masallaci da ke Kaleri a jihar Borno.

A inda yayi kukan-kura ya tunkari yar kunan bakin-kake da ta nufi Masallacin yayin da mutane ke tsaka da Ibada, a In da bam din jikanta ya tarwatse tare da shi, ya ceci rayukan wadanda suke cikin Masallacin.

Allah Ya jiƙan Yakubu Muhammad Fannami.

25/01/2025

Malamai Na Ci Gaba Da Yi Wa Shugaban Izala Sheikh Bala Lau Raddi Akan Taron Bikin Alkur'ani

DA ƊUMI-ƊUMI.....Shugaban ƙasa Ahmad Bola Tinubu ya naɗa Shugaban jam‘iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje  zai rike mukamin...
24/01/2025

DA ƊUMI-ƊUMI.....

Shugaban ƙasa Ahmad Bola Tinubu ya naɗa Shugaban jam‘iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje zai rike mukamin shugaban hukumar gudanarwa wato Board Chairman na hukumar FAAN mai lura da tashoshin jiragen sama.

24/01/2025

Tarihin Asalin Bikin Alkur'ani (Qur'an Festival) Daga Bakin Sheikh Ahmad Gumi

An Fasa Ɗaura Aure Saboda Angon Yaki Saya wa Amarya Waya- Ƙawar Amarya Ta aure Angon Daga: Abubakar Sadeeq ShangaA ranar...
29/10/2024

An Fasa Ɗaura Aure Saboda Angon Yaki Saya wa Amarya Waya

- Ƙawar Amarya Ta aure Angon

Daga: Abubakar Sadeeq Shanga

A ranar 26/10/2024 aka yi wani abin mamaki a garin Shanga dake jihar Kebbi wata yarinya mai suna Sadiya ta fasa auren saurayinta saboda ya ƙi saya mata waya ta Naira Dubu Ɗari Da Hamsin (150, 000)

Jama'a sun hallara domin ɗaurin aure, kwatsam sai ga labarin amaryar ta fasa auren saboda angon yaki ya saya mata waya.

Kafin Auren al'ummar karamar hukumar mulki ta Shanga sun sa dokar wajibi sai an gwajin jini (Test) ga angon da kuma amarya domin tabbatar da lafiyar su.

Amaryar tayi amfani da wannan damar tace ita ba zata je awon ba sai angon ya saya mata waya sannan zata je wurin awon kuma ita kaɗai ake jira a kawo awon a ɗaura auren.

Angon kuma ba shi da halin sayen wayar ga lokacin na kurewa, kawai sai amaryar ta yanke hukuncin idan babu wayar ita ta fasa auren kuma haka ya faru.

Cikin ƙawayen amaryar wata tace idan shi angon ya amince ta yarda a ɗaura auren da ita. Kuma abin mamaki shine ita ƙawar amaryar sunan su daya da amaryar watau (SADIYA)

Yan uwan ƙawar amaryar duk sun yarda sun amince kuma an ɗaura aure.

Uwar marayun shanga Hajiya. Saudatu Abdullahi Shanga, uwa ga ango ta ɗauke ma uwayen amaryar nauyin kayan ɗaki gaba ɗaya kuma ta ba amaryar kuɗi Naira Dubu Hamsin (50k) idan taje gidan mijin ta ta nemi sana'a domin ta taimaka wa mijinta.

Tsohuwar ƴar shekaru 70 a duniya Jivunben Rabari, ta haifi shantalelen jinjiri a Indiya.Prince Amoeva
11/10/2024

Tsohuwar ƴar shekaru 70 a duniya Jivunben Rabari, ta haifi shantalelen jinjiri a Indiya.

Prince Amoeva

17/09/2024

BARI CELE: MAWAKIN TIKTOK YA RASU

07/09/2024

TINUBU NA SON MU DA ALHERI ANA BIN SA DA SHARRI

*Ba da saninsa aka ƙara kuɗin man fetur ba.

A wannan bidiyo Sheikh Yahaya Jingir ya bayyana yadda maƙiya maƙiya Muslim-Muslim ke shirya wa shugaban ƙasa Bola Tinubu maƙarƙashiya.

Abba Gida-gida ya gwangwaje Dattijo Dattijon nan da ya nemi ganin Gwamnan Kano a wani bidiyon da ya karaɗe Social Media ...
01/09/2024

Abba Gida-gida ya gwangwaje Dattijo

Dattijon nan da ya nemi ganin Gwamnan Kano a wani bidiyon da ya karaɗe Social Media ya samu ganawa da Gwamnan Engr. Abba Kabir Yusuf har ma ya bashi kyautar Miliyan Guda tare da alkawarin siya masa gida.

Gwamnan ya kuma bashi tallafin kayan abinci.

📸 Ibrahim Adam

10/08/2024

"Da yawa daga cikin jami'an gwamnati ya dace ace suna garƙame a kurkuku". - Obasanjo

10/08/2024

APCn Kano ta nemi Tinubu ya k**a Jaafar Jaafar, Bulama Bukarti da kuma Ɗan Bello, saboda zargin su da tunzura mutane.

Innalillahi wainna illahi rajuun: Mun samu labarin rasuwar Jarumar fina-finai ta Kannywood Fatima Usman wacce aka fi san...
28/05/2024

Innalillahi wainna illahi rajuun: Mun samu labarin rasuwar Jarumar fina-finai ta Kannywood Fatima Usman wacce aka fi sani da Fati Slow

Daga Prince Amoeva

Margayiya Fati ta yi fice daga masana'ata kwanakin baya

An ruwaito Jarumar ta rasu ne jiya da daddare a Abasha wani gari dake kusa da Sudan.

Mansura Isah wacce ta fitar da labarin rasuwar ta ce "a can za ayi jana'izar ta, amma ana zaman makoki a gidan su dake Unguwa Uku"

Wata yar ƙasar Brazil da ta auri dan tsana har ta haifi yan Ukun biyu   Daga:  Prince Amoeva Kamar yadda wata jarida ta ...
21/05/2024

Wata yar ƙasar Brazil da ta auri dan tsana har ta haifi yan Ukun biyu

Daga: Prince Amoeva

Kamar yadda wata jarida ta rawaito, wata mata yar kasar Brazil mai suna Meirivone Rocha Moraes ta yi ikirarin haifar yan Uku tare da mijinta dan tsana,

Jaridar ta rawaito cewa matar ta ce ta yanke shawarar aurar dan tsanar ne sak**akon ta kasa samun namiji da za ta iya natsuwa da shi, wanda zai riƙe mata amana,

A karshe dai mahaifiyarta ta hada mata dan tsana wanda s**a sanya wa suna Marcelo inda s**a yi soyayya ta aure shi, gashi kuma yanzu sun samu albarkar aure da yan ukun biyu.

Abin al'ajabi da mamaki baya qarewa

Maryam Waziri ba ta rasu ba. A daina yaɗa ƙarya. A yi mata addu'a don Allah.- Rahoton Mujallar FIM
11/05/2024

Maryam Waziri ba ta rasu ba. A daina yaɗa ƙarya. A yi mata addu'a don Allah.

- Rahoton Mujallar FIM

Jarumi Sani Danja da Haj Mansura Isa na gayyatar yan uwa.
04/05/2024

Jarumi Sani Danja da Haj Mansura Isa na gayyatar yan uwa.

Address

Maiduguri Road, Tarauni LGA
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SARAUNIYA NEWS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to SARAUNIYA NEWS:

Videos

Share