Jaridar Zahiri

Jaridar Zahiri This is the official page for Aminu Harsanu Guyaba, and the page is meant to educate, entertain and

Kana tsammanin Najeriya zata gyaru?Najeriya bazata taɓa gyaruwa ba muddin Malamai zasu cigaba da zama kwaɗayayyu sannan ...
03/04/2022

Kana tsammanin Najeriya zata gyaru?

Najeriya bazata taɓa gyaruwa ba muddin Malamai zasu cigaba da zama kwaɗayayyu sannan kuma yaran ƴan siyasa domin kuwa babu yadda za'ayi mutum ya baka abun duniya sannan kuma kace zaka fito ka faɗi gaskiya.

Muna da tarin Malamai a ƙasar nan amma da dama daga cikin su ba zasu iya fitowa suyi magana akan abubuwan da suke faruwa a ƙasar nan ba saboda abun duniya ya rufe musu ido.

Ba daidai bane don wanda yake Shugabantar ƙasar nan Musulmi ɗan arewa ne ace idan yayi kuskure ba za'a faɗa ba domin kuwa hakan ba adalci bane.

A lokacin da Goodluck Jonathan yake Shugabantar ƙasar nan abubuwa basu taɓarɓare k**ar yanzu ba amma kuma yasha s**a da Allah wadai daga wajen ƴan arewa yanzu kuma da ɗan arewa ne akan kujerar sun kasa ce komai.

Imam Nuru Khalid ya fito ya faɗi gaskiya ya kuma bada shawarin cewa zaɓe bata da amfani matuƙar waɗanda ake zaɓa bazasu kare rayuka da dukiyoyin al'umma ba.

Yanzu don Allah kai hakan yana maka daɗi yadda ake rayuwa a Najeriya? Kodai saboda lamarin bai shafeka kai tsaye bane? Ko kuma don lamarin bai shafi wani naka ba?

Wallahi idan har muna neman mafita tou dole ne muyi amfani da shawarin Imam Khalid.

Allah yasa mudace.
[email protected]

Idan har akwai kishin ƙasa a ranka da kuma son cigaban al'umma tou iya abinda yake faruwa a jam'iyar APC ya isheka hujja...
16/03/2022

Idan har akwai kishin ƙasa a ranka da kuma son cigaban al'umma tou iya abinda yake faruwa a jam'iyar APC ya isheka hujja kar ka goyi bayan ASIWAJU BOLA AHMAD TINUBU.

Shugaba Buhari mutum ne da ya tsufa hakan yasa yake ta jeka kadawo akan batun shugabancin riƙon jam'iyar su ta APC.

Ya kai ɗan uwa! Yaya kake tunani lamarin zai kasance idan kuma Baba TINUBU ya zama shugaban Najeriya la'akari da irin baiwan shekaru da Ubangiji ya masa? Shin kana tunanin zaiyi abinda ya k**ata?

Ya k**ata mu gane cewa riƙe Najeriya tafi ƙarfin tsoho.

Allah yasa mudace.

16/03/2022

Ya kai ɗan uwa! Ka sauƙe girman Kai ka koyi sana'a domin kuwa a shekarun ka yanzu ba lokacin hutu bane a gare ka, bai k**ata ka zauna kullum kana jiran wani ya ɗauka ya baka ba.

Kana matashi mai jini a jika amma baka da sana'a? Amma kuma kana riƙe da wayar salula da ta kai dubu hamsin? Kuma kana iya takura kanka domin ka ɗinka shadda mai walƙiya don ka burge mutane ko? Gaskiya ɗan uwa ka gyara tunanin ka domin baka san yadda gobe zata kasance ba.

Wallahi idan kabari har girma ya k**a ka ba ka iya wata sana'ar hannu ba lashakka zakayi kuka da idon ka domin kuwa waɗanda kake burgewa yanzu kana musu ƙaryan kana da shi watarana baza ka gansu ba ma.

Ina amfanin kaje gurin mace kana mata ƙaryan abinda baka da shi? Ita kuma dake shashasha ce ta ganka da shadda sai tayi tunanin cewa kana hutawa batasan irin kashin daka haɗa ba kafin kayi wannan ɗinki.

Ya ke ƴar Uwa! Kiyi tunani sannan kiyi nazarin gobe, ba mutuncin ki bane ki tsaya da wanda bashi da sana'a a matsayin saurayi ko shi ɗan gidan waye kuwa domin abun mahaifinsa ay ba nashi bane.

Ya k**ata ƴan uwa mu sauƙe girman kai mu nemi abin dogaro da Kai tun kafin lokaci ya ƙure mana.

Allah yasa mudace.
Aminu Harsanu Guyaba

ALKALERI/KIRFI MUNYI ASARAR WAKILIA matsayina na talakan mazaɓar Alkaleri/Kirfi inada hakki akan wakili na domin kuwa wa...
12/03/2022

ALKALERI/KIRFI MUNYI ASARAR WAKILI

A matsayina na talakan mazaɓar Alkaleri/Kirfi inada hakki akan wakili na domin kuwa wakiltar mu yake yi a majalisar wakilai ta tarayya.

Tun bayan shigar sa majalisa bansan wani abinda yayi na alkhairi wa al'ummar mazaɓar shi ba ballantana ace ya tashi tsaye a majalisar ya kai wani ƙuduri.

Muna ganin irin abinda sauran takwarorin sa sukeyi a mazaɓun su amma mukuma bamu shaida komai ba, ko shin abinda ake basu shi baya samu ne? Ko kuma baya samun daman da suke samu ne? Meye yasa idan abun alhini ya faru baya zuwa gida ko kuma ya kai ƙuduri domin akawo mana agajin gaggawa.

Don Allah wanda yake da kishin al'umma da tausayin talaka a ransa zaije ya gina Hotel a jihar Kano ko a wani waje? Bamu ce kar kayi kasuwanci ba amma dai ya zamana akwai kishi da kuma tausayin al'umma.

Sannan munga hanyar kwalta a Unguwar G.R.A a Bauchi kuma wannan aiki anyi ne saboda Hotel ɗin sa dake wannan Unguwa, ya manta da cewa talakawan da s**a zaɓe shi suna buƙatar wannan hanyar a inda suke fiye da waɗanda suke zuwa Hotel ɗin.

Allah sarki rayuwa! Wallahi shugabannin mu suna manta cewa watarana zamu tashi dasu a gaban Ubangiji kuma Allah zai karɓa mana hakkin mu.

Kai kuma talaka ɗan uwa na kana nan baka da sana'a sai yabon mutumin da kai kan ka kasan bai cancanta ya zama shugaba ba saboda kawai ana baka ɗan wani abu da bai taka kara ya karya ba.

A maimakon ya tallafa maka kayi karatu ko ya baka jari amma sai ka zaɓi kayita rubutun ƙarya dana gaskiya kana yaɗawa saboda abaka na DATA.

Wallahi matasa ya k**ata muyi wa kan mu karatun ta nutsu muyi abinda zai amfane mu da ƴan uwan mu anan gaba.

Yanzu kam lokaci yayi da ya k**ata talaka ya farka ya san inda yake masa ciwo ya kuma zaɓi shugaba nagari wanda zai wakilce shi da kyau bawai yaje yana gina Hotel ɗin da bata da amfani ga al'ummar mazaɓar sa ba.
Allah yasa mudace

Chief Aminu Guyaba
[email protected]

Indiya ta ce ta harba makami mai linzami cikin kuskure zuwa Pakistan ranar Laraba, inda ta ɗora alhakin abin kan "matsal...
11/03/2022

Indiya ta ce ta harba makami mai linzami cikin kuskure zuwa Pakistan ranar Laraba, inda ta ɗora alhakin abin kan "matsalar na'ura" yayin aikin duba mak**an.

Indiya ta ce ta yi nadama sannan ta nuna jin daɗinta da "ba a kashe kowa ba".

Rundunar sojan Pakistan ta ce "wani abu mai ɗan karen gudu" ya faɗo a kusa da birnin Mian Channu kuma hanyar da ya bi ta tsorata jiragen fasinja.

Dukkan ƙasashen na da makamin nukilya.

Pakistan ta gargaɗi maƙociyar tata da ta kiyaye sake afkuwar hakan.

An harba makamin ne daga tashar Sirsa da ke jihar Haryana, a cewar wata sanarwa daga ma'aikatar tsaro ta Indiya.
BBC HAUSA

Barka da Juma'a daga BitCloud Solutions. Muna nan muna dakon ku a kamfanin mu dake kan hanyar Fadaman Mada kusa da makar...
11/03/2022

Barka da Juma'a daga BitCloud Solutions. Muna nan muna dakon ku a kamfanin mu dake kan hanyar Fadaman Mada kusa da makarantar Fariah.

11/03/2022

The Inspector-General of Police Usman Baba, has ordered the immediate evacuation of all impounded and unregistered exhibit vehicles as well as those involved in accidents from police stations nationwide.

The IGP also urged all concerned members of the public to approach various police stations/formations for the recovery of their vehicles with valid proof of ownership and proper means of identification.

The directive was contained in a statement on Tuesday by the acting Force Public Relations Officer, Muyiwa Adejobi.

Mr Adejobi said that the order followed the unprofessional manner the vehicles were stacked within police facilities, causing nuisance and disgusting sight.

He said the IGP had expressed dissatisfaction over the practice of stockpiling vehicles recovered from crime scenes or those whose ownership was being contested.

The spokesperson said the situation had been made worse by stringent requirements and cumbersome processes for the rightful owners of the vehicles to reclaim them.

Address

Bauchi

Telephone

+2347031575598

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Zahiri posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Zahiri:

Share

Nearby media companies


Other Media/News Companies in Bauchi

Show All

You may also like