Rusdy Media Team

Rusdy Media Team Kasance Da Wanan Shafin Don Ilmantarwa Fadakarwa.

19/10/2024

Miliyoyin Yara ne ke fama da matsananciyar yunwa a G@z@/ falasdinu! Wannan kadan ne daga ciki

@top fans

Rusdy Media Team

Muhimmiyar sanarwa! Da Allah muna neman wani Bidiyo da jagora (H) yace (Isra'ila na burim mamaye falasdinu har da saudiy...
13/10/2024

Muhimmiyar sanarwa! Da Allah muna neman wani Bidiyo da jagora (H) yace (Isra'ila na burim mamaye falasdinu har da saudiyya) please urgent !

11/10/2024

Assalamualaikum ya ahlul wilayati wal basira! Barkanmu da sake zagayowar ranar haihuwar babban gwarzo Shahid Sayyid Ahmad Ibrahim Zakzaky (H).

‏اِنَّا لِلّٰہِ وَاِنَّآ اِلَیْہِ رَاجِعُوْنَA madadin membobin wanan shafi Rusdy Media Team Muna miqa saqon ta'aziyar m...
10/10/2024

‏اِنَّا لِلّٰہِ وَاِنَّآ اِلَیْہِ رَاجِعُوْنَ
A madadin membobin wanan shafi Rusdy Media Team Muna miqa saqon ta'aziyar mu ga Dan uwa abokin aikin mu a wannan shafi Mahdi Yunusa bisa rasuwar da Allah yay wa Yayar sa jiya, Allah ya jiqanta ya sadata da Sayyida Zahra (a.s).

08/10/2024

*WAKE UP AFRICANS!* 🌍
*MU FARKA 'YAN AFRIKA!* 🌍

Qalubalen dake gaban 'yan gwagwarmaya na yankin Africa musamman matasa!

Ku saurara domin jin irin kullin da yahudawa ke dashi a yankin mu na Africa, da kuma irin rawar daya kamata mutaka a matsayin mu na matasa 'yan gwagwarmaya na wannan qarni.

* *
* *
* *
* *

- *Telegram* https://t.me/RusdyMedia
- *WhatsApp* https://whatsapp.com/channel/0029VaJW2tEKbYMVStV5Gw2f
- *Facebook* https://www.facebook.com/profile.php?id=100083971901701

*Rusdy Media*
8/10/2024

Innalillahi wa'inna illahiraji'uإنالله وإنا إليه راجعون مِنَ الْمُؤْمِنِينَ رِجَالٌ صَدَقُوا مَا عَاهَدُوا اللَّهَ عَلَي...
28/09/2024

Innalillahi wa'inna illahiraji'u
إنالله وإنا إليه راجعون
مِنَ الْمُؤْمِنِينَ رِجَالٌ صَدَقُوا مَا عَاهَدُوا اللَّهَ عَلَيْهِ فَمِنْهُم مَّن قَضَى نَحْبَهُ وَمِنْهُم مَّن يَنتَظِرُ وَمَا بَدَّلُوا تَبْدِيلاً

Sister. Duk wanda yazo miki da Soyayya. Idan ba Gwagwarmaya a zancen sa! Kiyi watsi dashi.Jagora Sayeed Qa'eed (H) yace:...
28/09/2024

Sister. Duk wanda yazo miki da Soyayya. Idan ba Gwagwarmaya a zancen sa! Kiyi watsi dashi.

Jagora Sayeed Qa'eed (H) yace: A wannan Marhalan dole suma Sistoci su Nazarci rawar da kowace zata iya takawa, saboda mun ruga da mun shiga ƙarnin Kammala aiki da F***j ɗin Nasara.

Azamar Sistoci a fagen fama da yanda suke bada Fata idan an kallli Salon Tunaninsu, har gobe Intelligence Personal na Isra'ila suna aunasu a barazana Mafi hadari fiye da luguden Missile, Al-burushi da Inter-regional Missile, wannan kaitsaye na karanta akan ku kiyayi wadannan masu baƙaken kayan masu zaman gida, Koya wannan turjiyar daga gare su yake gangarowa inji Security Intellectual personal na MOSSAD, ashe ba zaku hankalta ba cewa a zamanin Premier Starlin Macece tayi sanadin kubutar Alexander.

Kamar yanda a Iran anyi zamanin da Darajar ka da kimar Soyayyar ka a zuciyar Sister ana auna shine da yawan ramin ciwon da yake kafofinka da jikinka, Azamar ka da tunaninka akan Sauyi da Makomar Al'umma, A yau Sistocin Harka Islamiyya Irin wannan salon shine zai kwaceki, idan kuma kinki ki ƙare a rukunin ba'amiyar Sister.

Duk wanda yazo neman zuciyarki, Nutsu ki aunashi da wayewarsa a Fagen yanda yake Nazarin Equation na Gwagwarmaya yau a duniya, Shin? yana kan bigiren kwami da ayyukan fata, yaya yake da fahimtar alakokin Muqawama yau na duniya, meke faruwa a Gabashin Duniya, yaya Nazarinsa yake akan raya ayyukan datse iyakokin Maqiya, ya yake miki zancen Fata da Makomar Zuriyarku, Akan Abuja, Jagora da Harka Islamiyya Menene lisafinsa.

Idan kin Nutsu kin samowa kanki yanci kin Huta! Marhalan da muke shirin shiga yanzu, Sunanta Marhalan Sabon Shafin da zuwan Jarrabawoyi.

Sister in relationship with Brother.

Isihaq yusup Gaya.

* *
* * * *
* *

- *Telegram* https://t.me/RusdyMedia
- *WhatsApp* https://whatsapp.com/channel/0029VaJW2tEKbYMVStV5Gw2f
- *Facebook* https://www.facebook.com/profile.php?id=100083971901701

*Rusdy Media*
28/9/2024

26/09/2024

Dole fa yan uwa saimun Shigo Abuja. JA DA BAYA MATSORACI.

A gane! Spirit na Harka Islamiyya yanzu yana Matakin Global Context! Political Advantages din da Abuja take dashi a tsakanin ƙasashen Yamma da Africa, Yanzu an fara tattauna lamarin Harka Islamiyya a Matsayin ƙarshen Matsalar yankin.

Baka, baki da Uzuri a tsarin gudanarwar jadawalin rayuwarka baka saka lissafin Shigowa Abuja tarukan Harka Islamiyya, ba Matsalar financial Difficulties ne yake da munba, Mental Meltdown ne kawai na rashin sanin a wanne Mataki Motsin Harkar yake yanzu.

Jagora (H) ya faɗa ya kara, ya kuma maimaitawa, JADA BAYA MATSORACI!, Hanyar mu irin ta Husaini ce, Inda ake ruwan Wuta ka kutsa, idan Lissafi ya bada ku labe su shigo ku rufe, A kwama. Me kuma kake sauraro, bayan duk makiyan Hankalin su ya gama tashi.

Tarukkan nan da Muzaharorinnan duk kididdigaggune a Shekara, Banda tsirarun Ribadi masu jiran kota kwana kowa yana da Haqqin Allah akansa cikin Lamarin Abuja.

Ba iya labbaika a furuci zamu tsaya ba, Dole mu amsa masa da jikinmu, Guminmu, Jininmu da ƙwaƙwalwar mu duk su wahala wajen aikata Labbaika a Aiki.

Yanda Abba (H) yayi hijirah dole mu bishi inda yake! Mu taimake shi. Addini ya tabbata.

JA DA BAYA MATSORACI.

Isihaq Yusup Gaya

* *
* *
* *
* *

- *Telegram* https://t.me/RusdyMedia
- *WhatsApp* https://whatsapp.com/channel/0029VaJW2tEKbYMVStV5Gw2f
- *Facebook* https://www.facebook.com/profile.php?id=100083971901701

*Rusdy Media*
26/9/2024

Da "Diqqa" Muke sauraron sa (H).Na rantse da Allah idan aka ce maka  tsakanin Isra'ila da America yawan masu Criticism, ...
21/09/2024

Da "Diqqa" Muke sauraron sa (H).

Na rantse da Allah idan aka ce maka tsakanin Isra'ila da America yawan masu Criticism, Analysis da taking Human Psychological Measure na magana sunkai dari 100, kada ka musa idan aka ce maka sunfi haka masu jujjuyawa da auna Maganar Abba (H) idan yayi. Jagora (H). Ya ruga ya zama The current Utmost Apex VIP na Duniya. Wallahi kenan.

Wanda s**a san abun da s**a sani sun sani, amman har a Cikin maqiya idan Abba (H) yayi jawabi tun a da can ma basa bari ya kwana, wasu Live suke kalla! Akwai Malaman da kulle kansu a daki suke suji yaya ya fassara wancen gurin, da yawa ɗaliban karanta Current Affairs da International relation a jawaban Abba akwai dubun abun da suke nema! Wallahi jiya da yana shimfida a jawabin Maulud, akan wannan Cigaban AI, Human Ever Growth of Technology, da cheap Inovation, Shishigi na dan Adam da yanda ya maida kirkirar Kimmiyya da fasaha makamin nau'in Halakarwa ga ɗan Adam, da Confusion din da yake tsakanin Science da Religion yace wasu Abubuwan ma sai Imam yazo za'a sha Mamaki domin zaka iya yiwa waqi'ar karbala tariyar baya ta dawo ka ganta, akwai amsar falsafar da nafi Shekara biyar ina nema jiya najita Wallahi. Ka runga jin jawabin Abba da diqqa Malam.

Baka da wani amfani a Harkar nan idan ba zakaji Jagora (H) ba.

Ka saurara da lissafin Sanin ya Duniya take ciki, Ɗan Gwagwarmaya dole ka zama wayayye.

Ka saura domin Sanin Addininka da abun daya hau kanka.

Ka kuma saurara da Manufar yin Mudlaqar Biyayya.

Kada ka bari ko waye yayi maka Katanga da jin Mutuminan Jagora (H).

Ka runga tattara Hankalinka ka runga sauraran sa da diqqa, kana Analysis akan ta ina zaka bada naka taimakon.

Allah ka bamu Sabaty.

Isihaq yusup.

* *
* * * *
* *

- *Telegram* https://t.me/RusdyMedia
- *WhatsApp* https://whatsapp.com/channel/0029VaJW2tEKbYMVStV5Gw2f
- *Facebook* https://www.facebook.com/profile.php?id=100083971901701

*Rusdy Media*
21/9/2024

MANZON ALLAH NE SAMFURI ABIN KOYI DON SAMUN MAFITA- Inji Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky a yayin jawabin ranar Mauludin b...
21/09/2024

MANZON ALLAH NE SAMFURI ABIN KOYI DON SAMUN MAFITA

- Inji Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky a yayin jawabin ranar Mauludin bana a Abuja

Daga Ofishin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

“Manzon Rahma (S) shi ne mafi kyawun alami da aka ajiye domin a kwafa. Shi ne samfur wanda kowane zai kwafa. Allah Ta’ala yana cewa: “Kuna da kyakkyawan misali ga Manzon Allah, ga mai kaunar Allah da ranar Lahira.” Wato wanda yake tunanin gamuwarsa da Allah a gobe kiyama, to ya san cewa wannan Manzo shi ne kyakkyawan misali (abin koyi).”

Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky ya bayyana haka ne a yayin da yake jawabin Mauludin Manzon Allah (S) a gaban dimbin al’umma a ranar Juma’a 17 ga Rabi’ul Auwal 1446 (20/9/2024) a garin Abuja.

Shaikh Zakzaky ya kara da bayyana cewa: “Canjin dabi’a shi ne muhimmin abu, kuma shi ke gabanmu, wanda kuma shi ke da wahala. Ka zama mutumin kirki, kana da kyakkyawan misali ga Manzon Allah, shi ne abin koyi. Duk cikanmu ba wanda zai zama kamar shi, ballantana ya fi shi, amma za a dauke shi amatsayin abin koyi kuma abin kwafa.”

Ya kara da cewa: “Lokacin da muke batun hadin kai, batun kawo Annabi (S) a matsayin ‘ramzi’ shi ne babba, saboda shi (Annabi) ne kyakkyawan ‘ramzin’ da za a yi koyi da shi domin haduwa akan abu guda. Duk mu hadu muce waye shugabanmu, jagoranmu; Manzon Rahma (S).”

Yace: “Daidai wannan lokaci, abin da muke karfafa junanmu gabadaya shi ne, mu hadu akan abu guda, sunanmu Musulmi, sunan addininmu Islam, sunan Manzonmu Muhammad (S), abin da ya zo da shi shi ne addini, yarda da abin da ya zo da shi shi ne Musulunci, shi ne kuma za mu tsaya a kai kyam, kuma insha Allahul Azeem tabbas abin nan da suke gudu na tabbatan addini, addinin nan fa zai tabbata! Saboda mene? alkawari ne na Allah, Allah kuma baya saba alkawari.”

Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa, mutane su gama duk kewaye-kewayen neman mafitansu a wurare, a karshe za su dawo ga inda mafitan na hakika yake. “Karshe za ku zo kuce ina mafita? Sai mu ce, to dama mun fada muku, mafita shi ne sakon da Allah ya aiko Manzonsa da shi.” Ya jaddada.

A wani bangaren jawabinsa, Shaikh Zakzaky ya yi tsokaci akan wautan ‘yan sanda bayan budewa taron Arba’in din Imam Husaini (AS) na bana wuta da s**a yi a Abuja. Yace: “wanda s**a yi na kwanan nan, wanda yake dariya zai baka ko mamaki ne ma, don wautan ta cika yawa, shi ne, yadda aka ce, wai folisawa sun ce, wai su wadannan masu jajen sun far musu, wai har sun kashe mutanensu.”

Shaikh Zakzaky yace: “To na san an yi rubuce-rubuce da bayanai (akan hakan a baya), amma abin da nake cewa shi ne, ni abin da na sani, wannan Harkar (ta Musulunci) mun fara ta tun karshen saba’inoni, na tabbatar kuma wanda yake yin I.G yanzu haka a lokacin (da muka fara Harkar) kila yana Firamare ne ma. Kuma wanda yake Kwamishinan ‘Yansanda shi ma kila bai shiga ko Firamare ba. Kuma da yawan ‘yan sanda ko haihuwarsu ma ba a yi ba, don da yawansu ‘yan kasa da shekara 40 ne, kowannensu ya bude ido ne ya gammu muna wannan abin. To yaushe rana tsaka za su canza mana, su ce wani abu muke yi?”

Yace: “Illa iyaka in kwangila aka baka, sai ka yi ka karbi abinka, amma ba yadda za a yi ka iya canza wai duban da ake yi mana, hatta a Abuja, ballantana a duniya, wanda Harkar da muke yi tun kafin a gina Abuja.”

Shaikh Zakzaky ya bayyana yadda ‘yan sandan bayan sun dirarwa ‘yan uwa, s**a kuma bayyana a fili suna fada da addinin Musulunci ne. Yace: “Sun yi wani abu wanda ya nuna baro-baro suna adawa ne da addinin Musulunci; shi ne cire wa mata hijabi. Don shi Hijabi umuni ne na Allah Ta’ala a ayoyin Alkur’ani daban-daban, kuma Sunnah ta tabbatar da shi, kuma ba wani wanda ke musu dangane da matsayin shi a tsakanin Musulmi. Kuma akan cire wa mace Hijabi aka yi rigimar farko (tsakanin Musulmi) da Yahudawan Banu Qainuka (a Madina).”

Ya kara da cewa: “In kuka yi fada da Hijabi, kun yi fada da addinin Muslunci ne, ba da wadansu mutane ba. Da addinin Musulunci ne gabadayansa kuke fada, da Alkur’ani kuke fada, kuma duk Musulmin duniya ya san cewa kuna fada da addini ne.”

Jagora, ya yaddada cewa: “Wannan lokaci namu, lokaci ne da ya kamata ba al’ummar Musulmi kawai ba, dukkanin mutane ya zama sun shiga hankalinsu, su gane meye mafita gare su. Ya zama sun fahimci cewa, in ma za ka rayu ne a doron kasa, baka dauka ma gwadaka ake ba, ka dauka ma nan ne wajen zama, to zaman ma da wahala, kuma wadansu mutane sun dauka ma kansu su saka ku a cikin wahaloli domin su su ji dadi. Kuma lallai dole ka yi tunanin to ina mafita? To ballantana mu da muka san cewa mun zo gidan gwaji ne, ana gwada mu ne, ana kuma gwada mu da juna ne. Mun san cewa lazim ne muna da mafita, mafitan nan kuma shi ne wannan sakon na Allah Ta’ala, wanda ya aiko wannan Manzo. Sakon karshe, dauke da addini cikakke, da shari’a cikakkiya, wanda ba za a yi wata shari’a ta zo ta wuce ta ko ta yi daidai da ita ba, ballantana ace ta fi ta. Ita ce kawai mafita.”

Ya karkare da fata Allah Ya hada kan al’ummar nan a karkashin La’ilaha ilallah. Tare da addu’ar “Allah Ya nuna mana lokacin da tutar La’ilaha illallah za ta filfila a kasar nan, har ya zama komai za a yi sai an ce Allah Ya ce, Manzonsa Ya ce.”





18/RabiuAwwal/1446
20/09/2024

MUZAHARAR MAULIDI MAI TAKEN LABBAIKA YA RASULULLAH A ABUJADaga masallacin Gudu Market, Apo Abuja, muzaharar maulidin Man...
20/09/2024

MUZAHARAR MAULIDI MAI TAKEN LABBAIKA YA RASULULLAH A ABUJA

Daga masallacin Gudu Market, Apo Abuja, muzaharar maulidin Manzon Allah (SAWW) ta yau 17 ga watan Rabiul-Auwal ta gudana yau Jumma'a. Dubunnan ƴan uwa musulmi ne s**a fito dauke da fararen tutocin Labbaika Ya Rasulullah tare da wakokin yabon Manzon Allah (SAWW).

Jim kaɗan da idar da sallan Juma'a a masallacin Gudu Market, yan uwa musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) s**a hau sahun muzaharar maulidin Manzon Allah (SAWW), wanda harkar musulunci ƙarƙashin Jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) take gudanarwa duk ranar 17 ga watan Rabiul-Auwal.

Anyi muzaharar tin daga masallacin Jumma'a har zuwa babban junction na gudu Market kan titin Ahmadu Bello Way, sannan aka rufe muzaharar, anyi muzaharar lafiya an ta shi lafiya. Ga wasu kaɗan daga cikin hotunan muzaharar.

– Asperger
– Isa Charis
20th Sept, 2024

Address

Kano

Telephone

+2347015052819

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rusdy Media Team posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rusdy Media Team:

Videos

Share