GDK TV

GDK TV Wannan gidan talabijin din, mun bude ta ne domin fadakar da al'umma, wayarwa, da nishadantarwa.

Sabon Shugaban Syria ya kai ziyara kasar Saudiya a karon farko. A ranar 2 ga Fabrairu, 2025, sabon shugaban riƙon ƙwarya...
02/02/2025

Sabon Shugaban Syria ya kai ziyara kasar Saudiya a karon farko.

A ranar 2 ga Fabrairu, 2025, sabon shugaban riƙon ƙwarya na Syria, Ahmed al-Sharaa, ya kai ziyara ta farko a ƙasar Saudiyya tun bayan da ya karɓi mulki. An yi wannan ziyara ne domin ƙarfafa dangantaka tsakanin Syria da Saudiyya, tare da tattauna batutuwa masu muhimmanci ga yankin Gabas ta Tsakiya.

Tun bayan da Ahmed al-Sharaa ya jagoranci hamɓarar da gwamnatin Bashar al-Assad a Disamba 2024, ya yi kira ga ƙasashen duniya su cire takunkuman da aka sanya wa Syria, yana mai jaddada cewa hakan zai taimaka wajen dawo da 'yan gudun hijira zuwa ƙasarsu.

A cikin wannan ziyara, ana sa ran shugabannin biyu za su tattauna kan batutuwa da s**a haɗa da farfaɗo da tattalin arziƙin Syria, haɗin gwiwa a fannin tsaro, da kuma yadda za a magance tasirin sauyin yanayi a yankin. Bugu da ƙari, Ahmed al-Sharaa ya yi alƙawarin cewa ba za a yi amfani da ƙasar Syria a matsayin wurin kaddamar da hare-hare kan Isra'ila ba, yana mai nuni da cewa ba sa son rikici da Isra'ila.

Wannan ziyara ta nuna sabon shafin dangantaka tsakanin Syria da Saudiyya, tare da fatan kawo zaman lafiya da ci gaba a yankin Gabas ta Tsakiya.

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙara Kuɗin Wutar LantarkiGwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za a ƙara kuɗin wutar lantarki a Nije...
02/02/2025

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙara Kuɗin Wutar Lantarki

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za a ƙara kuɗin wutar lantarki a Nijeriya cikin ‘yan watanni masu zuwa.

Wannan mataki na daga cikin shirin gyaran harkar samar da lantarki a ƙasar.

HOTUNA: Yadda ’yan sanda s**a fara kamen takardun motoci a wasu sassan Najeriya.Daga yau ne doka ta ba jami'an damar bin...
02/02/2025

HOTUNA: Yadda ’yan sanda s**a fara kamen takardun motoci a wasu sassan Najeriya.

Daga yau ne doka ta ba jami'an damar bincike kan takardun ababen hawa don tabbatar da cewa takardun sun cika.

📷 Aminiya:

Dan majalisar tarayya mai walkita Fika da Fune Hon Engr Muhammed Buba Jajere ya jajanta wa al-umma garin Ngalda game da ...
01/02/2025

Dan majalisar tarayya mai walkita Fika da Fune Hon Engr Muhammed Buba Jajere ya jajanta wa al-umma garin Ngalda game da ibtila'in hare-haren da barayin yan ta'ada da s**a afaka wa yan kasuwa a garin Ngalda dake karamar hukumar Fika ta jihar Yobe ziyara wanda ya gudana a yammacin jiya juma'a

An daura auren Saleh Hussaini (Yayandu) da amaryar sa Hauwa Saleh Umar wanda ya gudana a garin Potsikum dake Jihar Yobe....
31/01/2025

An daura auren Saleh Hussaini (Yayandu) da amaryar sa Hauwa Saleh Umar wanda ya gudana a garin Potsikum dake Jihar Yobe.

Yadda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Ya Yi Salla tlTare Da Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass, Shekh Mahi Inyass A Masallac...
31/01/2025

Yadda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Ya Yi Salla tlTare Da Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass, Shekh Mahi Inyass A Masallacin Fadar Shugaban Kasa

Khalifan ya yi wa Najeriya addu'ar zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, Kana ya yi wa Shugaban kasar fatan samin nasarar aiyukan da ya ke yi na sake raya kasa.

Gwamnan Jigawa ya zama sanadiyar dawo da ruwan famfo bayan shafe shekaru 32 babu ruwan a kauyen Kantudu jihar Jigawa. Al...
31/01/2025

Gwamnan Jigawa ya zama sanadiyar dawo da ruwan famfo bayan shafe shekaru 32 babu ruwan a kauyen Kantudu jihar Jigawa.

Al’ummar kauyen Kantudu da ke a karamar hukumar Birninkudu a jihar Jigawa sun nuna farin ciki tare da jin dadi sak**akon mai do da ruwan famfo da aka yi a garin, bayan safe shekaru 32 da daukewar ruwan.

Bayan haka a yanzu haka Gwamnan ya nemo aikin jawowa kananan hukumomi masu yawa ruwan fanfo a kusan fadin jihar wanda aka shafe fiye da shekaru 20 Gwamnonin baya suna neman a zo a musu aikin, sai yanzu Gwamna Malam Umar Namadi ya yi Nasarar samo aikin wanda tuni an fara gudanarwa.

Ba lallai Nijeriya ta iya cike kujerun aikin hajjin da Saudiyya ta ware mata na hajjin 2025, saboda cikar wa'adin biyan ...
31/01/2025

Ba lallai Nijeriya ta iya cike kujerun aikin hajjin da Saudiyya ta ware mata na hajjin 2025, saboda cikar wa'adin biyan kudin kujera a ranar 31 ga watan Junairu - binciken Daily Trust

Muɲ Zare Takobíɲ Yaƙi Da Azzâlúmaí Masu Daƙile Cigaban Jihar Kano – Gwamna AbbaGwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusu...
31/01/2025

Muɲ Zare Takobíɲ Yaƙi Da Azzâlúmaí Masu Daƙile Cigaban Jihar Kano – Gwamna Abba

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf yace lokaci yayi da zai fara yãƙi da masu hana jihar zama lafiya a duk inda suke .

A yayin ƙaddamar da aikin wani t**i mai tsawon kilomita tara, Gwamna na Kano Abba Kabir Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida-Gida, ya zare tâkòbí wanda hakan ke nufi ya shirya tsaf domin yãƙar mutanan da ya kira azzâlųmâi maƙiya jihar da s**a hana mutane zama lafiya.

Gwamna ya karɓi kyautar kwafiɲ Al’qur’ani bugun hannu da kuma falleliyar takòbí daga hannu Dr. Ishaq Falalu Zarewa a madadin al’ummar yankin bisa kammala aikin t**in.

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Obot Akpabio Ya Karɓi Bakuncin Shugaban Hukumar Gudanarwar Kula Da Ayyukan Ƴ...
30/01/2025

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Obot Akpabio Ya Karɓi Bakuncin Shugaban Hukumar Gudanarwar Kula Da Ayyukan Ƴansandan Najeriya, Alhaji Hashimu Argungun

30/01/2025

Kudaden haraji da Nijeriya ta samu a shekara ta 2024 sun kai naira tiriliyan 21.6 - Shugaban hukumar tattara haraji FIRS

Kotun ta amince da bukatar tsohon Gwamnan Taraba, Darius Ishaku, na tafiya UAE domin duba lafiyarsa. Justice Sylvanus Or...
30/01/2025

Kotun ta amince da bukatar tsohon Gwamnan Taraba, Darius Ishaku, na tafiya UAE domin duba lafiyarsa.

Justice Sylvanus Oriji ya yarda da rokon ne bayan takardar roko da lauya na sa ya gabatar.

A halin yanzu, Ishaku yana fuskantar shari'a tare da Bello Yero, kan zargin sama da Fadi da naira 27 biliyan daga kudaden gwamnati.

YANZU-YANZU: Shugaban riƙon ƙwarya na Burkina Faso, Ibrahim Traoré, ya karɓi fasfo na farko na gamayyar kasashe uku na (...
30/01/2025

YANZU-YANZU: Shugaban riƙon ƙwarya na Burkina Faso, Ibrahim Traoré, ya karɓi fasfo na farko na gamayyar kasashe uku na (AES)

Shugaban riƙon ƙwarya na Burkina Faso, Kaftin Ibrahim Traoré, ya karɓi fasfo na farko na zahiri daga ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Sahel (AES) a birnin Ouagadougou.

Ƙungiyar AES, wacce ƙasashen Burkina Faso, Mali da Nijar s**a kafa, ta ƙaddamar da sabuwar takardar fasfo ta bai ɗaya, bayan ficewarsu daga ƙungiyar ECOWAS.

Ficewar su daga ECOWAS ta fara aiki ne a hukumance a ranar Laraba, 29 ga Janairu.

Hukumar kwastam a Nijeriya ta k**a fetur da ya kai lita 199,495 a jihar Adamawa
30/01/2025

Hukumar kwastam a Nijeriya ta k**a fetur da ya kai lita 199,495 a jihar Adamawa

YANZU-YANZU: Hukumar Kwastam Tayi Gwanjon Wani Gidan Mai Da Ta K**a A Jihar Adamawa Haka zalika hukumar ta sauke farashi...
30/01/2025

YANZU-YANZU: Hukumar Kwastam Tayi Gwanjon Wani Gidan Mai Da Ta K**a A Jihar Adamawa

Haka zalika hukumar ta sauke farashin mai zuwa 630, a kowacce lita, gidan mai din yana nan akan hanyar Shigowa jihar Adamawa dai-dai shatale-tale mai doki dake jihar.

Muhammad Kwairi Waziri

Kiristocin Arewacin Najeriya Sunfi Amfana da  ingantattatun abubuwa a  Karkashin Gwamnatin Tinubu – Shugaban CANRev. Yak...
30/01/2025

Kiristocin Arewacin Najeriya Sunfi Amfana da ingantattatun abubuwa a Karkashin Gwamnatin Tinubu – Shugaban CAN

Rev. Yakubu Pam, Shugaban Kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) Reshen Arewa, ya yaba wa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu kan inganta rayuwar Kiristoci a Arewacin Najeriya.

Ya jaddada raguwar zaluncin da a keyiwa Kiristoci, musamman wajen samun fili don gina coci da kuma tilastawa ’yan mata Kiristoci canza addini ko auren tilas.

Duk da acewarsa ya tabbatar da cewa har yanzu ana samun zaluncin da a keyiwa Kiristoci Amma Bai Kai K**ar a mulkin bayaba.

Pam ya qara da cewa zaluncin da a keyiwa Kiristoci ya ragu sosai a karkashin shugabancin Tinubu. Hakan na nuna cewa yana dauke da kowa.

yana neman a bawa Kiristoci wakilci a manyan muk**ai, k**ar na mataimakin shugaban kasa, inda ya ambata cewa Kiristocin Arewa suna sha'awar samun kujerar mataimakin shugaban kasa a zaben 2027.

Umar Dahiru (Procain) yana farin gayyata yan uwa da abokan arziki zuwa wajen daurin auren sa gobe Jumu'a , bayan sallah ...
30/01/2025

Umar Dahiru (Procain) yana farin gayyata yan uwa da abokan arziki zuwa wajen daurin auren sa gobe Jumu'a , bayan sallah da misalin karfe 2:30pm
A unguwan View center cikin garin Gadaka

Ku masa fatan alkhairi

ECOWAS ta ba shugabannin Mali da Burkina Faso da Nijar kudin tallafi sun ki su karba, amma kuma sun karbi tallafin motoc...
30/01/2025

ECOWAS ta ba shugabannin Mali da Burkina Faso da Nijar kudin tallafi sun ki su karba, amma kuma sun karbi tallafin motocin daukar marasa lafiya 'Ambulances' sun ce ba a sa son a sani, saboda haka za su shafe fentin motocin – Yusuf Tuggar Ministan harkokin wajen Najeriya

Address

Gadaka

Telephone

+2348082396404

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GDK TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share

Category