ABN Hausa

ABN Hausa Please follow my page

Makiyayi ya gartsa wa kada cizo don kubutar da kansaWani makiyayi dan kasar Australia ya tsallake rijiya da baya, bayan ...
08/11/2023

Makiyayi ya gartsa wa kada cizo don kubutar da kansa
Wani makiyayi dan kasar Australia ya tsallake rijiya da baya, bayan ya yi artabu da wani kada da ya far masa, inda shi ma ya gatsa wa kadan cizo.
Mai kiwon shanun Colin Deveraux ya shafe tsawon wata daya yana jinya a asibiti, bayan zabgegen kadan mai tsawon kafa goma ya raunata shi a yankin Northern Territory.
Ya fada wa tashar labarai ta ABC News cewa ya gartsa wa kadan cizo ne a kan fatar idonsa lokacin da yake fafutukar tsira da rai.
Mista Colin Deveraux ya ce ya shiga garari ne bayan ya tsaya a wani tafki lokacin da yake tafiya a kusa da Kogin Finniss cikin watan jiya.
Ya ce ya dan tsaya a gefe, bayan ya lura da kifayen da ke ninkaya a ruwa. Amma lokacin da ya dan ja da baya, sai ya ji kawai kada ya cafkar masa kafar dama, inda ya jijjiga shi k**ar tsumma sannan ya fizge shi cikin ruwa.
Makiyayin ya fada wa tashar ABC cewa da farko ya sa daya kafarsa ya shuri kadan - kafin ya sa baki ya gartsa masa cizo.
"Ina cikin wani yanayi na rudewa… sai kwatsam na ji hakorana sun k**a fatar idonsa. Tana da matukar kauri, k**ar wata jakar fata, amma kawai sai na ja da karfi, ai kuwa sai ya sake ni.
"Na yi tsalle na fito, na nufi wurin da motata take. Amma ya sake biyo ni k**ar tafiyar mita hudu, kafin kuma sai ya tsaya."
Mista Colin Deveraux ya ce ya yi amfani da tawul da igiya wajen daure kafarsa da ke zubar da jini, sannan dan'uwansa ya tuko shi a mota, tafiyar kilomita 130 zuwa Asibitin Royal Darwin.

© BBC Hausa

Tsohon shugaban ƙasar wanda ya bayyana hakan a cikin saƙonsa na Babbar Sallah, ya kuma nemi 'yan Najeriya su goya wa Shu...
27/06/2023

Tsohon shugaban ƙasar wanda ya bayyana hakan a cikin saƙonsa na Babbar Sallah, ya kuma nemi 'yan Najeriya su goya wa Shugaba Tinubu baya don ganin ya yi nasara a mulkinsa.

Kalli yadda aka kai mahajjatan da ke kwance a gadon asibiti Makkah daga Madina domin su cigaba da aikin Hajjinsu.📸: Hara...
24/06/2023

Kalli yadda aka kai mahajjatan da ke kwance a gadon asibiti Makkah daga Madina domin su cigaba da aikin Hajjinsu.

📸: Haramain Sharifain

Hotunan rufe tafsiri a masallacin fadar shugaban Najeriya, wanda shi ne na karshe da Buhari zai halarta a matsayinsa na ...
08/04/2023

Hotunan rufe tafsiri a masallacin fadar shugaban Najeriya, wanda shi ne na karshe da Buhari zai halarta a matsayinsa na shugaban kasa.

An rufe tafsirin da wuri ne kasancewar mai gabatar da tafsirin, Sheikh Abdulwahab Sulaiman zai tafi aikin umara a kasar Saudiyya.

📸 - Fadar Shugaban Najeriya

Gwamnatin Kaduna ta mayar da malaman da ta kora bakin aikiGwamnatin Kaduna ta amince a mayar da malaman makarantar firam...
05/04/2023

Gwamnatin Kaduna ta mayar da malaman da ta kora bakin aiki

Gwamnatin Kaduna ta amince a mayar da malaman makarantar firamare fiye da duɓu ɗaya da ta sallama a Yunin 2022 bayan yi musu wata jarrabawar tabbatar da ƙwarewarsu.

Kakakin ma'aikatar ilimi ta jihar Hajiya Hauwa Muhammad ce ta bayyana hakan cikin sanarwar da aka fitar yau Laraba.

Hajiya Hauwa ta ce malamai 1,266 ne aka yi wa jarrabawar gwajin cancantar yayin da 22 a cikinsu aka tsame su daga jadawalin albashin gwamnati.

Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito cewa a Yunin 2022 ne ma'aikatar ilimin ta kori malaman Firamare 2,357 saboda gaza tsallake jarrabawar.

Ita ma jaridar Punch ta ruwaito ma'aikatar ta yi bayanin cewa an sallami malamai 2,192 saboda ƙin rubuta jarabawar yayin da malamai 165 kuma aka kore su saboda rashin tabuka abin a zo a gani.

Wasu daga cikin malaman da matakin ya shafa sun yi ƙorafin cewa sun rubuta jarrabawar kuma sun ci kuma duk da haka aka kore su yayin da wasu kuma s**a yi iƙirarin cewa ba su da lafiya a lokacin da aka yi jarabawar kuma sun gabatar da takardar shaida.

Su kuwa wasu malaman cewa s**a yi an yi garkuwa da su ne a lokacin, yayin da wasu s**a ce a lokacin an dakatar da su ne saboda aikin tantance takardunsu.

© BBC Hausa

Yau zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Tinubu ke cika shekara 71 da haihuwa a duniya.Wane saƙo kuke da shi zuwa gare shi?
29/03/2023

Yau zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Tinubu ke cika shekara 71 da haihuwa a duniya.

Wane saƙo kuke da shi zuwa gare shi?

Buhari ya ƙaddamar da rijiyar man fetur a jihar NasarawaShugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ƙammadar da aikin haƙar ri...
28/03/2023

Buhari ya ƙaddamar da rijiyar man fetur a jihar Nasarawa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ƙammadar da aikin haƙar rijiyar man fetu a ƙaramar hukumar Obi a jihar Nasarawa da ke arewa ta tsakiyar ƙasar.

Ƙaddamar da aikin tona rijiyar zai sa kamfanin mai na ƙasar NNPC Ltd, ta fara tono man fetur daga jihar.

A cikin watan Nuwamban bara ne dai shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙo man fetur a yankin Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Yawancin man da ƙasar ke da shi dai tana haƙoshi ne daga yankin Niger Delta a kudu maso kudancin ƙasar.

Najeriya dai ta dogara ne kan man fetur da take fitarwa a matsayin hanayr samun kuɗin shiga, duk kuwa da ƙoƙarin da gwamnatocin ƙasar ke yi na faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga ga ƙasar.

© BBC Hausa

Uwargidan zaɓaɓɓen Sanatan Katsina ta tsakiya, Hajiya Binta Abdul-aziz Musa Yar'adua, na yima Al-ummar Katsina ta tsakiy...
26/03/2023

Uwargidan zaɓaɓɓen Sanatan Katsina ta tsakiya, Hajiya Binta Abdul-aziz Musa Yar'adua, na yima Al-ummar Katsina ta tsakiya da na Jihar tare da ƙasa baki daya murnar Shigowar Watan Azumin Ramadan.

Ta kuma yi kira ga Al-umma da Su ribaci falalar watan Ramadan tare yin adduoi Allah ya karo mana zaman lafiya ga Al-umma baki daya.

© Katsina Post

Hotunan sallar juma’a ta farko a cikin watan Ramadan da aka yi a masallacin Ka’aba da ke Makkah. 📸 - Haramain Sharifain
24/03/2023

Hotunan sallar juma’a ta farko a cikin watan Ramadan da aka yi a masallacin Ka’aba da ke Makkah.

📸 - Haramain Sharifain

Sarkin Kano Aminu Ado ya taya Abba Kabir murnar zama gwamnaSarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya taya zaɓaɓɓen gwamnan ...
23/03/2023

Sarkin Kano Aminu Ado ya taya Abba Kabir murnar zama gwamna

Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya taya zaɓaɓɓen gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan da aka gudanar a ranar Asabar 18 ga watan Maris.

Cikin wata wasiƙa da ya aike da ita, Sarkin Kano ya ce ya fahimci mutane sun karɓi dimokradiyya hannu biyu-biyu, kuma abu mafi mahimmani shi ne yadda s**a fito s**a kaɗa kuri'unsu k**ar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Gabanin haka shi ma Sarkin Gaya Alhaji Aliyu Ibrahim Gaya ya aike da ta shi wasiƙar taya murna ga sabon zaɓaɓɓen gwamnan, wanda ya ce a madadinsa da iyalansa ya aika sakon.

Sarkin Rano ma Alhaji Kabiru Muhammad Inuwa ya aike da na shi saƙon tare da fatan Allah ya taya sabon shugaban riƙo da shugabancin mutanen Kano.

Duka sarakunan sun miƙa godiya ga malaman addinai da shugabannin jama'a da s**a riƙa wayar da kan al'umma, aka yi zaɓe lafiya aka gama lafiya.

© BBC Hausa

Mai alfarma, Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar na uku ya bukaci 'yan Najeriya su yi wa shugabannin da aka zaɓa a zaɓen da y...
23/03/2023

Mai alfarma, Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar na uku ya bukaci 'yan Najeriya su yi wa shugabannin da aka zaɓa a zaɓen da ya gabata addu'ar samun nasara.

© BBC Hausa

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar na uku ya sanar da ganin jaririn watan Ramadan na shekarar 2023 a wasu...
22/03/2023

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar na uku ya sanar da ganin jaririn watan Ramadan na shekarar 2023 a wasu sassan Najeriya.

© BBC Hausa

Alhamdulillah Anga Wata Yanzu Yanzu
22/03/2023

Alhamdulillah Anga Wata Yanzu Yanzu

An fara duba jinjirin watan Ramadana a Saudiyya. 📸 - Haramain Sharifain
21/03/2023

An fara duba jinjirin watan Ramadana a Saudiyya.

📸 - Haramain Sharifain

Sa’o’i kadan bayan da aka sanar da sak**akon zaben gwamnan jihar Kano, ‘yan daba sun afka cikin gidan mawakin siyasar, i...
20/03/2023

Sa’o’i kadan bayan da aka sanar da sak**akon zaben gwamnan jihar Kano, ‘yan daba sun afka cikin gidan mawakin siyasar, inda s**a rika lalata kayayyaki, da motoci kafin cinna wa wani bangaren gidan wuta.
© BBC Hausa

Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya yi murnar lashe zaben gwamnan Kano.📸 - Ibrahim Adam
20/03/2023

Yadda Abba Kabir Yusuf na NNPP ya yi murnar lashe zaben gwamnan Kano.

📸 - Ibrahim Adam

Yadda Dikko Radda Yaci Zabe A Katsina
19/03/2023

Yadda Dikko Radda Yaci Zabe A Katsina

Congratulations Dikko Umar Radda Ne Ya Lashe Zaben Jihar Katsina Allah Yataya Shi Riko
19/03/2023

Congratulations Dikko Umar Radda Ne Ya Lashe Zaben Jihar Katsina Allah Yataya Shi Riko

Hukumar zabe a jihar Jigawa ta sanar da Umar Namadi na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar.© BB...
19/03/2023

Hukumar zabe a jihar Jigawa ta sanar da Umar Namadi na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar.

© BBC Hausa

Dikko Radda ya bai wa Lado Dan Marke tazara mai yawa a Katsina
19/03/2023

Dikko Radda ya bai wa Lado Dan Marke tazara mai yawa a Katsina

Ana shirin fara bayyana sak**akon zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi a Katsina da Adamawa da Bauchi da kuma Nasaraw...
19/03/2023

Ana shirin fara bayyana sak**akon zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi a Katsina da Adamawa da Bauchi da kuma Nasarawa.

Garba Lado Ɗanmarke na ci gaba da shan kashi hannu Dikko Radda a jihar Katsina.
18/03/2023

Garba Lado Ɗanmarke na ci gaba da shan kashi hannu Dikko Radda a jihar Katsina.

18/03/2023

Taliya uku tasa dan fulani ya shiga uku sau uku a wajen zabe

Yayin da ake ci gaba da kada kuri'a don zaben gwamnoni da 'yan majalisun jihohi, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya s...
18/03/2023

Yayin da ake ci gaba da kada kuri'a don zaben gwamnoni da 'yan majalisun jihohi, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya shawarci 'yan ƙasar da su bi ra'ayinsu wajen zaɓar shugabanni na gari.

‘Yar takarar Gwamnan jihar Adamawa a APC, Aishatu Binani da dan takarar Gwamnan Katsina a APC, Dikko Radda, da kuma dan ...
18/03/2023

‘Yar takarar Gwamnan jihar Adamawa a APC, Aishatu Binani da dan takarar Gwamnan Katsina a APC, Dikko Radda, da kuma dan takarar gwamnan Bauchi a NNPP, Halliru Jika, su ma duk sun kada kuri’unsu a mazabunsu don zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi.

Zababben Sanatan shiyar katsina ta tsakiya Sanata Abdul’aziz Musa Yar’ada da matarshi Hajiya Binta Abdul’aziz Yar’adua s...
18/03/2023

Zababben Sanatan shiyar katsina ta tsakiya Sanata Abdul’aziz Musa Yar’ada da matarshi Hajiya Binta Abdul’aziz Yar’adua sun kada kuri’arsu a mazabarsu dake Kangiwa Ward, a unguwar Saulawa Katsina.

Yadda Hajiya Fatima Dikko Umar Radda Matar Dantakarar Kujerar Gwamnan Jihar Katsina Karkashin Tutar Jam'iyyar APC ta kad...
18/03/2023

Yadda Hajiya Fatima Dikko Umar Radda Matar Dantakarar Kujerar Gwamnan Jihar Katsina Karkashin Tutar Jam'iyyar APC ta kada kuri'ar ta

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya kada kuri’arsa a mazabarsa da ke Daura a Katsina, domin zaben gwamna da ‘yan maj...
18/03/2023

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya kada kuri’arsa a mazabarsa da ke Daura a Katsina, domin zaben gwamna da ‘yan majalisun jihohi.

📸 - Fadar Shugaban Najeriya

An samu rahotonnin sayen ƙuri'a a KanoRahotonni daga jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya na cewa an ga wasu da...
18/03/2023

An samu rahotonnin sayen ƙuri'a a Kano

Rahotonni daga jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya na cewa an ga wasu da ake zargin wakilan wasu jam'iyyun siyasa ne na raba atamfa da yaduka har ma da kuɗi.

Hotuna da BBC ta samu sun nuna yadda mutane suke karɓar irin waɗannan atamfofi, yayin da wasu kuma s**a ƙi karɓa.

Jihar Kano dai na ɗaya daga cikin jihohin da ake ganin zaɓen gwamna zai yi zafi sosai tsakanin 'yan takara.

A ranar Talata Sheikh Abdul Rehman Sudais ya cika shekara 40 da zama limamin masallacin Ka'aba. Shafin Haramain Sharifai...
15/03/2023

A ranar Talata Sheikh Abdul Rehman Sudais ya cika shekara 40 da zama limamin masallacin Ka'aba.

Shafin Haramain Sharifain ya ruwaito cewa Sudais ya fara jagoranci da sallar La'asar a Harami yana ɗan shekara 22 a 1984.

Wace surah kuka fi jin daɗi a karatun Sudais?

'Mun daƙile yunƙurin kutse ta intanet har sau miliyan 13 lokacin zaɓe'Hukumomi a Najeriya sun ce ƙasar ta daƙile yunƙuri...
15/03/2023

'Mun daƙile yunƙurin kutse ta intanet har sau miliyan 13 lokacin zaɓe'

Hukumomi a Najeriya sun ce ƙasar ta daƙile yunƙurin kutse ko hare-hare a kan hanyoyin sadarwa na intanet har kimanin miliyan 13 a lokacin zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar.

Babban daraktan hukumar bunƙasa fasahar sadarwa ta Najeriya, wato NITDA, Kashifu Inuwa AbdulLahi, shi ya bayyana haka a lokacin da yake tattaunawa da BBC, inda ya ce an samu nasarar ce sak**akon wasu cibiyoyi da aka kafa don yaƙi da kutsen ta intanet da kuma wani kwamiti na musamman da aka kafa da ya ƙunshi hukumomin NITDA da NCC da Galaxy Backbone.

Ya ce a ranar zaɓe kaɗai sun daƙile yunƙurin kutse har miliyan shida da dubu ɗari tara.

Daraktan na NITDA ya ce an yi ƙoƙarin yin kutsen daga cikin gida da kuma ƙasashen waje saboda suna amfani da wasu manhajoji.

Ya ce kutsen ya shafi shafukan intanet na hukumomi da na kamfanoni masu zaman kansu da kuma na hukumar zaɓe wanda shi ne aka fi kai wa hari saboda zaɓe.

Ya ce babban hatsari da ke tattare da yin kutsen, shi ne hakan zai sa a deɓi bayanai da canza wasu da kuma sanya wa mutane shakku kan amincewa da sahihan bayanai.

Saudiyya za ta ɗauki mata sama da 80 a matsayin direbobi a filayen jirgin samaGwamnatin Saudiyya ta ce za ta ɗauki hayar...
14/03/2023

Saudiyya za ta ɗauki mata sama da 80 a matsayin direbobi a filayen jirgin sama

Gwamnatin Saudiyya ta ce za ta ɗauki hayar mata sama da 80 a matsayin direbobi a manyan filayen jirgin sama na ƙasar guda huɗu.

Filayen jirgin sun haɗa da na Khalid da ke Riyadh da na Sarki Abdulaziz a Jeddah da na Sarki Fahd da ke birnin Dammam da kuma na Yarima Muhammad da ke Madinah.

Gwamnatin ƙasar ta ce hakan na cikin wani tsari da hukumar kula da sufuri ta ƙasar ta kaddamar a ranar Lahadi tare da haɗin gwiwar ma'aikatar albarkatun ƙasa da ci gaba, wanda aka yi domin sama wa mata aiki a bangaren sufuri, k**ar yadda jaridar Al-Watan ta ruwait.

Ta ce tsarin ya haɗa da kirkiro da wani shiri da zai horar da matuka motocin da kuma bayar da taimakon agaji da sauransu. Hukumar ta ce tsarin zai kuma taimaka wajen ci gaban ɓangaren sufuri da yanda ake kula da fasinjoji don tabbatar da ɗorewar fannin.

Bayan da CBN ya ce a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun Naira, shin kun fara kashe kudin?
14/03/2023

Bayan da CBN ya ce a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun Naira, shin kun fara kashe kudin?

Tinubu ya jajanta wa ƴan kasuwar Singer ta Kano kan gobaraSabon zaɓabben shugaban Najeriya mai jiran-gado Asiwaju Bola A...
14/03/2023

Tinubu ya jajanta wa ƴan kasuwar Singer ta Kano kan gobara

Sabon zaɓabben shugaban Najeriya mai jiran-gado Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya aika da saƙon jaje ga ƴan kasuwar da s**a yi asarar dukiyarsa da gobara ta ci a jihar kano
A wata sanarwa da ofishin yaɗa labaransa ya fitar a yau Talata, wadda ke ɗauke da sa hannun Abdulaziz Abdulaziz, Tinubu ya nuna takaicinsa kan bala'in gobarar da ya afka wa wani sashe na kasuwar Singer da kuma wasu kasuwannin biyu (Kurmi da Rimi) a jihar, duka a 'yan kwanakin nan.
Ya ce ya kaɗu da jin irin ɓarnar da bala'in ya haddasa ga al'ummar Kano da ma gwamnatin jihar.
Sannan ya yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su yi ƙoƙarin gano musabbabin tashin gobarar da ake ta samu a sassan Najeriya, tare da agaza wa waɗanda s**a yi asara.

Ban umarci CBN ya ƙi bin umarnin kotu kan takardun ƙudi ba – BuhariKarin bayani: https://bbc.in/3JdBkQm
14/03/2023

Ban umarci CBN ya ƙi bin umarnin kotu kan takardun ƙudi ba – Buhari

Karin bayani: https://bbc.in/3JdBkQm

Shugaba Muhammadu Buhari ya koma Abuja ranar Litinin bayan shafe kwanaki a mahaifarsa Daura, inda kuma ya kaɗa ƙuri'arsa...
13/03/2023

Shugaba Muhammadu Buhari ya koma Abuja ranar Litinin bayan shafe kwanaki a mahaifarsa Daura, inda kuma ya kaɗa ƙuri'arsa a zaɓen shugaban ƙasa ranar 25 ga watan Fabarairu.

📸: Fadar Shugaban Najeriya

Wata mummunar gobara ta ƙona kayayyaki na miliyoyin Naira a kasuwar Singa da ke birnin Kano bayan ta tashi a daren da ya...
13/03/2023

Wata mummunar gobara ta ƙona kayayyaki na miliyoyin Naira a kasuwar Singa da ke birnin Kano bayan ta tashi a daren da ya gabata.

© BBC Hausa

inna-li-llahi-wa-inna-ilaihi-rajiuun Duniyar Musulunci tayi babban rashin Mutumin daya zana rubutun sunan Allah da sunan...
12/03/2023

inna-li-llahi-wa-inna-ilaihi-rajiuun
Duniyar Musulunci tayi babban rashin
Mutumin daya zana rubutun sunan Allah da sunan Annabi Muhammadu a jikin Tutar Saudiyya Sheikh Al-Mansouf ya rasu,shine wanda ya sabunta tsarin rubutun dake jikin Tutar kasar Saudiyya.

Tinubu zai gana da zaɓaɓɓun 'yan majalisa kan shugabancin majalisun tarayyaJam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta gayyaci...
12/03/2023

Tinubu zai gana da zaɓaɓɓun 'yan majalisa kan shugabancin majalisun tarayya

Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta gayyaci zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu, tare da mataimakinsa Kashim Shettima, da sauran zaɓaɓɓun sanatoci na 'yan majalisar wakilai na jam'iyyar zuwa wata ganawa ta musamman.

An tsara gudanar da ganawar ranar Litinin a fadar gwamnati da ke Abuja babban birnin ƙasar.

Rahotonni na cewa an tsara ganawar ne domin tattauna batun shugabancin majalisun dokokin ƙasar biyu da yadda za a rarraba muƙaman majalisun zuwa shiyyoyin ƙasar daban-daban.

Gayyatar ganawa da zaɓaɓɓun wakilan - wadda sakataren jam'iyyar na ƙasa, Iyiola Omisore ya sanya wa hannu aka kuma wallafa a shafin jam'iyyar na Twitter - ta bayyan cewa za a yi ganawar ne ranar Litinin 13 ga watan Maris da misalin ƙarfe 12:00 na rana.

Jam'iyyar ta kuma buƙaci duka zaɓaɓɓun wakilan su hallara tare da takardun shaidar cin zaɓe da hukumar zaɓen ƙasar ta ba su.

Ganawar na zuwa ne bayan da tuni wasu 'yan majalisun s**a fara bayyana sha'awarsu ta zama shugabannin majalisun dokokin ƙasar biyu.

Samun haɗin kan shugabancin majalisun biyu dai na da matuƙar tasiri wajen gudanar da ayyuka a ɓangaren shugaban ƙasa.

© BBC Hausa

Address

Anglo Jos

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ABN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ABN Hausa:

Videos

Share

Nearby media companies


Other Media/News Companies in Anglo Jos

Show All

You may also like