Madogara TV/Radio

Madogara TV/Radio Kafar watsa labarai ce mai zaman kanta da aka samar domin yada labarai da rahotanni na gaskiya. Kafar watsa labarai mai hasko labarai masu amfanarwa.
(1)

HOTUNA: Yadda sojoji s**a hallaka ’yan bindiga a yankin ƙaramar hukumar Shanono ta Jihar Kano
03/11/2025

HOTUNA: Yadda sojoji s**a hallaka ’yan bindiga a yankin ƙaramar hukumar Shanono ta Jihar Kano

Jerin Jihohin Arewa Guda 12 Da Amurkà Za Ța Sanyawa Takunkumi Kan Zargin Tauye Hakkìn Addini1-Zamfara.2-Kano 3-Sokoto4-K...
03/11/2025

Jerin Jihohin Arewa Guda 12 Da Amurkà Za Ța Sanyawa Takunkumi Kan Zargin Tauye Hakkìn Addini

1-Zamfara.

2-Kano

3-Sokoto

4-Katsina

5-Bauchi

6-Borno

7-Jigawa

8-Kebbi

9-Yobe

10-Kaduna

11-Niger

12-Gombe.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!!Yanzu mu ke samun labarin rasuwar Malam Nata'ala a cikin daren bayan fama da jinya...
02/11/2025

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!!

Yanzu mu ke samun labarin rasuwar Malam Nata'ala a cikin daren bayan fama da jinya.

Farfesa Sheriff Almuhajir daga jihar Yobe ne ya tabbatar da labarin. Inda ya nuna matuƙar kaɗuwarsa da rsuwar.

Na Bar Shan Sigari Ne Saboda Lare Mutunci Na - Cewa shahararriyar Mawakiya Yemi Alade Shahararriyar mawaƙiyar Nijeriya, ...
02/11/2025

Na Bar Shan Sigari Ne Saboda Lare Mutunci Na

- Cewa shahararriyar Mawakiya Yemi Alade

Shahararriyar mawaƙiyar Nijeriya, Yemi Alade ta baiyana cewa ta dena shan taba sigari ne saboda kare mutuncin ta.

A wata tattaunawa a shirin WithChude da ake watsawa ta yanar gizo, Alade ta ce ta fuskanci cewa shan sigari ya zame mata jiki har tana jin ba daɗi idan ba ta yi ba.

A cewar Alade, duk sanda ta zo kwanciya sai ya zuzzuki sigari, inda ta ce bata samun damar sha da rana saboda shiga cikin mutane.

A cewar ta, ɓoye shan sigari a bainal jama'a ne ya sa ta ga cewa gwara ma ta yarda ƙwallon mangwaro ta huta da ƙuda.

Daily Nigerian

Farfesa Maqari ya Kai Ziyarar Haɗin Kan Malamai ga Sheikh Zakzaky a AbujaA wani yunƙuri na ƙarfafa haɗin kai tsakanin ma...
02/11/2025

Farfesa Maqari ya Kai Ziyarar Haɗin Kan Malamai ga Sheikh Zakzaky a Abuja

A wani yunƙuri na ƙarfafa haɗin kai tsakanin malamai da mabiya addinin Musulunci, Farfesa Ibraheem Maqari tare da tawagarsa sun kai ziyara ga Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), a gidansa da ke Abuja, ranar Lahadi 2 ga watan Nuwamba 2025. A cikin tawagar Malaman akwai Shaikh Nura Khalid da sauran Malamai.

Ziyarar ta mayar da hankali ne kan buƙatar haɗin kai, fahimtar juna da kusanci a tsakanin malamai daga bangarori daban-daban na addinin Musulunci, domin ƙarfafa zumunci da kawar da sabani a tsakanin al’umma.

Rahoton da ya fito ne daga ofishin Jagora, ya labarta cewa Sheikh Zakzaky (H) ya yi maraba da wannan yunƙuri, inda ya yabawa ƙoƙarin Farfesa Maqari da tawagarsa wajen ganin an samu haɗin kai da zaman lafiya a tsakanin malamai da mabiya addini.

A yayin ziyarar, Sheikh Zakzaky ya ƙarfafa buƙatar ci gaba da irin waɗannan tattaunawa, yana mai addu’ar alkhairi da nasara ga dukkanin ɓangarorin da ke neman haɗin kai da fahimtar juna.
Ziyarar ta Farfesa Maqari ta zo a lokaci mai muhimmanci, inda ake ci gaba da kira ga haɗin kan Musulmi a fadin duniya da kuma addu’a ga al’ummar Falasdinu da shahidan Musulunci.

Fityanul Islam ta karrama wasu muhimman mutane  a AbujaDaga Ibrahim Shuiabu SudduKungiyar Fityanul Islam of Nigeria, res...
02/11/2025

Fityanul Islam ta karrama wasu muhimman mutane a Abuja

Daga Ibrahim Shuiabu Suddu

Kungiyar Fityanul Islam of Nigeria, reshen babban birnin tarayya Abuja, ta gudanar da taron mauludi da ta saba yi duk shekara da kuma karramawa ga wasu fitattun mutane da ke taimaka wa Addinin Musulunci.

Taron ya gudana ne a ranar Lahadi 19/10/2025 a babban masallacin kasa da ke Abuja.

Daga cikin waɗanda s**a samu lambar girmamawar akwai Mataimakiya ta masamman ga shugaban kasa kan harkar redio da yada labarai
Sayyida Rahma Abdulmajid.

Kungiyar ta bayyana cewa an zaɓi Rahma Abdulmajid ne bisa la’akari da irin rawar gani da take takawa wajen ci gaban Najeriya musamman ma arewacin ƙasar, tare da jajircewarta wajen ɗaukaka addinin Musulunci.

Rahma Abdulmajid ta kuma shahara wajen:

Tallafa wa marayu,
daukar nauyin karatun matasa da masu buƙata, ta masamman da bayar da gudummawa a fannoni daban-daban

Kungiyar ta yaba wa irin wannan ƙoƙari, tana mai fatan hakan zai ƙara zuga sauran ‘yan uwa musulmi wajen bada gudummawa ga al’umma da addini.

✍️SAUKI NA ZUWA

Zaben Kananan hukumomi a Neja; Yan sanda sun harbi mutane ukuDaga Awwal Umar KontagoraYau daya ga watan Nuwanban shekara...
02/11/2025

Zaben Kananan hukumomi a Neja; Yan sanda sun harbi mutane uku

Daga Awwal Umar Kontagora

Yau daya ga watan Nuwanban shekarar nan ne hukumar zabe ta jihar Neja ta ke gudanar da zabukan kananan hukumomi ashirin da biyar na jihar. Zaben wanda ya kunshi shugabannin kananan hukumomi da kansulolin su.

Tunda farko kafin rufe yakin neman zabe a karamar hukumar Chanchaga an samu rashin fahimta tsakanin wasu matasan da s**a fito daga gundumar mazabarsa na Tudun-South, inda har ta kai ga fitar da mak**ai tsakanin matasan da wasu yan vigilantee, da ya kai ga satar wani dan vigilatee a hannu, kan haka jami'an yan sanda s**a gudanar da atisayen musamman a wasu unguwannin da ake tsammanin za a samu tashin hankali.

Bayan kai ruwa rana a yankunan wasu kananan hukumomi na rashin kai kayan zabe kan lokaci wanda daga baya kayan sun isa runfunar zabe dan cigaba da gudanar da zabe.

A karamar hukumar Kontagora kuwa da tayi shuhura wajen adawa musamman duba da yadda yan bindiga s**a daidaita yankunan karkaru, hakan bai hana gudanar da zaben ba.

Zaben wanda aka gwabza tsakanin yan takarkarun jam'iyyar APC, PDP da SDP ya samu bullar jama'a duk da cewar yan adawa da dama sun koka kan irin cin zarafin da yan bangar siyasa su kai masu.
A mazabar Central Word kuwa, mutane uku ne s**a sha harsasai, yayin da mutum daya ya rasa ransa, biyu kuma suna kwance gadon asibiti.
Ganin yadda lamarin ya kai ga harbi da bindiga yasa jama'a da dama nuna takaicinsu tare da yin Allah-waddai da lamarin.

Kungiya ta shigar da ƙara kan NBC da Arewa24 bisa zargin karya dokar yaɗa shirye-shirye.Wata kungiya mai zaman kanta mai...
01/11/2025

Kungiya ta shigar da ƙara kan NBC da Arewa24 bisa zargin karya dokar yaɗa shirye-shirye.

Wata kungiya mai zaman kanta mai suna Islamic Research and Da’awa Foundation da ke Abuja ta shigar da ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, kan gidan talabijin na Arewa24 da kuma Hukumar Kula da Kafafen Yaɗa Labarai ta Ƙasa (NBC), bisa zargin karya ƙa’idojin Nigeria Broadcasting Code.

Kungiyar ta ce shirye-shiryen gidan talabijin ɗin na ɗauke da abubuwan da “ba su dace ba” tare da “sabawar al’adun Hausawa da dabi’un Arewa.”

A cikin wata wasiƙa mai kwanan watan 30 ga Oktoba, 2025, wacce lauyoyin kungiyar A. A. Hikima & Co. s**a aika wa Daraktan NBC na Kano, ta yi amfani da dokar Freedom of Information Act (2011) domin neman bayanai kan matakan da hukumar ta ɗauka kan gidan talabijin ɗin.

Rahoton ya ce koken ya fi mayar da hankali ne kan shirye-shiryen “Mata A Yau” da “H-Hip Hop”, waɗanda ake zargin suna ƙunshe da “abubuwa na rashin kunya, masu tayar da hankali, da kuma sabawa al’adun Arewa,” wanda hakan ke sabawa tanade-tanaden Nigeria Broadcasting Code (bugu na 6).

A cewar wasikar da lauya A. A. Hikima, Esq. ya sanya wa hannu, shirye-shiryen sun jawo “matsananciyar s**a daga shugabanni da malamai masu daraja.”

Kungiyar ta kuma zargi masu gabatar da shirin Mata A Yau da cewa “a lokuta da dama suna karfafa mata da su ɗauki doka a hannunsu wajen magance matsalolin aure,” wanda, a cewarta, “yana sabawa koyarwar addini da al’adun yankin.”

Duk da koke-koken jama’a da na wasu hukumomi, kungiyar ta bayyana cewa NBC ta “gaza ɗaukar matakan ladabtarwa ko bincike yadda doka ta tanada,” bisa dokar National Broadcasting Commission Act, Cap N11, Laws of the Federation of Nigeria, 2004.

Kungiyar ta bukaci NBC da ta samar da cikakkun bayanai cikin kwanaki bakwai, waɗanda s**a haɗa da:

1. Bayani kan koke-koken da aka taɓa samu game da shirye-shiryen Mata A Yau da H-Hip Hop ko wani shirin Arewa24.

2. Rahoton bincike da sak**akon hukunci, idan akwai.

3. Kwafin takardun gargadi ko takunkumi da aka taɓa aikawa gidan talabijin ɗin.

4. Matsayin izinin da aka bayar na watsa shirye-shiryen da abin ya shafa.

Kungiyar ta gargadi cewa jinkiri ko ƙin bayar da bayanan zai zama karya tanade-tanaden dokar Freedom of Information Act (2011), kuma hakan na iya zama hujjar shigar da ƙara a kotu don tilasta bin doka.

“Za mu yaba da gaggawar amsawar ku, kuma za mu karɓi bayanan da aka nema a ofishinmu ko ta hanyar imel,” in ji ƙarshen wasikar.

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji a cikin wasu motocin bas Toyota guda biyu da asuba, a titin Itobe zuwa Ajegwu-A...
01/11/2025

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji a cikin wasu motocin bas Toyota guda biyu da asuba, a titin Itobe zuwa Ajegwu-Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu ta jihar Kogi, a hanyarsu ta zuwa Abuja.

📸: Tijani Labaran

Hutunan Yadda Matar Gwamnan Jihar Katsina Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa Ta Jagoranci Bikin Ranar Masu Cutar Kansar Mama Ta D...
01/11/2025

Hutunan Yadda Matar Gwamnan Jihar Katsina Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa Ta Jagoranci Bikin Ranar Masu Cutar Kansar Mama Ta Duniya A Katsina

‎Matar Gwamnan Jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Umar Radda, wacce aka fi sani da Zinariyar Gwagwaren Katsina, ta jagoranci gagarumin gangamin bikin Ranar Tunawa da Masu Cutar Kansar Mama ta Duniya a jihar Katsina, a wani shiri mai cike da wayar da kan Mata kan ilimantarwa ga Mata da al’umma baki ɗaya.

‎Taron, wanda ya samu halartar mata daga sassa daban-daban na jihar, ya mayar da hankali kan wayar da kan jama’a musamman mata kan muhimmancin duba lafiyar mama akai-akai, domin gano matsaloli tun kafin su tsananta da kuma kare lafiyarsu daga cutar kansar mama.

‎A cikin jawabin ta, Hajiya Fatima Dikko Radda ta jaddada cewa,

‎“Gano cutar tun da wuri na iya ceto rai, kuma hakan yana bukatar ilimi, kulawa da karfafa gwiwar mata su rika zuwa asibiti don binciken lafiyarsu.”

‎An fara gangamin ne daga Tsohon Gidan Gwamnatin Jihar Katsina, inda aka gudanar da tafiya mai ɗauke da sakonnin wayar da kai, sannan aka kammala taron a Filin Wasannin Muhammadu Dikko, inda daruruwan mata, matasa da kungiyoyi s**a halarta cikin nishadi da sha’awa.

‎A yayin taron, an gudanar da gwajin cutar kansar mama kyauta ta amfani da na’urori na zamani, tare da bayar da shawarwari daga kwararrun likitoci kan hanyoyin kariya da gano cutar tun da wuri.

‎Wannan gangami ya gudana ne da haɗin gwiwar Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Katsina, cibiyoyin lafiya masu zaman kansu, da ƙungiyoyi masu rajin kare lafiyar mata, domin ƙara wayar da kai da rage yawan mace-macen da ke da nasaba da kansar mama.

‎Ranar 15 ga watan Oktoban kowace shekara ne sai, Majalisar Dinkin Duniya ta ware a matsayin Ranar Tunawa da Masu Cutar Kansar Mama ta Duniya, kuma Katsina ta gudanar da nata bikin a ranar Alhamis, 30 ga watan Oktoba, 2025, ƙarƙashin jagorancin Zinariyar Gwagwaren Katsina, wadda take nuna alama ta tausayi, jajircewa da kishin lafiyar mata a jihar.

‎“Lafiyar mace ginshiƙi ce ta ƙasa. Idan mata sun kasance lafiya, al’umma ma zata kasance lafiya,” in ji Hajiya Fatima Dikko Radda.

‎Taron ya zama abin yabo da jan hankali ga mata, matasa da kungiyoyin al’umma da dama, inda aka yaba da irin jajircewar matar gwamnan wajen kare lafiyar mata da ƙarfafa su wajen kula da jikinsu.

Yanzu Yanzu: Wargaza Yunkurin Juyin Mulki A Guinea-BissauSojojin kasar ta Guinea-Bissau s**a ce an yi yunkurin kifar da ...
31/10/2025

Yanzu Yanzu: Wargaza Yunkurin Juyin Mulki A Guinea-Bissau

Sojojin kasar ta Guinea-Bissau s**a ce an yi yunkurin kifar da gwamnatin Umaro Sissoco Embalo ne ta hanyar amfani da wasu sojoji.

Sun kara da cewa an k**a wasu manyan hafsoshin soji kafun fara yakin neman zabe.

Mataimakin Shugaban Rundunar Sojin kasar, Janar Mamadu Ture, ne ya tabbatar da wannan yunkurin a kasar da ke yammacin Afirka wacce za ta gudanar da zaben shugaban kasa a ranar 23 ga Nuwamban 2025.

Ku shiga domin kallon shirin
30/10/2025

Ku shiga domin kallon shirin

Wannan shirin zai rika zuwa maku a duk ranar Alhamis, da misalin karfe 8 na dare a wannan tashar tamu. #...

Address

Gwargwaje Birnin Gwari Road Opposite Old KAEDCO Office, Zaria
Kaduna
800102

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Madogara TV/Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Madogara TV/Radio:

Share