AWAINIYA.com

AWAINIYA.com Barka Da Zuwa Gidan AWAINIYA.

mai Chanza Kala Har Kullum muna mar hba dazuwanku wAnnan shafi ku dannamana like Da Shere Domin Kasancewa Tare Acikin Wannan Sharmfin

MALAMAN DA AKE YAYI Zabi gwaninki/gwaninka muje zuwa yan uwa Sai Munjiku
09/12/2024

MALAMAN DA AKE YAYI Zabi gwaninki/gwaninka muje zuwa yan uwa Sai Munjiku

Ba Zan Iya Barin Ɗiyata Mace Ta Shiga Harkar Fim Ba, Amma Zan Iya Barin Ɗana Namiji, Cewar Jarumin Finafinan Hausa, Yusu...
09/12/2024

Ba Zan Iya Barin Ɗiyata Mace Ta Shiga Harkar Fim Ba, Amma Zan Iya Barin Ɗana Namiji, Cewar Jarumin Finafinan Hausa, Yusuf Muhammad (Lukuman)

Me zaku ce?

ALLAH YA TAYA RIKO SIR Yayin da ake sakawa Alkali Abubakar salihu Zari'a Rank ya samu karin matsayi a majalissar Agaji t...
08/12/2024

ALLAH YA TAYA RIKO SIR

Yayin da ake sakawa Alkali Abubakar salihu Zari'a Rank ya samu karin matsayi a majalissar Agaji ta kasa ya Zama National legal adviser fag of Jibwis Nhq Jos Nigerian.

Muna maka addu'ah Allah ya tayaka reko Allah yasa albarka.

MAZAJE Wani boka dake bada maganin bindiga a Abuja kenan kwance, bayan ya dirkawa cikin sa bindiga kuma ta k**a shi. An ...
05/12/2024

MAZAJE Wani boka dake bada maganin bindiga a Abuja kenan kwance, bayan ya dirkawa cikin sa bindiga kuma ta k**a shi. An bayyana sunansa a matsayin Ismail Usman dake kauyen Kuchibiyi a Bwari dake yankin Abuja.

📷 AWAINIYA.com

05/12/2024

Aure Ba Naka Bane Idan Baka Samun Dubu Dari Tara a Wata. Inji Wata Goyon Palo Me Zakuce👈

Yaya hudu da akasace Kun kubuta 🤔
05/12/2024

Yaya hudu da akasace Kun kubuta 🤔

Innalillahi Wainna Ilaihi Raji'un: 😭 Kulli Nafsin Za'ikatul Mut  Allah Yayiwa Babban Producer a Masana'antar Kannywood E...
05/12/2024

Innalillahi Wainna Ilaihi Raji'un: 😭 Kulli Nafsin Za'ikatul Mut Allah Yayiwa Babban Producer a Masana'antar Kannywood El'muazz Rasuwa A Daren Jiya 😭🥹
Muna Rokon Allah Yajikan Sa da Rahama

Ashe Tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, CBN, Wato Emifiele Ne Ya Mallaki Rukunin Gidaje Sama Da 700, Wanda Ya Kai Un...
04/12/2024

Ashe Tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, CBN, Wato Emifiele Ne Ya Mallaki Rukunin Gidaje Sama Da 700, Wanda Ya Kai Unguwa Guda Da Hukumar EFCC Ta Kwato A Yankin Lokogoma Dake Abuja

Me za ku ce?

Tatsuniya ta 38: Labarin Makauniya Da DantaGatanan gatanan ku A wani ƙauye da ke yamma da Dajin Kurege, akwai wani manom...
04/12/2024

Tatsuniya ta 38: Labarin Makauniya Da Danta

Gatanan gatanan ku

A wani ƙauye da ke yamma da Dajin Kurege, akwai wani manomi da matarsa makauniya. Suna zaune cikin ƙanƙanta, sai Allah ya ba su ɗa mai suna Zama. Uwarsa ta sha wahala wajen renonsa. Kullum sai ta je yin bara kafin ta ciyar da kanta da ɗanta. Mijinta bai bar musu dukiya ba sai shanu biyu kawai da Zama ya gada. Ita kuma mace mai tsinkaye da rikon amana, ta kai shanun nan wani garke a rugar wasu makiyaya da ke kusa da ƙauyensu. Ta yi haka ne da nufin idan yaron ya girma, kuma shanun sun yadu, za ta nuna masa abin da ubansa ya bar masa. Duk abin da danta yake so takan je ta samo masa.

Sannu a hankali, yaro ya girma ya isa aure. Wata rana bayan sun ci abincin dare, sai uwar ta kira shi ta ce: "To, Zama, da ma ina jira ne idan ka yi hankali sosai in danka maka abin da ka gada daga mahaifinka. Amma na kai su garke ne, a rugar wasu makiyaya."

Da ya ji lafazin mahaifiyarsa, sai ya tambaye ta: "Mene ne? Wane irin abu ne?"

Ta ce: "Shanu biyu ne ya bar maka, amma ban sani ba ko yanzu sun karu?" Sai ta k**a hannunsa ta ce: "Mu je inda aka kai shanun, mu jiyo labari." Ta yi masa kwatancen hanyar da za su bi; s**a k**a hanya har s**a kai.

Mai garke ya yi musu maraba s**a gaisa k**ar yadda ya k**ata, sai makauniya ta tuna masa shanun da ta kawo masa kiwo tun shekarun baya. Sai mai garke ya ce: "Haka aka yi kuwa. Ai yanzu shanu sun hayayyafa, har ma sun kai ashirin."

Da ta ji haka sai ta yi masa godiya, ta ce da shi: "To, ga magajinsu ya kawo karfi, bukatu sun taso, shi ya sa muka zo mu kora su."

Sai mai garke ya ware musu shanunsu; s**a k**a hanyar gida, Zama yana kora su har s**a je gida.

Bayan sun dan huta da kwana biyu, sai uwar ta ce da Zama: "Ya k**ata yanzu kam ka yi aure domin ina so in sami jikan da zan rinka wasa da shi."

Sai ya ce da ita: "To, amma fa ni ba zan yi aure a ƙauyen nan ba sai dai daga birni."

A kwana a tashi, wata rana sai Zama ya shiga birni, ya je kasuwa, sai ya tarar an sa wata kyakkyawar yarinya a gaba, makada na cashewa ana yi mata kirari, da wake-wake. Sai ya tambayi wani dan kallo da ke wurin: "Me ya sa aka kewaye wannan yarinya mai kyau k**ar aljana, ana yi mata kida da waka?"

Sai ya ce da shi: "Saboda kyaunta ne uwarta ta ce duk mai son ta, sai ya ba ta duk dukiyar da ya mallaka kafin ya aure ta. Duk masu dukiyar da ke garin nan kuma sun kasa."

Da ya ji haka sai ya yi tsaki, ya ce: "Ni zan aure ta." Sai ya matsa kusa, ya sa aka yi sanarwa, ya ce: "A gaya wa uwar yarinyar cewa ni zan aure ta, kuma zan ba da duk dukiyar da na mallaka."

Wani daga cikin danginta ya ce: “To me ka mallaka?"

Zama ya ce: "Ina da rikakkun shanu ashirin."

Sai dangin ya ce: "To, ka je ka kawo su za a ba ka ita."

Da Zama ya ji haka, sai kurum a cikin doki ya koma gida ya gaya wa mahaifiyarsa cewa ya sami wadda zai aura.

Uwar ta ce: "Wane sharadi iyayenta s**a sa maka?"

Sai ya ce: "Sun ce sai na ba su duk dukiyata kafin su ba ni ita."

Uwar daga farko ta yi murna, amma da ta yi tunani kadan sai ta ce: "Kai ɗan nan, wannan fa shi ne iyakar abin da ka mallaka, babu hikima a ce ka ba su ita gaba ɗaya."

Wannan magana dai ba ta shigi yaron ba. Sai kawai ya ce shi fa sai ya auri wannan yarinyar. Sai uwar ta ce: "Shi ke nan, yi abin da kake so."

Ya kora shanu, ya kai su gidan iyayen yarinyar da zai aura. S**a karba s**a kuma ba shi yarinyar, aka ɗaura aure ya dauki matarsa ya kai ta gidansu, ya je kuma ya sanar da mahaifiyarsa. Ita kuma ta ce da shi: "Ai ya k**ata ka kai ni in yi mata barka da zuwa."

Bai yi wata-wata ba ko sai ya k**a sandarta ya kai ta har dakin amaryar. Amma da ta ga mahaifiyar Zama makauniya ce, sai ta ki yi mata magana, ta nuna cewa ai ba ta yi wa makafi magana. Uwar kuma ba ta nuna damuwa a kan halayyar surukarta ba, saboda hakurin da Allah ya ba ta.

Ana nan, bayan 'yan kwanaki sai amarya ta ce da Zama: "Ni fa na gaji, ba zan iya ci gaba da girki a gidan nan ba."

Sai ya ce: "To, yaya k**e so a yi?"

Ta ce da shi: "Mai dafa abinci za ka nemo mini."

Da ya ga matarsa ta kafe a kan haka sai ya gaya wa mahaifiyarsa. Ita kuma ta ce da shi: "Ba komai, ni zan ci gaba da dafawa; ai dama tun kafin ta zo, ni nake dafawa". Haka ta ci gaba da yi musu girki, surukarta kuwa ta ci gaba da zaman ƙwambo.

Wata rana matar Zama ta tambayi mijin inda ya samo shanun da ya kai gidansu ya aure ta. Sai ya kwashe labarin yadda ya ci gadon mahaifinsa, ya gaya mata. Da ta ji haka sai ta ce: "Ai mahaifiyarka ta cuce ka domin ta boye sauran shanun. Ka je ka bincike ta da kyau, za ta gaya maka inda sauran suke."

Nan da nan ya tashi ya je ya sami mahaifiyarsa, ya fara yi mata rashin ladabi da fada, wai sai ta fito masa da sauran shanunsa. Ita kuma ta ce da shi: "Haba ɗana, ban boye maka komai ba."

Haka dai Zama ya yi ta yi wa mahaifiyarsa rashin ladabi har tsawon wasu 'yan kwanaki.

Da matar Zama ta ga bai yi wa mahaifiyarsa wulakanci k**ar yadda take so ba, sai ta ce da shi: "Ni fa zan koma gidanmu; domin na gaji da zama da makauniya a gidan nan.

04/12/2024

Da naira 1,550 dinka zaka yi waya na tsawon awa 5hrs, ma'ana zaka samu naira 7,500 daga MTN da samun damar tura sakon Bulk messages guda 100 da samun kyautar data har 500MB, Har na tsawon wata daya, ba wannan kadai ba, da sauran garabasa, irinsu da 3,100 zakayi waya na tsawon awa 10hrs Da 5,200 zakayi waya na tsawon awa 16.6hrs da 10,500 zaka kwana kana waya, domin zakayi awa 33.3hrs.
Duk wannan yana yiwuwa ne a karkashin tsarin da kamfanin data na Salfat s**a kawo na *SalFat Thryve Talk* ga link: https://salfat.com.ng

A tuntube su: 09011361110
08137350232

Da Dumi Dumi Dan Takarar APC A Zaben Gwabnan Jihar Kano Yafita Hutu Kasashen Waje Me Zaku 👈
03/12/2024

Da Dumi Dumi Dan Takarar APC A Zaben Gwabnan Jihar Kano Yafita Hutu Kasashen Waje Me Zaku 👈

Tsohon Ministan Tsaron Nigeria.Janar T. Y. Danjuma Mai Ritaya Yace Shugaban Kasar Nigeria Bola Ahmad Tunibu Yana Gudanar...
03/12/2024

Tsohon Ministan Tsaron Nigeria.

Janar T. Y. Danjuma Mai Ritaya Yace Shugaban Kasar Nigeria Bola Ahmad Tunibu Yana Gudanar Da Mulkin Kasar Ne Batare Da yana Tuntubar Iyayen Kowacce Shiyya ta Kasar Ba Sai Wasu Mutane Dake Zaune a Wajen Kasar Wadanda basusan Halin Da Kasar Ke Ciki Ba.

Yace Wannan Babbar Barazana Ce Ga Gwamnatin Shugaban Kasar

ALLAHU AKBAR: Matashi Dennis kenan wanda ya karɓi addinin musulunci inda ya canza suna zuwa Adam.Allah ya tabbatar da du...
29/11/2024

ALLAHU AKBAR: Matashi Dennis kenan wanda ya karɓi addinin musulunci inda ya canza suna zuwa Adam.

Allah ya tabbatar da duga-dugansa kan musulunci tare da mu baki ɗaya.

Idan aka ce ka zaɓi mutum uku a cikin waɗannan fitattun malaman da ke cikin wannan hoto shin wanne malami da wanne malam...
28/11/2024

Idan aka ce ka zaɓi mutum uku a cikin waɗannan fitattun malaman da ke cikin wannan hoto shin wanne malami da wanne malami za ka zaɓa wanda ko a lahira kake fatan Allah a haɗa ku a tawaga guda

ANA ZATON WUTA A MAKERA.....A JIHAR KANO ANA ZARGIN WASU MANYAN MUTANE CIKI HARDA MANYAN MALAMAI  DA KARKATAR DA SHINKAF...
28/11/2024

ANA ZATON WUTA A MAKERA.....

A JIHAR KANO ANA ZARGIN WASU MANYAN MUTANE CIKI HARDA MANYAN MALAMAI DA KARKATAR DA SHINKAFAR TALAKAWA ZUWA KASUWAR SONGA😢

Tun Kafin Shugaban Hukumar Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Jihar Kano Ya Bankado Wannan Muke Da Zargi Akai, Mutumin Da Kake Bi Amatsayin Tsanin Da Zai Ka Zuwa Ga Halarar Shugaba Saw Kake Fadi Tashi Gurin Kare Muhibbar Sa Da Mutuncin Sa Da Mutuncin Iyalan Sa Ba Dare Babu Rana Shine Gwamnaty Zata Bawa Abinci Ya Baka Ya Karkatar Da Abimcin Zuwa Kasuwa Domin Saka Kudin A Aljihun Sa 😢

A Yayin Da Mafi Yawan Mabiya Suna Cikin Talauci Da Halin Ni 'Yasu Abin Da Zasu Kai Baki Na Gagarar Su Wannan Mutanen Su Zaka Ci Gaba Da Rikewa Matsayin Malaman Ka Har Ka Nunawa Duniya Kana Alfahari Da Su ? Hakkin Ku Aka Bashi Ya Baku Ya Hana Ku Kana Tunanin Wannan Ze Zam Wanda Ma'aiki Saw Zai Yi Alfahari Da Shi Kasancewar Sa Malamin Addini Anan Gidan Duniya ?

Sune S**a Shelanta Muku Zabar Muslim-muslim Aka Basu Kudi Gashi Anci Zaben Amma Shinkafar Da Gwamnatyn Ta Bayar A Baku An Hana Ku Se Yan Kalilan Daga Cikin Ku Aka Bawa Sauran Akai Habzi Da Su

Banyi Mamaki Dan Siyasa Yayi Haka Ba Dama Ze Iya Yin Hakan Koma Abin Da Yafi Hakan Amma Samun Hakan Daga Malaman Addini Wannan Kam Zambatar Addinin Allah Ne Da Miskinan Bayin Da Suke Bayan Su Kuma Allah Bazai Bari Ba

Muhyi Magaji Rimin Gado Muna Tare Da Kai 100% Yana Da Kyau Duk Wanda Aka K**a Da Hannu Cikin Wannan Case Din Kada A Rufa Masa Asiri Domin Bai Zama Wakili Na Gari Ba Ko Malami Ko Dan Siyasa.

KoDai Layine Akebi Sai Ayimana Bayani Mugane KoDai Ya Kukace😭
28/11/2024

KoDai Layine Akebi Sai Ayimana Bayani Mugane KoDai Ya Kukace😭

ALLAHU AKBAR: yanzu yanzu Anfara Gudanarda Sallahne Rokon Ruwa A Masalacin Annabi SAW Hoto Inside the Haramain
28/11/2024

ALLAHU AKBAR: yanzu yanzu Anfara Gudanarda Sallahne Rokon Ruwa A Masalacin Annabi SAW

Hoto Inside the Haramain

An zargi Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, da badakalar Naira biliyan  N110.An bayyana Bello a matsayin wanda ake...
27/11/2024

An zargi Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, da badakalar Naira biliyan N110.

An bayyana Bello a matsayin wanda ake nema tun a watan Afrilu 2024 daga Hukumar Yaki da Rashawa da Hana yi wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC). Sai dai a ranar Talata, ya mika kansa ga hukumar, inda aka gurfanar da shi a gaban kotu kan tuhumar cin amanar jama’a da wasu laifuffuka masu alaka da rashawa.

Jaridar ATP News ta ruwaito cewa, bayan Yahaya Bello ya mika kansa a ofishin EFCC da ke Abuja, an k**a shi tare da shirin gurfanar da shi a kotu a ranar Laraba (yau).

Shari’ar da aka sanya lamba FCT/HC/CR/778/24 tana da alaka da zarge-zargen badakala ta kudi da s**a kai jimillar Naira biliyan 110,446,470,089.

Ana tuhumar Yahaya Bello tare da wasu mutum biyu, Umar Shuaibu Oricha da Abdulsalam Hudu, a matsayin abokan laifi.

A baya, ATP News ta 'ruwaito cewa Mai Shari’a Maryann E. Anenih ta bayar da sammaci ga Yahaya Bello, tana umartar tsohon gwamnan da ya bayyana a kotu domin fuskantar shari’a kan zargin almundahanar Naira biliyan 110 da ake masa.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AWAINIYA.com posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AWAINIYA.com:

Videos

Share