Dokin kara 24

Dokin kara 24 Kafar watsa labarai a cikin harshen hausa

Arewa Ba Mu Shirya Wa Goben Mu Ba, Duk Abinda Zai Amfane Mu Ba Shi Muke Sawa A Gaba BaDaga Nafi'u Dawaki Bari ku ji....F...
03/02/2025

Arewa Ba Mu Shirya Wa Goben Mu Ba, Duk Abinda Zai Amfane Mu Ba Shi Muke Sawa A Gaba Ba

Daga Nafi'u Dawaki

Bari ku ji....

Farfesa Usman Yusuf, ya gina rayuwa mai matuƙar kyau cikin daraja da kare mutuncin kai, ya yi rayuwar karatu da aiki a sassa mai yawa na duniya, daga baya an nemi ya dawo gida domin bada gunmawa, ya dawo ya tsaya tsayin daka domin kare mutuncin al'ummar Arewa. Wannan ya ja masa baƙin jini a wajen masu mulki, ƙarshe s**a k**a shi s**a ɗaure bisa zalunci.

A gefe kuma 'yan TikTok da ba su tsinanawa rayuwarku komai ba ballantana rayuwar wasunsu, saboda kawai sun gama shiriritarsu ƙarshe sun dawo sunyi aure, maganar sai yawo take, ko ina ka duba sai tattaunawa ake k**ar wani abu mai muhimmanci.

Shin da wannan shirmen, rashin wayewa da rashin sanin mutuncin kai muke tunanin samun nasara?

Su fa yanzu su Sowore IG na 'yan sanda s**a sako a gaba kuma suke burin sai sun kai shi ƙasa, amma mu an bar mu da labaran su G-fresh, Murja Kunya da sauran shiririya. Arewa kenan!

Allah yasa mu gane.

Idan 'Yan Izala S**a Yi Wasa To Ruĝujêwarșu Ta Zo, Sabøda Na Ga Dan Shéikh Dahiru Bauchi Yana Ta Yawo Akan An Ba Shi Mat...
01/02/2025

Idan 'Yan Izala S**a Yi Wasa To Ruĝujêwarșu Ta Zo, Sabøda Na Ga Dan Shéikh Dahiru Bauchi Yana Ta Yawo Akan An Ba Shi Matsayin Shugaban Sasanta Musulman Nijeriya, Inda Yake Ta Bin Malaman Izala Yana Zama Da Su Har Suna Wa'azi Tare, Ka Ga Kenan Idan Aka Hade Babu Wa'azin S**ar Bidi'a, Inji Sheik Dutsen Tanshi

Me zaku ce?

An zaɓi Limamai 7 da ake sa ran za su jagoranci Sallar Taraweehi a masallacin Harami na Makkah, a watan Ramadan. Allah y...
01/02/2025

An zaɓi Limamai 7 da ake sa ran za su jagoranci Sallar Taraweehi a masallacin Harami na Makkah, a watan Ramadan. Allah ya ƙarawa Annabi SAW daraja.

1- Sheikh Abdur Rahman As Sudais
2- Sheikh Maher Al Muaiqly
3- Sheikh Abdullah Juhany
4- Sheikh Bandar Baleelah
5- Sheikh Yasir Dawsary
6- Sheikh Badr Al Turki
7- Sheikh Waleed Al Shamsan

Wannan ita ce Dr Tiwa Savage shahararriyar Mawakiya a yankin Kudu Najeriya. Dubi yanda ta fito wata santaleliyar hadaddi...
31/01/2025

Wannan ita ce Dr Tiwa Savage shahararriyar Mawakiya a yankin Kudu Najeriya. Dubi yanda ta fito wata santaleliyar hadaddiyar Sarauniya yayin da ta yi shiga irin tamu ta masu k**ala.

Da sun san irin dadin da ke cikin suturta jikinsu da tuni sun yadda kwallon Mangoro sun huta da kuda.

Matan Hausawa dake sha'awar kwaikwayonsu ku sani babu wata burgewa a ciki nuna tsaraici sai lalaci da la'anci kuma wutace za ta ci.

DA DUMI DUMINSA: Akwai lokacin da Naje wajan shugaban ƙasa Bola Tinubu naga ya jiƙa garin kwaki yanaci, Sabida Tausayin ...
30/01/2025

DA DUMI DUMINSA: Akwai lokacin da Naje wajan shugaban ƙasa Bola Tinubu naga ya jiƙa garin kwaki yanaci, Sabida Tausayin Talakawa, har Zuwa yanzu Tinubu garin kwaki yake Ci Baya iya cin Abinci Mai rai da Lafiya, inji Ganduje

Nayi matukar mamaki da naga kalar gidan shugaban ƙasa Bola Tinubu yake ciki a yanzu dake Legas.

Bayan Gwaje-Gwajen, Cututtukan Ķanjàmau, Zuciya, Da Na Jini Da Ake Yi Kafin Aure, Ya K**ata A Kara Da Na Tabin Hànkali D...
27/01/2025

Bayan Gwaje-Gwajen, Cututtukan Ķanjàmau, Zuciya, Da Na Jini Da Ake Yi Kafin Aure, Ya K**ata A Kara Da Na Tabin Hànkali Da Na Shan Miyagun Kwayoyi, Ra'ayin Fatima 'Yar Mallawa, Zaria

Me za ku ce?

BABBAR MAGANA: Dillalan man fetur na shawarar daina sayen man daga matatar Dangote domin wanda ake shigowa da shi daga w...
27/01/2025

BABBAR MAGANA: Dillalan man fetur na shawarar daina sayen man daga matatar Dangote domin wanda ake shigowa da shi daga waje ya fi arha.

Ƴansanda sun fake da barazanar tsaro ne kawai don su hana Maulidin Tijjaniyya - Gwamnatin Kano Gwamnatin Jihar Kano ta z...
25/01/2025

Ƴansanda sun fake da barazanar tsaro ne kawai don su hana Maulidin Tijjaniyya - Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta zargi ƴasanda da kokarin hana taron addini na na dariƙar Tijjaniyya na shekara-shekara a jihar, inda ta ƙaryata cewa akwai barazanar tsaro a jihar k**ar yadda rundunar ƴansanda ta sanar a yau a jihar.

Da ya ke jawabi ga manema labarai a Fadar Sarkin Kano a yau Juma’a, Kwamishinan yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya musanta gargadin da ‘yan sanda s**a fitar tun da fari.

Waiya ya ce rundunar ƴansanda kawai ta fake da barazanar tsaro ne don ta hana gudanar da taron Mauludin na Tijjaniyya na kasa, wanda ya ce an kwashe kisan shekaru 40 ana gudanar da shi.

Kwamishinan ya bayyana cewa, duk da matakin da ƴansanda s**a dauka, Mauludin zai gudana k**ar yadda aka tsara a filin wasa na Kofar Mata, yana mai tabbatar wa wadanda ke son halarta cewa gwamnatin jihar ba za ta bari a samu wata matsala ba.

24/01/2025

"Sojojin ƙasar Nijer sun k**a Bello Turji a kan iyakar Illela da Ƙonni"

🤚

Muna lashe zaɓe a shekarar 2027 za mu ɗaure Kwankwaso da Abba gida-gida na tsawon shekaru 40 a gidan yari ~ Abdullahi Ab...
23/01/2025

Muna lashe zaɓe a shekarar 2027 za mu ɗaure Kwankwaso da Abba gida-gida na tsawon shekaru 40 a gidan yari ~ Abdullahi Abbas

Shugaban APC na jihar kano ya ƙara da cewa "Ko Goro ba zai fi Abba Gida-gida ɗauruwa a wajenmu ba, da shi da me gidansa idan ya sauka daga mulki, har ƙiri-ƙiri sai mun kai shi."

Me za ku ce?

WUYA KO DA MAGANI, BA DADI: An Jiyo Muryar Bello Tuŕji A Raunace Yana Kiran Yaransa Su Kawo Masa Daukin Gaggawa A Yayin ...
20/01/2025

WUYA KO DA MAGANI, BA DADI: An Jiyo Muryar Bello Tuŕji A Raunace Yana Kiran Yaransa Su Kawo Masa Daukin Gaggawa A Yayin Fàŕmàkin Da Sojoni S**a Kai Mafakarsa. Amma Babu Wanda Ya Kawo Masa Daukin Saboda Su Ma Ta Kansu Suke

A yayin sabon farmakin, an tarwațsa sansanin dan ta'àďďan tare da ķashè dansa da kuma yaransa da dama.

Hukumar tace finafinai ta dakatar da mawaki da jarumai mata 2 Hukumar Tace Fina-Finai ta Jihar Kano ta dakatar da mawaki...
20/01/2025

Hukumar tace finafinai ta dakatar da mawaki da jarumai mata 2

Hukumar Tace Fina-Finai ta Jihar Kano ta dakatar da mawakin Kannywood, Usman Sojaboy da wasu jarumai biyu, Shamsiyya Muhammad da Hasina Suzan daga shiga duk wasu harkoki na masana’antar fina-finan Hausa a jihar.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar dauke da sa hannun mai magana da yawunta, Abdullahi Sani Sulaiman a Kano a yau Litinin, ta ce ta yanke hukuncin ne biyo bayan wani faifan bidiyo da aka yi ta yadawa inda ake zarginsu da aikata alfasha.

Sulaiman yace ayyukan sun sabawa addini da al'adar jihar Kano.

A cewarsa, hukumar ta dauki matakin ne bisa korafe-korafe da jama’a s**a yi na cewa a dauki mataki kan yan Kannywood din.

Ya ce babban sakataren hukumar, Abba El-Mustapha, ya umurci sashin tantancewa da su tabbatar da cewa Sojaboy da jaruman biyu ba su shiga wani shiri na Kannywood ba.

Cikakken labarin yadda aka nemi a hallaka Sheikh Murtala Bello Assada sokoto Inna Lillahi Wa'inna Ilaihi raji'un!Yawansu...
17/01/2025

Cikakken labarin yadda aka nemi a hallaka Sheikh Murtala Bello Assada sokoto Inna Lillahi Wa'inna Ilaihi raji'un!

Yawansu ya kai kimanin mutane 10 a cikin shiga irinta burtu ba tare da ana ganin fuskokinsu ba, dauke da miyagun mak**ai sun kai farmaki a gidan malamin addini Sheikh Murtala Bello Assada Sokoto a tsakiyar daren ranar talata, yayin da malamin ke lura da abinda ke shiga da fice ta na'urar CCTV.

Wani daga cikinsu ne ya fara haurawa ta bayan ginin gidan, domin bude kofa a lokacin da sauran s**a zagaye gidan, daidai lokacin da suke kokarin halaka mai gadi bayan dayan ya haura, yan bindigar s**a ji ketowar sautin harsashi da karar bindiga na fitowa ta koina wanda ya razanasu su ka ranta a cikin na kare tare da shiga motocin da s**a zo dasu bada shiriba.

Tuni dai jami'an tsaro a Jihar Sakkwato sun dukufa ga yin bincike don gano yadda lamarin yake, sai dai a wasu bayanai an nuna cewa " Na'urar CCTV ta nade wasu daga cikin bayanan maharan, inda ake tsammanin bayan kammala binciken jami'an tsaron za'a gano yadda lamarin yake.

DA ƊUMI-ƊUMI: Wata babbar kotu a Minna a jihar Neja ta yanke ma wata mata, Amina Aliyu da ‘ƴar uwarta, Aishat Mohammed h...
17/01/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Wata babbar kotu a Minna a jihar Neja ta yanke ma wata mata, Amina Aliyu da ‘ƴar uwarta, Aishat Mohammed hukuncin k!s@ ta hanyar rataya, bisa laifin kashe uwar gidanta, Hafsat Fatima Aliyu.

'Yan Sanda Sun K**a Wani Sojan Nijèŕiya Da Kullin Kayan Màyè'Yan sanda sun k**a Sojan Nijeriya mai suna Kofur Sani Aminu...
16/01/2025

'Yan Sanda Sun K**a Wani Sojan Nijèŕiya Da Kullin Kayan Màyè

'Yan sanda sun k**a Sojan Nijeriya mai suna Kofur Sani Aminu wanda yake da lambar aiki da rundinar sojin Nijeriya k**ar haka 70/11481L.

'Yan sanda sun k**a Kofur Sani Aminu yana dauke da sinadarin haramtattun kayan maye da ake kira Canadian-Loud wanda Gwamnatin Nijeriya ta haramta shigo da shi cikin kasa saboda haďarinsa

A tunaninku me ya k**ata Gwamnatin Nijeriya ta yi wa jami'an tsaronta domin hana su aikata irin wadannan laifuka?

Albashinsu ne ya yi kadan, ko kuma mece ce matsalar a tunaninku?

Daga Datti Assalafiy

ME ZA'AYI DA BARAWO!!!Daga Kasuwar Kauran Bauchi New GSM Village Bayan alkawarin da jajircewa na shugabannin Kasuwar Kau...
16/01/2025

ME ZA'AYI DA BARAWO!!!

Daga Kasuwar Kauran Bauchi New GSM Village

Bayan alkawarin da jajircewa na shugabannin Kasuwar Kauran Bauchi New GSM Village tayi na tsayawa kai da fata wajan ganin Sun yaki duk wani Barawo wadda suke Satan wayoyin jama'a ko fasa shagunan ko gidaje Suna kawo kasuwar da sunan sayarwa

Cikin ikon Allah yau Allah Ya bawa shugabannin nasaran k**a wasu gaggan barayi Daga Bogoro LGA Sun fasa shaguna Sun debe wayoyin jama'a

Tuni Hukumar Kasuwar ta Mika wannan barayin zuwaga Hukumar 'yan Sanda ,Domin gudanar da bincike

Allah Ya shiga tsakanin nagari da mugu

Dahiru Sahaba
16/1/2025

Rundunar 'Yan Sandan jahar Kebbi ta k**a wasu mutane 3 da s**ayi yunkurin baiwa Jami'anta cin hancin naira Miliyan ɗaya ...
15/01/2025

Rundunar 'Yan Sandan jahar Kebbi ta k**a wasu mutane 3 da s**ayi yunkurin baiwa Jami'anta cin hancin naira Miliyan ɗaya da dubu sittin (₦1,060,000) a binciken harin 'yan ta'addan Lakurawa da rundunar ke yi.

Wadanda aka k**a sune; Umaru Garba mai shekaru 53.daga kauyen Dangandu na ƙaramar hukumar Arewa, Abubakar Alhaji Mamman mai shekaru 51 daga kauyen Maimaichi a ƙaramar hukumar Arewa da kuma Usman Muhammad mai shekaru 50 daga kauyen Bakaramba a ƙaramar hukumar Argungu.

Rundunar tace zata gabatarda su gaban kuliya da zaran an kammala bincike

DA ƊUMI-ƊUMINSA: Hukumar Alhazan Najeriya ta sanar da kamfanonin sufurin jiragen da za su gudanar da jigilar alhazai a H...
13/01/2025

DA ƊUMI-ƊUMINSA: Hukumar Alhazan Najeriya ta sanar da kamfanonin sufurin jiragen da za su gudanar da jigilar alhazai a Hajjin bana. Jiragen su ne k**ar haka:

1- UMZA Air (sabon kamfani)

2- Fly Nas

3- Max Air

4- Air Peace

Allah ka sa mu na daga cikin waɗanda za ka ƙira a bana.

Address

Kaduna
09023624451

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dokin kara 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dokin kara 24:

Videos

Share