Sani Twoeffect Yawuri Online

Sani Twoeffect Yawuri Online Blogger
Media Influencer
Writer
Media Consultant
Publisher
Content Creator

Gwamnatin Jihar Kebbi ta amince da cire kuɗi sama da Naira miliyan ɗari tara (₦925m) domin biyan kuɗin haƙƙoƙin ma'aikat...
15/01/2025

Gwamnatin Jihar Kebbi ta amince da cire kuɗi sama da Naira miliyan ɗari tara (₦925m) domin biyan kuɗin haƙƙoƙin ma'aikatan da s**ayi ritaya da kuma waɗanda s**a rasu a bakin aiki mutum 367:

Daga Sani Twoeffect Yawuri

Maigirma Gwamna Kwamared Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu ya amince da cire kuɗi sama da Naira miliyan ɗari tara (₦925m) domin biyan kuɗin haƙƙoƙin ma'aikatan Jihar da s**ayi ritaya na gratuity da kuma Death benefits na mutane 367.

Sanarwar hakan ta fito ne a cikin wata takarda da ta fito daga ofishin shugaban ma'aikatan Jihar mai ɗauke da sanya hannun Abdulrashid Muhammad Bala.

An rabawa manema labarai kofin takardun ranar laraba 15/1/2025 a garin Birnin Kebbi babban Birnin Jihar.

Takardar ta bayyana cewar ma'aikatan da za'a biya hakkokin nasu sun hada da ma'aikatan Jiha, ma'aikatan ƙananan hukumomi, ma'aikatan hukumar ilimi na ƙananan hukumomi wato LGEA, da kuma ma'aikatan wuccin gadi wato Contract staff da s**a aje aiki ko s**a rasu tsakanin 16/7/2024 zuwa 15/11/2024.

Wannan amincewa da Maigirma Gwamna yayi na biyan waɗannan kuɗaɗen ya nuna irin yadda Maigirma Gwamna ya ɗauki walwala da jindadin ma'aikatan Jihar da muhimmanci.

Sign Yahya Sarki

Gwamnatin Jihar Kebbi ya baiwa matan tsofaffin sojojin Jihar da s**a rasa rayukansu kyautar kuɗi Naira miliyan talatin (...
15/01/2025

Gwamnatin Jihar Kebbi ya baiwa matan tsofaffin sojojin Jihar da s**a rasa rayukansu kyautar kuɗi Naira miliyan talatin (₦30m):

Daga Sani Twoeffect Yawuri

Maigirma Gwamnan Jihar Kebbi Kwamared Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ya bayyana bayar da wannan kuɗin ne ranar laraba 15/1/2025 a wurin faretin bikin tunawa da ƴan mazan jiya wato Armed Forces Remembrance Day na wannan shekarar ta 2025 da ya gudana a filin wasa na Haliru Abdu Stadium dake cikin garin Birnin Kebbi babban Birnin Jihar.

Gwamnan ya bayyana cewar bikin tunawa da ƴan mazan jiyan yana tunawa al'ummar Najeriya da irin gudunmawar da ƴan mazan jiyan s**a bayar wajen kare ƙasar su da kuma tabbatar da zaman lafiya da walwalar al'ummar ƙasar.

Haka kuma Gwamnan ya bayyana cewar wannan rashin na tsofaffin sojojin da s**a rasa rayukansu wajen kare ƙasar su ba kawai rashi ne na iyalansu ba, babban rashi ne da ya shafi al'ummar Najeriya baki ɗaya inda ya basu tabbacin Gwamnati tana tare dasu.

Haka kuma Gwamnan ya bayar da gudunmawar kuɗi Naira miliyan goma (₦10m) ga masu yiwa ƙasa hidima wato Corp Members da kuma marayun barikin sojojin garin Birnin Kebbi wato 1 Battalion, Dukku Barack.

Bayan haka kuma Gwamnan ya bayar da kyautar Naira miliyan goma sha biyar (₦15m) ga barikin sojojin garin Zuru wato 223 Light Tank, Zuru Barrack a turance.

Daga karshe Gwamnan yayi kira ga al'ummar jihar dasuyi aiki tare wajen nuna godiyar su ga ƴan mazan jiyan da s**a kwanta dama wajen tabbatar da zaman lafiyar kasar mu inda ya bayyana irin kyawawan haɗin kai dake tsakanin hukumomin tsaron Jihar da Gwamnatin Jihar wajen tabbatar da ingantaccen tsaro a fadin Jihar baki ɗaya.

Sign Ahmed Idris

Gwamnan Jihar Kebbi ya ɗaurawa wasu Jami'an tsaron sa shaidar ƙarin girma da s**a samu:Daga Sani Twoeffect YawuriMaigirm...
15/01/2025

Gwamnan Jihar Kebbi ya ɗaurawa wasu Jami'an tsaron sa shaidar ƙarin girma da s**a samu:

Daga Sani Twoeffect Yawuri

Maigirma Gwamnan Jihar Kebbi Kwamared Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ya jagoranci ɗaurawa wasu mutum biyu daga cikin manyan jami'an tsaron sa shaidar ƙarin girma da s**a samu.

Waɗannan Jami'an tsaron nasa da s**a samu ƙarin girman sun hada da: Babban Jami'in tsaron Maigirma Gwamnan wato Chief Security Officer (CSO) Ahmed Suleiman da kuma Es**rt Commander Ahmed Abdullahi Nora waɗanda dukkanin su s**a samu ƙarin girma a wajen aikin su zuwa muƙamin Deputy Superintendent of Police wato DSP.

Anyi bikin ɗaura musu igiyar ƙarin girman zuwa muƙamin DSPs ne a babban dakin taro na fadar Gwamnatin Jihar Kebbi wato Government House Chamber ƙarƙashin jagorancin maigirma Gwamna da taimakon Kwamishinan ƴan sandan Jihar CP Bello Sani.

Da yake jawabi a wurin taron, maigirma Gwamna ya taya su murnar samun wannan ƙarin girman a fagen aikin nasu inda yayi musu fatar alheri a cikin sauran shekarun su na aiki da s**a rage.

Shima da yake jawabi a madadin jami'an da s**a samu ƙarin girman, DSP Ahmed Suleiman yayi godiya ga maigirma Gwamna da kuma nuna jindaɗinsu bisa wannan ƙarin girman da s**a samu inda ya bayyana ba ƙaramin nasara bace a garesu ace Maigirma Gwamna ne da kansa ya ɗaura musu lambar girman da kansa.

Haka kuma ya bayyana cewar wannan ƙarin girman zai kara musu ƙaimi wajen cigaba da aiki tuƙuru wajen kare ƙasar su da gudanar da aiki bisa ka'ida da kuma himma.

Haka kuma ya bayyana cewar irin jagoranci da kyakkyawar hulda da Maigirma Gwamna yakeyi da jami'an tsaro musamman ƴan sandan Jihar ya ƙara masa kwarin guiwar cigaba da gudanar da ayyukan sa kamar yadda ya dace.

Sign Ahmed Idris

Sakon Taya Murna;Muna Taya Khalifa Jega murnar samun karuwa ta haihuwar diya mace da maraicen yau laraba 15/01/2025, jin...
15/01/2025

Sakon Taya Murna;

Muna Taya Khalifa Jega murnar samun karuwa ta haihuwar diya mace da maraicen yau laraba 15/01/2025, jinjirar tana cikin koshin lafiya, amma mahaifiyar tana bukatar Addu'ar ku.

Muna Addu'ar Allah ya raya mana akan tafarkin sunnah madaidaiciya. Amin.

Sakon Taya Murna;Muna Taya Hassan Gule murnar Samun Kyautar sabuwar mota Kirar Golf Daga hannun Kwamishinan Kananan Huku...
15/01/2025

Sakon Taya Murna;

Muna Taya Hassan Gule murnar Samun Kyautar sabuwar mota Kirar Golf Daga hannun Kwamishinan Kananan Hukumomi da Masarautun Jihar Kebbi Alhaji Abubakar Dutsinmari Kaigaman Yawuri na farko.

Muna Addu'ar Allah ya saka masa da Mafificin Alherinsa. Amin

Sani Twoeffect Yawuri
15/1/2025

15/01/2025

Najeriya Kenan 🤔🤔

Ku Saurara Kuji 👂.

15/01/2025

Ɗan Jarida Yayi Free.

15/01/2025

Shugaba Tinubu Maigidana ne, Ba zan taba s**arsa ba, ina s**ar wasu manufofin gwamnatinsa ne kawai, Gwomnatinmu cewar Senator Ali Ndume.

Ranar tunawa da ƴan mazan jiya (tsofaffin sojoji): Gwamnatin Jihar Kebbi ta baiwa tsofaffin sojojin Jihar gudunmuwar Nai...
15/01/2025

Ranar tunawa da ƴan mazan jiya (tsofaffin sojoji): Gwamnatin Jihar Kebbi ta baiwa tsofaffin sojojin Jihar gudunmuwar Naira miliyan hamsin (₦50m):

Daga Sani Twoeffect Yawuri

Maigirma Gwamna Kwamared Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ne ya bayyana bayar da gudummawar ta Naira miliyan hamsin (₦50m) ne ga tsofaffin sojojin Jihar a wurin kaddamar da gidauniyar neman taimako ga tsofaffin sojojin wato Emblem of appeal fund for the fallen heros a turance wanda ɗaya ne daga cikin shirye-shiryen bukukuwan tunawa da tsofaffin sojojin na wannan shekarar ta 2025.

An kaddamar da neman taimakon ne a fadar Gwamnatin Jihar Kebbi dake cikin garin Birnin Kebbi.

Bayan gudunmuwar Gwamnatin Jihar Kebbi, Maigirma Gwamna Kwamared Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu shima ya bayar da tashi gudunmawar ta Naira miliyan goma (₦10m) a madadin shi kansa da iyalansa da kuma gidauniyar sa ta ƙauran Gwandu foundation.

Da yake jawabi a wurin taron, maigirma Gwamna Kwamared Nasir Idris Ƙauran Gwandu yayi jinjina da godiya ta musamman ga tsofaffin sojojin bisa irin gudunmawar da s**a bayar da kuma sadaukarwar da s**ayi wajen kare ƙasar mu Najeriya da kuma tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan al'ummar kasar baki ɗaya.

Maigirma Gwamna yayi kira ga al'ummar Jihar masu hannu da shuni da suma su bayar da nasu gudunmawar ga iyalan tsofaffin sojojin da s**a rasa rayukansu wajen kare martabar ƙasar mu Najeriya da tabbatar da zaman lafiya.

Haka kuma Gwamnan ya umarci Kwamishinan filaye da gidaje na jihar Kebbi da ya samar da filaye ga kungiyar ta tsofaffin sojojin Jihar a garuruwan Argungu, Yawuri da kuma Zuru.

Haka kuma Gwamnan ya jaddada ƙudurin Gwamnatin sa na tabbatar da samar da tsaro da inganta shi a fadin Jihar tareda tabbatar da zaman lafiya a dukkanin faɗin ƙananan hukumomin jihar.

Shima shugaban ƙungiyar tsofaffin sojojin Jahar Sajant Garba Hassan Suru (RTD) da yake nasa jawabin tun a farko, ya yaba tareda godiya ta musamman ga maigirma Gwamna bisa irin taimakon da yake yiwa ƴaƴan kungiyar a fadin Jihar baki ɗaya.

Garba Hassan Suru (Rtd) ya bayyana cewar maigirma Gwamna ya taimakawa ƴaƴan kungiyar da dama a ɓangarori daban-daban inda shima yayi kira ga al'ummar jihar baki ɗaya masu hannu da shuni dasu taimaka wa iyalan tsofaffin sojojin da s**a rasa rayukansu a fagen daga.

A wurin kaddamar da neman tallafin an gudanar da ababe kamar haka; anyiwa maigirma Gwamna da mataimakin sa da kakakin majalisar dokokin jihar ado da alama wato Emblem na neman gudunmuwar

Sign Ahmed Idris

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Shafii Mansur, Z***r A Sale, Hussaini Jibir Na'alire, Umm...
15/01/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Shafii Mansur, Z***r A Sale, Hussaini Jibir Na'alire, Ummu Fadimah Hafsah Rabiu, Umar Yakubu, Sidi Zubairu Muhammad, Abubakar Ubaliyo, Idrissa Sawadogo, Abdoul Razak Amadou, Abu Amnah Kubarachi, Sani Suleman, Mohammed Ahmed Jameel Kumo, Hamisu Gambo, Istifanus Eliya, Yakubu Adamu, Hon Obiora Uchenna, Nura Saad, Mustapha Ahmed, Maekaji Ahmadu, Bashar Abubakar, Halima Usman, Shapilo Adamz, Zayyanu Sahabi, Kingsarleem Saeed Barwa, Henry Mbaya, Abdullahi Mai Rariya, Ibrahim Abdulaziz, A Usman Xaki, Oskona Masheki, Aliyu Al Amin, Nura Abdul Nura Abdul, Abdulkadir Adamu Shekarau Kakangi, Usini Uamr, Master Zaria, Nasir Abubakar, Yusuf Garba, Sadik Mohammed, Ibraheem On Top, Ali Haruna, Hussaini Haruna, Moussa Yaro, Hassan Mokawu, Patience Hosea, Muntari Hussaini, Habubakar Ibrahim, Mas Ud Mase, Dahiru Osori, يوسف ابكر حسن محمد

14/01/2025

A gaban ikhiwani da Alhazai an nannagawa Madara Kwallaye 5-2👇👇

President Bola Ahmed Tinubu attends the 2025 Abu Dhabi Sustainability Week Opening Ceremony and Sustainability Prize Awa...
14/01/2025

President Bola Ahmed Tinubu attends the 2025 Abu Dhabi Sustainability Week Opening Ceremony and Sustainability Prize Award Ceremony in the United Arab Emirates.

Hukumar Jindaɗin Alhazzai ta Jihar Kebbi ta sanya ranar 5/2/2025 a matsayin ranar da zata rufe rajistan maniyyan aikin H...
14/01/2025

Hukumar Jindaɗin Alhazzai ta Jihar Kebbi ta sanya ranar 5/2/2025 a matsayin ranar da zata rufe rajistan maniyyan aikin Hajjin bana:

Daga Sani Twoeffect Yawuri

Maigirma shugaban hukumar jindadin alhazzan jihar Kebbi Alhaji Farouq Musa Yaro Enabo (Jagaban Gwandu) ne ya bayyana hakan a wata sanarwar da ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewar sanya ranar rufe rajistan maniyyan aikin Hajjin banan tazo ne bayan da hukumar aikin Hajji ta ƙasa NAHCON ta fitar da wani sabon Jadawalin tsare-tsaren gudanar da shirye-shiryen jigilar alhazan bana tareda umartar dukkanin hukumomin jindadin alhazzai na jihohi dasu shigar da dukkanin kudaden maniyyan aikin Hajjin bana asusun ta nan zuwa 1/2/2025.

Haka kuma sanarwar ta bayyana cewar hukumar jindadin alhazzan ta riga ta sarrafa kaso 60 na kuɗin ta na aikin Hajjin wannan shekarar tun lokacin da aka ƙaddamar da fara biyan kudin aikin Hajjin a wata Satumba na shekarar da ta gabata 2024.

Jagaban Gwandu yayi kira ga maniyyatan dasu yi amfani da wannan damar wajen biyan kudaden su kafin sabuwar ranar da aka sanya na rufe rajistan maniyyatan.

Haka kuma ya bayyana dukkanin maniyyatan na aikin Hajjin bana zasu fara saka Naira miliyan takwas da dubu ɗari huɗu (₦8,400,000) a cikin asusun hukumar daga kowani banki a matsayin kudin buƙatar kujerar aikin hajji wanda hukumar Jindaɗin Alhazzai ta ƙasa ta fitar.

Shugaban hukumar alhazzan na jihar Kebbi ya bayyana cewar za'a samar da kujerun aikin hajjin ga waɗanda s**a fara biyan kudin su wato First to Come-First to Serve a turance bisa adalci.

Haka kuma sanarwar tayi kira ga wadanda s**a biya kuɗin aikin hajjin bara na shekarar 2024 kuma basu samu zuwa ba s**a bar kuɗaɗen su ga hukumar alhazzai dasu cika sauran kudin nasu domin samun kujerar aikin hajjin bana kafin ranar da aka sanya na rufe rajistan maniyyatan.

Haka kuma sanarwar ta bayyana cewar hukumar jindadin alhazzan ta ƙasa NAHCON a shirye take tsaf domin kara jaddada ƙoƙarin ta wajen jigilar alhazan bana ta hanyar sabbin tsare-tsaren da ta fito dasu

Gwamnan Jihar Kebbi ya gabatar da ta'aziyar sa ga al'ummar garin Gwandu bisa rasuwar Sarkin Malaman Garin Gwandu:Daga Sa...
14/01/2025

Gwamnan Jihar Kebbi ya gabatar da ta'aziyar sa ga al'ummar garin Gwandu bisa rasuwar Sarkin Malaman Garin Gwandu:

Daga Sani Twoeffect Yawuri

Maigirma Gwamnan Jihar Kebbi Kwamared Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ya miƙa ta'aziyar sa ga al'ummar garin Gwandu bisa rashin sarkin malaman garin Gwandu Malam Umaru Hassan wanda ya rasu ranar lahadi 12/1/2025 bayan yayi fama da wata doguwar jinya.

Sarkin Malaman na garin Gwandu Malam Umaru Hassan ya rasu ne yana da shekaru casa'in da tara (99yrs) a duniya kuma ya rasu yabar matarsa da ƴa'ƴa goma sha ɗaya (11) da kuma jikoki da dama daga ciki harda Malam Faruk Umar wanda yayi ritaya a matsayin ma'aikaci a asibitin kwararru na Gwamnatin tarayya dake Jihar Kebbi wato Federal Medical Center Birnin Kebbi (FMC).

A lokacin ta'aziyar maigirma Gwamna Kwamared Dakta Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) a yau Litinin 13/1/2025, maigirma Gwamna ya bayyana alhinin sa bisa rashin sarkin malaman na garin Gwandu.

Gwamnan yayi ta'aziyar ne ga babban ɗan marigayin Alhaji Sanusi Umar wanda Daraktan harkokin kuɗi ne a Ma'aikatar harkokin filayen jiragen sama na Najeriya wato Federal Airports Aviation Authority (FAAN) da kuma sauran iyalan marigayin.

Haka kuma Gwamnan yayi addu'ar Allah ya gafarta ma sarkin malaman garin Gwandu Malam Umaru Hassan kuma yasa Aljannar Firdausi ce makomarsa.

Shima Alhaji Sanusi Umar, da yake jawabi a madadin sauran iyalan marigayin, yayi godiya ta musamman ga maigirma Gwamna bisa wannan ta'aziyar da yayi musu ta rashin mahaifinsu inda yayi addu'ar Allah ya sakawa maigirma Gwamna da alheri kuma ya karɓi dukkanin addu'oin da aka gudanar domin neman gafara ga mahaifin nasu.

Sign Yahya Sarki

Gwamnatin Jihar Kebbi zata gina wani katafaren ɗakin wasanni mai ɗaukar mutum dubu shida (6,000) wato Indoor stadium a t...
14/01/2025

Gwamnatin Jihar Kebbi zata gina wani katafaren ɗakin wasanni mai ɗaukar mutum dubu shida (6,000) wato Indoor stadium a turance domin inganta harkokin wasanni da motsa jiki a jihar Kebbi:

Daga Sani Twoeffect Yawuri

A ƙoƙarinta na inganta harkokin motsa jiki, inganta harkokin lafiyar matasa da kuma wasannin, Gwamnatin Jihar Kebbi zata gina wani katafaren ɗakin wasanni da ake kira da turanci Indoor stadium a garin Birnin Kebbi.

Kwamishinan harkokin wasanni da matasa na jihar Kebbi Honorabul Nura Bala Fingilla ne ya bayyana hakan a wurin bikin buɗe gasar kofin Gimbiyar Basaura Hajiya Dakta Nafisa Nasir Idris Kauran Gwandu wato Dakta Nafisa Nasir Idris Gimbiyar Basaura Unity Challenge Cup Competition a turance wanda aka ƙaddamar ranar Lahadi 12/1/2025 a garin Birnin Kebbi.

Da yake jawabi a wurin taron, Honorabul Fingilla ya bayyana ƙudurin maigirma Gwamna na inganta harkokin wasanni da matasa a matsayin daya daga cikin ƙudurorin Gwamnatin Maigirma Gwamna Kwamared Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu wanda inganta harkokin wasanni zai inganta tareda samar da haɗin kai, cigaban tattalin arziki da bunƙasa lafiyar matasa dama al'ummar Jihar Kebbi baki daya.

Honorabul Fingilla ya ƙara da cewar Maigirma Gwamna ya shigar da ababe da dama da s**a shafi inganta harkokin motsa jiki da wasanni a cikin kundin kasafin kudin bana na shekarar 2025 wanda wannan aikin gina Indoor stadium din Yana daya daga ciki.

Honorabul Fingilla ya bayyana cewar shirin irin wadannan wasannin ya samar da haɗin kai tsakanin matasa tareda inganta tattalin arzikin su dana jiha baki ɗaya inda yanzu harkar wasar Ƙwallon Ƙafa ya wuce wasar motsa jiki kawai, wata hanyar sana'a ce dake inganta rayuwar matasa a duniya.

Haka kuma ya jinjinawa Gwamnatin Jihar Kebbi bisa irin nasarorin da aka samu a ɓangarorin wasannin motsa jiki inda yanzu haka Jihar Kebbi tana da ƴan wasa a matakin ƙasa da kuma duniya irinsu Zaidu Sanusi Jega inda yace jihar tana cigaba da kokari na musamman wajen samar da matasa kwararru a harkokin wasanni a matakin ƙasa da duniya baki daya.

Haka kuma Kwamishinan wasannin ya yabawa waɗanda s**a shirya wannan gasar cin kofin na matar Gwamna kuma Gimbiyar Basaura Hajiya Dakta Nafisa Nasir Idris Alhaji Khairullah Abdullahi (Sarkin Yamman Jega) da haɗin guiwar ofishin matar Gwamna Hajiya Dakta Nafisa Nasir Idris wanda hakan yayi daidai da manufofin Gwamnatin Jihar Kebbi ƙarƙashin jagorancin maigirma Gwamna Kwamared Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu wajen samar da haɗin kai tsakanin matasa da kuma tallafa musu wajen samun sana'o'in dogaro dakai.

Ita dai wannan gasar cin kofin na matar Gwamna zai samu halartar ƴan wasa daga dukkanin kananan hukumomin jihar 21 da zasu fafata a gasar.

Alhaji Khairullah Abdullahi Jega shugaban gidauniyar Alkhairiyya Foundation ne ya shirya tare da ɗaukar nauyin gudanar da gasar a madadin matar maigirma Gwamna domin karrama ta.

Babban manufar shirya gasar shine samar da haɗin kai tsakanin matasan jihar, zakulo matasa masu hazaka a harkokin wasanni da inganta tattalin arzikin matasan da jihar baki ɗaya.

Alhaji Khairullah Jega wanda shine ya ɗauki nauyin shirya gasar ya samu halartar kaddamar da wasar inda ya kalli wasa tsakanin kungiyar sa ta Sarkin Yamman Jega Football Club da kuma Dutsinmari Football Club.

Da yake cigaba da jawabi a wurin kaddamar da gasar, sarkin yamman jega ya jaddada ƙudurin sa wajen cigaba da tallafawa harkokin wasanni da matasa kamar yadda gwamnatin maigirma Gwamna Kwamared Dakta Nasir Idris take da manufa.

Sarkin Yamman Jega Football Club ne yayi nasara a wasar buɗe fagen da ci uku (3) ba ko ɗaya (0) akan Dutsinmari Football Club

Sign Yahya Sarki

President Tinubu’s Drive Towards a Sustainable Industrialization for NigeriaBy Dada Olusegun President Bola Tinubu as pa...
13/01/2025

President Tinubu’s Drive Towards a Sustainable Industrialization for Nigeria

By Dada Olusegun

President Bola Tinubu as part of his national industrial plan in his Renewed Hope manifesto promised to prioritise growing Nigeria's industrial base to provide jobs to Nigeria's expanding population. Just over 19 months in office, the President has been walking the talk thanks to the various strategic efforts currently being put in place by the administration towards increasing Nigeria's industrial capacity at both the micro and macro levels.

The Tinubu administration has so far begun the implementation of certain initiatives that are geared towards expanding the production capacity of existing manufacturing firms and also providing a friendly environment and stimulus for new ones to set up shop in Nigeria. I will outline some of these steps and policy moves below:

1. Bank Recapitalization: The CBN in March last year began a recapitalization programme in the banking sector where Nigerian banks are required to increase their minimum paid-in capital to a particular threshold depending on the type of banking licenses they hold. For commercial banks with international licenses, the minimum capital requirement is N500 billion.

This exercise, which is expected to be concluded in 2026 is geared towards creating a more robust financial framework that will contribute massively to the growth and development of the real sector by providing liquidity and credit needed for the desired development, especially in the industrial sector, which is a major driver of economic growth and job creation. The aim is that after recapitalization, many of the banks will increase the ability to take bigger risks and provide credit to new and existing manufacturers, including those operating at a small or medium scale level.

2. Nigeria Credit Guarantee Company: Closely aligned with the bank recapitalization efforts of the Tinubu administration is the anticipated creation of the Nigeria Credit Guarantee Bank announced by the President in his New Year message. The company which is expected to begin operations before the end of the second quarter of 2025 aims to derisk the financial market and provide the needed buffer for lenders to perform the intended duty from the recapitalization process without any fear of loan default or loss of capital.

The Nigeria Credit Guarantee Company is designed to be in partnership with government institutions that play a role in the industrialisation drive, such as the Bank of Industry, the Nigerian Consumer Credit Corporation (CREDICORP), the Nigerian Sovereign Investment Agency (NSIA) and the Ministry of Finance Incorporated (MOFI) as well as the private sector and multilateral institutions. This initiative will remove one of the biggest barriers that makes banks reluctant to extend credit to the manufacturing sector.

3. Multi-billion Naira Low Interest Credit for Manufacturers: President Bola Tinubu as part of efforts to provide immediate support to large enterprises including manufacturers to sustain and expand their operations announced a N75 billion Manufacturing Intervention Fund. The aim is to offer large manufacturing enterprises up to N1 billion credit at a 9% interest rate instead of the going rate in the lending market which is around 30%. The repayment period is spread over 10 years. According to the Bank of Industry, around 140 manufacturers have applied for the low-interest credit facility.

One of the significant aspects of the Intervention Fund is its revolving nature where repayments from previous beneficiaries are used to provide loans to new businesses, ensuring a continuous flow of funds and most importantly availability of cheaper financing to manufacturing companies. This is a huge incentive for industrialisation in Nigeria.

13/01/2025

Wannan Yaro Lamin Yamal
Baya ganin darajar manya.

inji Wani Dan Madara🤣

13/01/2025

Jama'a Wani Ɗan Barcelona Yadawo Gida Ya Ɗau Buhu Zai Koma Gidan Kallo.

Address

Birnin-Kebbi

Telephone

+2348094147776

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sani Twoeffect Yawuri Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share