ABN Hausa

ABN Hausa Please follow my page

Makiyayi ya gartsa wa kada cizo don kubutar da kansaWani makiyayi dan kasar Australia ya tsallake rijiya da baya, bayan ...
08/11/2023

Makiyayi ya gartsa wa kada cizo don kubutar da kansa
Wani makiyayi dan kasar Australia ya tsallake rijiya da baya, bayan ya yi artabu da wani kada da ya far masa, inda shi ma ya gatsa wa kadan cizo.
Mai kiwon shanun Colin Deveraux ya shafe tsawon wata daya yana jinya a asibiti, bayan zabgegen kadan mai tsawon kafa goma ya raunata shi a yankin Northern Territory.
Ya fada wa tashar labarai ta ABC News cewa ya gartsa wa kadan cizo ne a kan fatar idonsa lokacin da yake fafutukar tsira da rai.
Mista Colin Deveraux ya ce ya shiga garari ne bayan ya tsaya a wani tafki lokacin da yake tafiya a kusa da Kogin Finniss cikin watan jiya.
Ya ce ya dan tsaya a gefe, bayan ya lura da kifayen da ke ninkaya a ruwa. Amma lokacin da ya dan ja da baya, sai ya ji kawai kada ya cafkar masa kafar dama, inda ya jijjiga shi k**ar tsumma sannan ya fizge shi cikin ruwa.
Makiyayin ya fada wa tashar ABC cewa da farko ya sa daya kafarsa ya shuri kadan - kafin ya sa baki ya gartsa masa cizo.
"Ina cikin wani yanayi na rudewa… sai kwatsam na ji hakorana sun k**a fatar idonsa. Tana da matukar kauri, k**ar wata jakar fata, amma kawai sai na ja da karfi, ai kuwa sai ya sake ni.
"Na yi tsalle na fito, na nufi wurin da motata take. Amma ya sake biyo ni k**ar tafiyar mita hudu, kafin kuma sai ya tsaya."
Mista Colin Deveraux ya ce ya yi amfani da tawul da igiya wajen daure kafarsa da ke zubar da jini, sannan dan'uwansa ya tuko shi a mota, tafiyar kilomita 130 zuwa Asibitin Royal Darwin.

© BBC Hausa

Tsohon shugaban ƙasar wanda ya bayyana hakan a cikin saƙonsa na Babbar Sallah, ya kuma nemi 'yan Najeriya su goya wa Shu...
27/06/2023

Tsohon shugaban ƙasar wanda ya bayyana hakan a cikin saƙonsa na Babbar Sallah, ya kuma nemi 'yan Najeriya su goya wa Shugaba Tinubu baya don ganin ya yi nasara a mulkinsa.

Kalli yadda aka kai mahajjatan da ke kwance a gadon asibiti Makkah daga Madina domin su cigaba da aikin Hajjinsu.📸: Hara...
24/06/2023

Kalli yadda aka kai mahajjatan da ke kwance a gadon asibiti Makkah daga Madina domin su cigaba da aikin Hajjinsu.

📸: Haramain Sharifain

Hotunan rufe tafsiri a masallacin fadar shugaban Najeriya, wanda shi ne na karshe da Buhari zai halarta a matsayinsa na ...
08/04/2023

Hotunan rufe tafsiri a masallacin fadar shugaban Najeriya, wanda shi ne na karshe da Buhari zai halarta a matsayinsa na shugaban kasa.

An rufe tafsirin da wuri ne kasancewar mai gabatar da tafsirin, Sheikh Abdulwahab Sulaiman zai tafi aikin umara a kasar Saudiyya.

📸 - Fadar Shugaban Najeriya

Gwamnatin Kaduna ta mayar da malaman da ta kora bakin aikiGwamnatin Kaduna ta amince a mayar da malaman makarantar firam...
05/04/2023

Gwamnatin Kaduna ta mayar da malaman da ta kora bakin aiki

Gwamnatin Kaduna ta amince a mayar da malaman makarantar firamare fiye da duɓu ɗaya da ta sallama a Yunin 2022 bayan yi musu wata jarrabawar tabbatar da ƙwarewarsu.

Kakakin ma'aikatar ilimi ta jihar Hajiya Hauwa Muhammad ce ta bayyana hakan cikin sanarwar da aka fitar yau Laraba.

Hajiya Hauwa ta ce malamai 1,266 ne aka yi wa jarrabawar gwajin cancantar yayin da 22 a cikinsu aka tsame su daga jadawalin albashin gwamnati.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito cewa a Yunin 2022 ne ma'aikatar ilimin ta kori malaman Firamare 2,357 saboda gaza tsallake jarrabawar.

Ita ma jaridar Punch ta ruwaito ma'aikatar ta yi bayanin cewa an sallami malamai 2,192 saboda ƙin rubuta jarabawar yayin da malamai 165 kuma aka kore su saboda rashin tabuka abin a zo a gani.

Wasu daga cikin malaman da matakin ya shafa sun yi ƙorafin cewa sun rubuta jarrabawar kuma sun ci kuma duk da haka aka kore su yayin da wasu kuma s**a yi iƙirarin cewa ba su da lafiya a lokacin da aka yi jarabawar kuma sun gabatar da takardar shaida.

Su kuwa wasu malaman cewa s**a yi an yi garkuwa da su ne a lokacin, yayin da wasu s**a ce a lokacin an dakatar da su ne saboda aikin tantance takardunsu.

© BBC Hausa

Yau zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Tinubu ke cika shekara 71 da haihuwa a duniya.Wane saƙo kuke da shi zuwa gare shi?
29/03/2023

Yau zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Tinubu ke cika shekara 71 da haihuwa a duniya.

Wane saƙo kuke da shi zuwa gare shi?

Buhari ya ƙaddamar da rijiyar man fetur a jihar NasarawaShugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ƙammadar da aikin haƙar ri...
28/03/2023

Buhari ya ƙaddamar da rijiyar man fetur a jihar Nasarawa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ƙammadar da aikin haƙar rijiyar man fetu a ƙaramar hukumar Obi a jihar Nasarawa da ke arewa ta tsakiyar ƙasar.

Ƙaddamar da aikin tona rijiyar zai sa kamfanin mai na ƙasar NNPC Ltd, ta fara tono man fetur daga jihar.

A cikin watan Nuwamban bara ne dai shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙo man fetur a yankin Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Yawancin man da ƙasar ke da shi dai tana haƙoshi ne daga yankin Niger Delta a kudu maso kudancin ƙasar.

Najeriya dai ta dogara ne kan man fetur da take fitarwa a matsayin hanayr samun kuɗin shiga, duk kuwa da ƙoƙarin da gwamnatocin ƙasar ke yi na faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga ga ƙasar.

© BBC Hausa

Uwargidan zaɓaɓɓen Sanatan Katsina ta tsakiya, Hajiya Binta Abdul-aziz Musa Yar'adua, na yima Al-ummar Katsina ta tsakiy...
26/03/2023

Uwargidan zaɓaɓɓen Sanatan Katsina ta tsakiya, Hajiya Binta Abdul-aziz Musa Yar'adua, na yima Al-ummar Katsina ta tsakiya da na Jihar tare da ƙasa baki daya murnar Shigowar Watan Azumin Ramadan.

Ta kuma yi kira ga Al-umma da Su ribaci falalar watan Ramadan tare yin adduoi Allah ya karo mana zaman lafiya ga Al-umma baki daya.

© Katsina Post

Hotunan sallar juma’a ta farko a cikin watan Ramadan da aka yi a masallacin Ka’aba da ke Makkah. 📸 - Haramain Sharifain
24/03/2023

Hotunan sallar juma’a ta farko a cikin watan Ramadan da aka yi a masallacin Ka’aba da ke Makkah.

📸 - Haramain Sharifain

Sarkin Kano Aminu Ado ya taya Abba Kabir murnar zama gwamnaSarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya taya zaɓaɓɓen gwamnan ...
23/03/2023

Sarkin Kano Aminu Ado ya taya Abba Kabir murnar zama gwamna

Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya taya zaɓaɓɓen gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan da aka gudanar a ranar Asabar 18 ga watan Maris.

Cikin wata wasiƙa da ya aike da ita, Sarkin Kano ya ce ya fahimci mutane sun karɓi dimokradiyya hannu biyu-biyu, kuma abu mafi mahimmani shi ne yadda s**a fito s**a kaɗa kuri'unsu k**ar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Gabanin haka shi ma Sarkin Gaya Alhaji Aliyu Ibrahim Gaya ya aike da ta shi wasiƙar taya murna ga sabon zaɓaɓɓen gwamnan, wanda ya ce a madadinsa da iyalansa ya aika sakon.

Sarkin Rano ma Alhaji Kabiru Muhammad Inuwa ya aike da na shi saƙon tare da fatan Allah ya taya sabon shugaban riƙo da shugabancin mutanen Kano.

Duka sarakunan sun miƙa godiya ga malaman addinai da shugabannin jama'a da s**a riƙa wayar da kan al'umma, aka yi zaɓe lafiya aka gama lafiya.

© BBC Hausa

Mai alfarma, Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar na uku ya bukaci 'yan Najeriya su yi wa shugabannin da aka zaɓa a zaɓen da y...
23/03/2023

Mai alfarma, Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar na uku ya bukaci 'yan Najeriya su yi wa shugabannin da aka zaɓa a zaɓen da ya gabata addu'ar samun nasara.

© BBC Hausa

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar na uku ya sanar da ganin jaririn watan Ramadan na shekarar 2023 a wasu...
22/03/2023

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar na uku ya sanar da ganin jaririn watan Ramadan na shekarar 2023 a wasu sassan Najeriya.

© BBC Hausa

Alhamdulillah Anga Wata Yanzu Yanzu
22/03/2023

Alhamdulillah Anga Wata Yanzu Yanzu

An fara duba jinjirin watan Ramadana a Saudiyya. 📸 - Haramain Sharifain
21/03/2023

An fara duba jinjirin watan Ramadana a Saudiyya.

📸 - Haramain Sharifain

Sa’o’i kadan bayan da aka sanar da sak**akon zaben gwamnan jihar Kano, ‘yan daba sun afka cikin gidan mawakin siyasar, i...
20/03/2023

Sa’o’i kadan bayan da aka sanar da sak**akon zaben gwamnan jihar Kano, ‘yan daba sun afka cikin gidan mawakin siyasar, inda s**a rika lalata kayayyaki, da motoci kafin cinna wa wani bangaren gidan wuta.
© BBC Hausa

Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya yi murnar lashe zaben gwamnan Kano.📸 - Ibrahim Adam
20/03/2023

Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya yi murnar lashe zaben gwamnan Kano.

📸 - Ibrahim Adam

Yadda Dikko Radda Yaci Zabe A Katsina
19/03/2023

Yadda Dikko Radda Yaci Zabe A Katsina

Address

Anglo Jos

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ABN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ABN Hausa:

Videos

Share