RCN Hausa

RCN Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from RCN Hausa, Social Media Agency, Abuja.
(1)

Muna Kira Ga Gwamnatin Jihar Zamfara Da Gwamnatin Tarayya Dasu Gaggauta Kuɓutar Da Daliban Da 'Yan Ta'adda S**a Sace A J...
02/10/2023

Muna Kira Ga Gwamnatin Jihar Zamfara Da Gwamnatin Tarayya Dasu Gaggauta Kuɓutar Da Daliban Da 'Yan Ta'adda S**a Sace A Jami'ar Gusau

Daga Ƙungiyar "Arewa Media Writers"

Ƙungiyar Marubutan Arewa a kafofin sadarwar Zamani “Arewa Media Writers” ƙarkashin jagorancin shugaban ƙungiyar na ƙasa Comr Haidar Hasheem Kano, tana kira ga gwamnatin jihar Zamfara, da gwamnatin Tarayya da su gaggauta kuɓutar da ɗaliban da 'yan ta'adda s**a yi garkuwa dasu a jami'ar gusau.

Idan ba'a manta ba a ranan 22 Sep, 2023, ne wasu 'yan ta'adda s**a Shiga ɗakunan kwanan ɗaliban jami'ar gusau dake jihar Zamfara, inda s**a yi awon gaba da dalibai da dama.

Da wannan ne ƙungiyar “Arewa Media Writers” take kira ga gwamnati a kan lallai ya k**ata su dage, su kuma zage damtse wajen ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban da suke hannun 'yan ta'addan.

Ƙungiyar “Arewa Media Writers” tana Addu'ar Allah ya ƙara baiwa Iyayen yaran haƙuri, Allah ya kuɓutar da yaran cikin ƙoshin lafiya, Allah ya bamu zaman lafiya mai daurewa. Amin

✍️✍️✍️ Muhammad Kwairi Waziri, National Directer Media And Publicity II Of Arewa Media Writer's

Gwamnan Jihar Jigawa Malam Umar Namadi FCA, ya kaddamar da fara raba tallafin Naira biliyan daya da Miliyan tamanin 1,08...
15/09/2023

Gwamnan Jihar Jigawa Malam Umar Namadi FCA, ya kaddamar da fara raba tallafin Naira biliyan daya da Miliyan tamanin 1,080,000,000 domin rabawa talakawan kananan hukumomi 27 da ke fadin jihar.
..Haka zalika Gwamnan ya sake kaddamar da rabawa al'ummar jihar abinci, shinkafa buhu dubu 47,412, taliya kwali dubu 33,229 da Masara buhu dubu 8,300.

A yau Jumma'a Mai Girma Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi, FCA, ya sake kaddamar da rabon tallafin Naira 10,000 ga mutane 4,000 a dukkannin kananan hukumomi 27 da ke fadin jihar, wanda ya k**a Naira biliyan daya da Miliyan tamanin 1,080,000,000, taron sake kaddamar da sabon tallafin, ya gudana ne a karamar hukumar Gumel.

Gwamnan ya kuma fara raba shinkafa ta Naira biliyan biyu buhu 47,412, inda gidaje dubu 3,000 za su amfana a kowace karamar hukuma da kuma taliyar sama da Naira miliyan 900, kimanin sama da kwali 33,229 da kuma Masara buhu dubu 8,300.

Idan baku manta ba a kwanakin baya Gwamnan ya raba abinci tirela Goma, ya kuma rabawa mata dubu 10 jarin Naira 50k, bayan abincin farko ya sake raba wani, yau ma gashi ya fara raba wanda yafi na baya, don ragewa talakawan jihar halin kunci da tsadar rayuwa da suke ciki, na radadin cire tallafin Man Fetur.

Amb Muhammad Salisu Seeker
Mataimaki na musamman ga Gwamnan jihar Jigawa a bangaren bugawa, watsawa da daukan hoto.

Ana fargabar yakin Sudan zai iya haifar da barkewar cutuka masu hatsarin gaske da zasu halaka dubannin mutane.....Kungiy...
25/04/2023

Ana fargabar yakin Sudan zai iya haifar da barkewar cutuka masu hatsarin gaske da zasu halaka dubannin mutane.....

Kungiyar lafiya ta duniya (WHO) tayi gargadin hakan.

WHO tayi hasashen yiwuwar barkewar munanan cutuka a kasar Sudan dalilin zazzafan yakin da ya barke a kasar,mafi yawan dakunan gwaji (LABORATORIES) dake kasar sun koma karkashin kulawar mayaka,kuma a wadannan dakunan gwajin, akwai dumbin samfurin cutuka da ake kan gwajin su don neman maganin su,a cewar WHO....

Yanzu da dakunan gwajin s**a koma hannun mayakan, babu tabbacin ingattacen tsaro da kulawa ga wadannan cutukan, kenan akwai yiwuwar cutukan su iya bazuwa cikin kasar wanda hakan zai yi sanadin bazuwar cutukan ga dubannin yan kasar da basuji basu gani ba a cewar kungiyar lafiya ta duniya wato WHO....

Me zaku ce kan hakan ?

Gidauniyar "Fasaudat Support Foundation” Ta Sake Tallafawa Marayu Da Kayayyakin Sallah A Jihar SokotoDaga Comr Nura Sini...
19/04/2023

Gidauniyar "Fasaudat Support Foundation” Ta Sake Tallafawa Marayu Da Kayayyakin Sallah A Jihar Sokoto

Daga Comr Nura Siniya ✍️

Gidauniyar dake tallafawa marayu da mabukata "Fasaudat Support Foundation" karkashin jagorancin Amb. Fatima Ahmad Maigari, na cigaba da tallafawa talakawa marayu da kayan Sallah a cikin watan azumin ramadan a jihar Sokoto.

Gidauniyar "Fasaudat Support Foundation" assasawar Amb. Fatima Ahmed Maigari na cigaba da tallafawa marayu da kayan Abinci, kayan Sallah a Jihar Sokoto k**ar yadda gidauniyar ta saba tallafawa marayu da gajiyayyu marassa karfi a duk shekara.

Gidauniyar ta rabawa sama da marayu 500 da tallafin kayayyakin sawa a tsangayu da gidajen marayun a kananan hukumomin Dangi da Shuni a jihar Sokoto.

Za a cigaba da rabon tallafin marayun har zuwa karewar azumin watan Ramadan domin cigaba da saka marayun cikin farin ciki.

Alhamdulillah. Kishirwa ta tafi,jijiyoji sun jiku kuma lada ta tabbata da izinin Allah.Kungiyar al'ummar karamar hukumar...
17/04/2023

Alhamdulillah.

Kishirwa ta tafi,jijiyoji sun jiku kuma lada ta tabbata da izinin Allah.

Kungiyar al'ummar karamar hukumar Batsari dake jihar Katsina watau BATSARI PEOPLE'S FORUM (BAPFO) na yiwa daukacin musulman duniya barka da shan ruwa tare da fatan dacewa da alkairan watan Ramadan.

Allah Shi karba ibadun mu yasa mu a bayinsa yantattu.

ALHERI GADON BACCI: Gidauniyar Fasaudat Support Foundation Ta Rabawa Marayu Da Mabukata Tallafin Kayan Azumi A Jihar Sok...
09/04/2023

ALHERI GADON BACCI: Gidauniyar Fasaudat Support Foundation Ta Rabawa Marayu Da Mabukata Tallafin Kayan Azumi A Jihar Sokoto

Daga Comr Nura Siniya

Gidauniyar tallafawa marayu da masu Karamin Karfi mai suna “Fasaudat Support Foundation” ta Amb. Fatima Ahmad Maigari (Uwar Marayu) ta rabawa kimanin marayu da mabukata sama da mutun dubu uku tallafin kayan azumi a unguwar Talakawa da Minananta da ke a jihar Sokoto.

gidauniyar ta raba tallafin kayan azumin gida-gida ne wanda ya hada da Sikari, Shinkafa da wake kwai da makaroni da kudaden cefane domin rage masu radadin halin matsi a watan Ramadan.

A karshe shugabar gidauniyar Amb. Fatima Ahmad Maigari tasha alwashin cigaba da rabon tallafin kayan azumin ne domin ganin mutane da yawa sun amfana kafin karewar azumin watan Ramadan.

07/04/2023
DA ƊUMI-ƊUMINSA: Hadakar ƙungiyoyin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya sun zabi mai girma tsohon Gwamnan jihar Zamfara k...
25/03/2023

DA ƊUMI-ƊUMINSA: Hadakar ƙungiyoyin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya sun zabi mai girma tsohon Gwamnan jihar Zamfara kuma zababben Sanatan Zamfara ta yamma Dr. Abdul’aziz Yari Abubakar (Shattiman Zamfara) a matsayin wanda zai tsaya takarar kujerar Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya (10 Assembly).

Kungiyar Amalgamated Support Group of APC, gamayyar kungiyoyin magoya bayan jam’iyyar APC kimanin 2,400, sun amince da takarar Abdul’aziz Yari Abubakar a matsayin shugaban majalisar dattawa a majalisa ta 10.

A gaban wakilan dukkanin kungiyoyin da daraktocinsu, babban darakta na kungiyar Amalgamated, Engr. Dokta Kailani ya bayyana hakan ne a babban ofishinsu a jiya 24 ga watan Maris 2023. Shugaban ya ce tallafin nasu ya kasance ne bisa la’akari da dimbin gogewa da halayen shugabancin tsohon Gwamna wanda insha Allahu zai yi tasiri mai kyau wajen ciyar da kasa gaba. Ya kuma ja hankalin dukkan Sanatocin Majalisar ta 10 da su marawa Sen Yari baya kan wannan matsayi.

Daga jiya Jumma’a 24 ga watan Maris 2023 kungiyoyin da ke goyon bayan Amalgamated za su ci gaba da ba da goyon bayansu ga nasarar da mai girma Gwamna Abdul’aziz Yari Abubakar ya samu ya jagoranci majalisa ta 10 a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Muna fatan Allah SWT ya cigaba da sanya albarka a cikin wannan lamarin, Allah ya bamu cikakkiyar Nasara. Amin

Al’mansoor Gusau,
Babban daraktan yada labarai na mai girma tsohon Gwamnan jihar Zamfara, Dr. Abdul'aziz Yari Abubakar.

Kamar akwai adawa mai ƙarfi tsakanin kamfanin wutar lantarki da watan Ramadan?Hoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache
24/03/2023

Kamar akwai adawa mai ƙarfi tsakanin kamfanin wutar lantarki da watan Ramadan?

Hoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache

Wani Matashi Ya Fara Tattaki Bisa Raƙumi Zuwa Abuja Domin Yi Ma Babban Limamin Masallacin Abuja Farfesa Ibrahim Makari B...
24/03/2023

Wani Matashi Ya Fara Tattaki Bisa Raƙumi Zuwa Abuja Domin Yi Ma Babban Limamin Masallacin Abuja Farfesa Ibrahim Makari Barka Da Shan Ruwa

Daga Comr Nura Siniya ✍️

Wani matashi daga jihar Katsina mai suna Ibrahim Hamisu wanda akafi sani da “Baƙin Balarabe ya fara tattaki a bisa raƙumi daga Katsina zuwa Abuja Domin Kai Ziyarar barka da shan ruwa ga babban limamin masallacin Abuja wato “Farfesa Ibrahim Maqari

A cewar matashin Ibrahim Hamisu, ya ce ya fara yin wannan tattakin ne domin girmama ga Farfesa Ibrahim Makari domin yi mashi barka da shan ruwa tare da neman tabaraki a matsayin shi na Uba kuma babban malamin addinin musulunci a Najeriya.

Bakin Balarabe ya bayyana cewa yana kyautata zaton zai sauka Abuja ne ranar da azumi zai cika Goma ga watan Ramadan.

Idan zaku iya tunawa a shekarar da ta gabata ne 2022 Bakin Balarabe ya je Abuja akan raƙumi inda ya halarci babban taron Jam'iyyar APC na ƙasa har ya gana shugaban jam'iyyar Sanata Abdullahi Adamu Wanda daga baya yabar jam'iyyar APC ya koma PDP a yanzu.

A ƙarshe Bakin Balarabe ya ce idan ya isa Abuja bazai dawo Katsina ba har sai ya sake yin tilawar saukar Al'qur'ani mai girma wajen Farfesa Ibrahim Makari sannan zai dawo gida.

Masu karatu wane fata za kuyi mashi?

DA DUMIDUMINSA: CBN Ya Rabawa Bankuna Tsoffin Kudaden Naira 1,000 Da Naira 500 Domin Rabawa Kwastomomi Saboda Kudo Ya Wa...
23/03/2023

DA DUMIDUMINSA: CBN Ya Rabawa Bankuna Tsoffin Kudaden Naira 1,000 Da Naira 500 Domin Rabawa Kwastomomi Saboda Kudo Ya Wadata A Fadin Kasa

An tanadi hukuncin ɗaurin rai da rai ga duk mutumin da ya ce mai neman jinsi ne a UgandaHoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache
22/03/2023

An tanadi hukuncin ɗaurin rai da rai ga duk mutumin da ya ce mai neman jinsi ne a Uganda

Hoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache

Jam'iyyar Labour ta lashe zaben gwamnan Abia,
22/03/2023

Jam'iyyar Labour ta lashe zaben gwamnan Abia,

Mesut Ozil ya yi ritaya daga fagen tamola yana da shekaru 34Hoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache
22/03/2023

Mesut Ozil ya yi ritaya daga fagen tamola yana da shekaru 34

Hoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache

Za a daɗe ba a shawo kan matsalar ƙarancin ruwa ba a Somaliya  Hoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache
22/03/2023

Za a daɗe ba a shawo kan matsalar ƙarancin ruwa ba a Somaliya

Hoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache

Buhari ya ƙi sanya hannu kan dokar da ta bai wa majalisa damar gayyatar shugaban ƙasaCewar shugaban majalisar dattawa Ah...
22/03/2023

Buhari ya ƙi sanya hannu kan dokar da ta bai wa majalisa damar gayyatar shugaban ƙasa

Cewar shugaban majalisar dattawa Ahmed Lawan,

Hoto 📷 Abbakar Aleeyu Anache

Kotu ta yi watsi da buƙatar Abba Kyari,Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da buƙatar da tsohon shugaban sashen...
22/03/2023

Kotu ta yi watsi da buƙatar Abba Kyari,

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da buƙatar da tsohon shugaban sashen tattara bayanan sirri na rundunar 'yan sandan Najeriya Abba Kyari ya gabatar a gabanta, yana neman kotun ta yi watsi da zarge-zargen da ake yi masa.

Yayin zaman kotuna a ranar Laraba alƙalin kotun mai shari'a Emeka Nwite ya yi watsi da buƙatar Abba Kyari, yana mai cewa kotun na da hurumin sauraron ƙararrakin da suke da alaƙa da ta'ammali da miyagun ƙwayoyi k**ar yadda kundin tsarin mulki da dokar da ta kafa hukumar NDLEA s**a ba ta dama.

Abba Kyari ya faɗa wa kotun cewa hukumar NDLEA ta yi gaggawar gabatar da shi a gaban kotu, tun kafin a kammala bincike, yana mai cewa k**ata ya yi hukumar ta bai wa 'yan sanda damar gudanar da binciken cikin gida, kafin ita NDLEA ta ɗauki mataki.

Ya ƙara da cewa 'yan sanda sun gudanar da bincike kan lamarin kuma har sun gabatar da rahoton cikin gida ga rundunar 'yan sanda.

Jami'in 'yan sanda ya ce za a gabatar da shi a gaban kotu ne kaɗai, idan 'yan sanda s**a kammala gudanar da bincike.

Ya kuma ce dokar aikin 'yan sanda ta ce hukumar kula da ayyukan 'yan sanda ta ƙasar na da ikon da za ta gudanar da bincike tare da ladabtar da jami'an 'yan sanda, k**ar yadda majalisar ƙoli ta ayyukan shari'a ke da ikon ladabtar da ma'aikatan shari'a.

To sai dai alƙalin kotun ya ce ikon da hukumar kula da ayyukan 'yan sandan ke da shi , bai zarta ikon da kotun tarayyar ke da shi ba.

Kyari mai muƙamin mataimakin kwamshinan 'yan sanda, tare da wasu mutum huɗu da ke aiki a rundana ɗaya na fuskantar tuhume-tuhumen haɗin baki wajen safarar hodar ibilis da nauyinta ya kai kilogiram 17.55

Abba Gida-gida ya buƙaci masu taya shi murna su yi masa addu'a maimakon dogon tattaki,Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano ...
22/03/2023

Abba Gida-gida ya buƙaci masu taya shi murna su yi masa addu'a maimakon dogon tattaki,

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya buƙaci masu yin doguwar tafiyar ƙafa domin nuna murnarsu kan samun nasarar zaɓe da ya yi, da cewa su daina.

A maimakon haka ya buƙace su da su yi masa addu'ar samun nasara a mulkinsa domin maido da ƙwarin gwiwar da 'yan jihar s**a rasa cikin shekaru takwas da s**a gabata.

A wata sanarwa da zaɓaɓɓen gwamnan ya fitar, mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawunsa Sanusi Bature Dawakin Tofa, Abba ya buƙaci magoya bayansa da 'yan jam'iyyarsa ta NNPP da su yi masa addu'ar samun nasara a mulkinsa.

Sabon gwamnan ya ce yin addu'a kaɗai ta wadatar wajen nuna murna ga nasarar da ya yi a zaɓen na ranar Asabar, ba sai mutum ya shafe tafiyar kilomitoci masu yawa a ƙafa ba.

Musamman a cewar sanarawar, idan aka yi la'akari da halin rashin tsaro na matsalar 'yan fashin daji da masu garkuwa da mutane, waɗanda ke barazana ga zirga-zirgar jama'a da kayayyaki a faɗin ƙasar.

Yayin da yake gode wa magoya bayansa na ciki da wajen jihar Kano, zaɓaɓɓen gwamnan ya buƙaci masu doguwar tafiyar ƙafa da su daina, domin kuwa a cewarsa hakan ba zai taimaka wajen magance tarin matsalolin da ke jiran sabuwar gwamnatinsa ba, k**ar yadda ya bayyana.

Jama'a Idan INEC Tafitar da sak**akon Cewa Dr Nasiru Yusuf Gawuna Yaci Zabe, Dan ALLah Banda Guje Guje A kan Hanya. Ayi ...
19/03/2023

Jama'a Idan INEC Tafitar da sak**akon Cewa Dr Nasiru Yusuf Gawuna Yaci Zabe, Dan ALLah Banda Guje Guje A kan Hanya. Ayi Murna Cikin kwanciyar Hankali da Lumana…

Daga Abdullahi Adamu

Dikko Radda Bai Cancanci Ya Mulki Jihar Katsina Ba, - Daga Comr Nura SiniyaA mahangar siyasa jihar Katsina bata yi lalac...
17/03/2023

Dikko Radda Bai Cancanci Ya Mulki Jihar Katsina Ba, - Daga Comr Nura Siniya

A mahangar siyasa jihar Katsina bata yi lalacewar da Ɗan takarar gwamna na APC Dikko Radda, zai mulke ta ba, duba da irin tarin damarmakin da ya samu a baya musanman kujerar SMEDAN da ya riƙe tsawon shekara biyar wacce ta zama asara ga ƴan kasuwar jihar Katsina ganin yadda bai taimaki kowa ba kuma bai gina kowa a jihar Katsina.

“A damar da Dikko Radda, ya samu a SMEDAN baka iya nuna matashi guda 5 a jihar Katsina wanda ya samarwa aiki domin dogaro da kai sai dai kashe masu zuciya da ya yi ta hanyar kewaya gari da su suna ihu akan mota a matsayin sojojin baka.

“A lokacin da Dikko Radda, yana riƙe da kujerar SMEDAN, kowa yasan yadda yai amfani da ƴan kasuwar jihar Katsina ta hanyar raba masu satifiket da sunan zai basu tallafi amma har yanzu basu amfana da komai ba face tagumi wani abin takaici a shekaru biyu da s**a wuce har gobara aka yi a babbar kasuwar Central, amma Dikko Radda har yau ko jaje bai masu ba bare ya basu wani tallafi. Wannan shi ya nuna cewa ba kishin al'umma da son cigaban jihar Katsina ke gaban shi ba.

“A rahoton jaridar Daily Trust, ta fitar na ranar 7 ga watan Sep. 2022. ta ruwaito cewa lokacin Dikko Radda, yana riƙe da Kujerar SMEDAN ne aka samu taɓarɓarewar cigaba wanda sama da ƴan kasuwa miliyan 2 a Najeriya s**a samu karayar jari da koma bayan tattalin arziƙi.

Haka zalika, a shekarar 2021. an zargi Dikko Radda, da haɗa baki da ƴan ƙwangilar boge kusan guda 33 (Unverified Contractors) wajen salwantar da biliyan 1.3b k**ar yadda Aderemi Ojekunle ya rubuta. Wanda kusan lokacin ne shugaba Buhari, ya bashi naira biliyan 75 da nufin ya rabawa mutane masu matsakaitan sana’o’i a lokacin Corona amma Inyamurai da Yarbawa ne kaɗai s**a amfana da wannan tallafin. abin takaici jihar da ya fito Katsina itace jiha ta 2 da tafi kowace jiha fama da talauci a jahohin Arewa maso yamma amma babu wani ɗan kasuwa da zaka nuna ya amfana da wannan tallafin a jihar Katsina.

A baya Dikko Radda, ya riƙe shugaban ƙaramar hukumar Charanchi amma babu wani abin azo a gani da ya tsinanawa garin sai dai kashe mu raba da aka zargi ya riƙa yi da Kansilolin shi.

Kuskuren da Katsinawa za suyi mafi muni shi ne zaɓar Dikko Radda a kowane irin mataki na shugabanci domin bai cancanci koda takarar Kansilan yankinsa ba.

Yan Bindiga Sun Tare Motar KTSTA Sun Kashe Fasinjojin Tare Da Raunata Wasu A Jihar KatsinaDaga Comr Nura Siniya Wasu ƴan...
17/03/2023

Yan Bindiga Sun Tare Motar KTSTA Sun Kashe Fasinjojin Tare Da Raunata Wasu A Jihar Katsina

Daga Comr Nura Siniya

Wasu ƴan bindiga sun tare motar hukumar Sufuri ta jihar Katsina KTSTA inda s**a kashe kashe fasinjoji tare da tafiya da kusan mutun 9 cikin daji, tare da raunata wasu a cikin motar a garin Dutsen kura.

“A rahoton da muka samu ƴan bindigar sun yin Garkuwa da Fasinjojin KTSTA ne akan hanyar su ta zuwa ƙaramar hukumar Batsari bayan tasowar su daga cikin garin Katsina.

lamarin ya faru a yau da misalin ƙarfe 3 na marecen ranar Alhamis a daidai Dutsin Kura a hanyar zuwa Batsari.

Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke Shine Ɗan Takarar Gwamna Mafi Samun Karɓuwa A Jihar Katsina - Daga Comrade Nura Siniya Alƙal...
15/03/2023

Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke Shine Ɗan Takarar Gwamna Mafi Samun Karɓuwa A Jihar Katsina - Daga Comrade Nura Siniya

Alƙalumman siyasa sun nuna cewa za a shiga zaɓen Gwamna a jihar Katsina Sen. Yakubu Lado na PDP dana kaso 70 Dikko Radda na APC yana da kaso 30 na goyon bayan jama'ar jihar Katsina

A binkicen da masana harkokin siyasa s**a gudanar akan goyan baya da karɓuwan da Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke yake samu baya rasa nasaba da yadda yake da son jama'a da kyautata rayuwar al'umma musanman marayu da ƴan gudun hijira da talakawa mara galihu a fadin jihar katsina.

“A mahangar siyasa idan muka yi duba da yadda talakawa suke ƙauracewa jam'iyyar APC mai mulki a daidai wannan lokacin baya rasa nasaba da ƙunci da talauci gami yunwa da matsalar rashin tsaro da jam'iyyar ta jefa al'ummar jihar Katsina a ciki wanda hakan ya jefa rayuwar dubban jama'a cikin tararrab

A ɗayan bangaren gwamnatin ta shekara 8 kan karagar mulki bata tsinanawa jama'a komai ba face ɗinbin bashi na tashin alƙiyama da taɓarɓarewar ilimi koma baya ta fuskar lafiya asibitoci sun lalace babu magani ga basuss**an da ƴan fansho suke bin gwamanti wanda hakan yai Sanadiyar mutuwa wasu tsofaffin da yawa ga rashin gudanar ayyukan raya ƙasa.

A yanzu duk inda zaka shiga ciki da wajen Katsina maganar Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke ya ake a kasuwanni da majalisun gari da ƴan tabur tebur domin a ganin su shine yafi kowane ɗan takara cacanta ya zama gwamnan jihar Katsina.

Insha Allahu jihar Katsina 2023 ta Sen Yakubu Lado Ɗanmarke ce da yardar Allah.

Shahararrun Faskoki Kuma Fitattun Yan Siyasa Da Jam'iyyar PDP Ta Kora A Jihar Kebbi Daga Jam'iyyar,Daga Abbakar Aleeyu A...
15/03/2023

Shahararrun Faskoki Kuma Fitattun Yan Siyasa Da Jam'iyyar PDP Ta Kora A Jihar Kebbi Daga Jam'iyyar,

Daga Abbakar Aleeyu Anache

Jam'iyyar PDP a jihar Kebbi ta k**a hanyar wargajewa biyo bayan korar jiga-jiganta 7 bisa zargin yiwa jam'iyyar zagon kasa a cewar sanarwa,

Alamu na cigaba da nuna cewa wankin hulla yana neman ya kai jam'iyyar PDP rana a jihar Kebbi a dai-dai lokacin da ake cigaba da tunkarar zaben gwamnoni da yan majalisu,

PDP ta shiga rudani a Kebbi inda uwar jam'iyyar ta bada wata sanarwa ga manema labarai kan korar jiga-jiganta 7 daga jam'iyyar bisa zargin su da yiwa jam'iyyar zagon kasa,

Akwai badakala kan rikicin jam'iyyar adawa ta PDP wanda ya kwashe shekaru ana cece-kuce kawo yanzu ba'a samu dai-dai to tsakanin manyam jiga-jigan ba an rasa zaune an rasa tsaye,

Uwargidan Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Katsina A Ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Hajia Zainab Sani Abacha Ta Gana Da Kungiyoyin Ma...
13/03/2023

Uwargidan Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Katsina A Ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Hajia Zainab Sani Abacha Ta Gana Da Kungiyoyin Malamai Mata, A Jihar Katsina

Mazaje Masu Neman Kudin Aure Don Su Kare Kansu Daga Zina Ya Allah Ka H**e Musu." Cewar Nanerh Hawwerh
13/03/2023

Mazaje Masu Neman Kudin Aure Don Su Kare Kansu Daga Zina Ya Allah Ka H**e Musu." Cewar Nanerh Hawwerh

Ko Mai Yasa Masu Riƙe Da Madafin Iko A Jihar Zamfara Ke Ko In Kula Da Matsalilin Jihar?Daga Mubarak Yahaya  SalihuAl'umm...
13/03/2023

Ko Mai Yasa Masu Riƙe Da Madafin Iko A Jihar Zamfara Ke Ko In Kula Da Matsalilin Jihar?

Daga Mubarak Yahaya Salihu

Al'ummar jihar Zamfara na cikin wani hali na rashin tsaro talauci rashin ilimi ingantacce rashin ruwan sha amma duk da haka bamu tsira daga shugabanni masu nuna ko oho akan matsalolin mu ba.

Lokaci yayi da ya k**ata mu nemawa kanmu yanci ta hanyar zaben shuwagabanni na kwarai a jihar mu mai Albarka ta zamfara.

Ko da yake wani lokaci ina alakanta matsalolin jihar zamfara da rashin dace da shugabanni masu kishinta wa'inda ana girmamasu a fadin
Kasar nan amma sun kasa
magance matsalar jihar ta mu didda ikirarin su na cewa suna kaunar jihar.

Masu madafin iko a jihar zamfara sun gagara gyara harkar ilimin jihar didda kasancewar ilimi ya zama ginshiki a rayuwar dan adam.

Abun takaicin ma shine yadda masu madafin ikon jihar zamfara ke bawa harkar siyasa muhimmanci basaba harkar ilimin al'ummar jihar wannan muhimmancin.

Rashin ingantancan ilimi a cikin fadin jihar zamfara yayi sanadiyyar ruguza duk wani jindadin da dan adam ke bukata a rayuwar yau da kullum kuma wannan yasamo asali ne na rashin jagoranci mai kyau a cikin fadin jihar zamfara.

A wani bangaren ni Mubarak Yahaya Salihu ina alakanta matsalar jihar zamfara da rashin manyan yan adawa a siyasar jihar tamu ta zamfara wanda hakan ya zamo siyar koma bayan wasu al'amuran jihar ta fuskar siyasa.

Amma kuma muma kanmu al'ummar jihar munada tamu matsalar wacce itama tabada gudun muwar koma bayan cigaban jihar musamman ta fuskar siyasa. Abun da nake nufi anan shine kaso 70 na al'ummar mu siyasar uban gida mukeyi ba cancanta ba.

Akarshe ina rokon Allah ya azurta jihar zamfara da shugabanni nagari masu kishin jihar ba aljihun su ba.

YANZU YANZU: Yanzu haka Wuta tana ta ci a babbar kasuwar kayayyaki ta Singa dake jihar Kano, mun sami labarin cewa tun c...
13/03/2023

YANZU YANZU: Yanzu haka Wuta tana ta ci a babbar kasuwar kayayyaki ta Singa dake jihar Kano, mun sami labarin cewa tun cikin dare wutar ke ci amma har yanzu bata dakata ba.

Shugaban Karamar Hukumar Zuru Ya Yabawa Kokarin Gwamnatin Jihar Kebbi Na Kubutar Da Mutum 35 Daga Hannun Masu Garkuwa Da...
09/03/2023

Shugaban Karamar Hukumar Zuru Ya Yabawa Kokarin Gwamnatin Jihar Kebbi Na Kubutar Da Mutum 35 Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane,

Daga Abbakar Aleeyu Anache

Bayanai daga karamar hukumar Zuru da ke jihar Kebbi a arewacin Najeriya sun tabbatar da an kubutar da wasu mutane kimanin mutum 35: da yan bindiga s**a yi garkuwa da su a garin Zodi,

Gajere ya yabawa gwamnan jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu bisa Jajirccewarsa wajen aiwatar da manufofin gwamnati na aiwatar da ayyukan wanzuwar zaman lafiya,

Da yake zantawa da manema labarai Bala Gajere ya Jinjinawa gwamnan kan rawar da yake takawa wajen samar da zaman lafiya da inganta harkokin tsaro a fadin jihar,

Gwamnatin Jihar Kebbi a karkashin jagoramcin Sanata Abubakar Atiku Bagudu ta Kubutar da su daga hannun masu garkuwa da mutane kana Hon Bala Gajere ya amshi mutum 35 da Gwamnatin jihar Kebbi ta kubutar da su a babbar sakatereyar Zuru,

Bala Gajere ya cigaba da cewa mutanen an dauke su daga garin Zodi ne sannan ya bayyana cewa wannan yana cikin Kokarin da Gwamnatin jihar Kebbi ta keyi don kawo karshen wannan matsala da muke fama da ita,

Gajere ya tabbatar wa al'ummar Zuru da cewa Gwamnatin jihar Kebbi ta nanan tana aiki tukuru don wanzar da zaman lafiya a kowane bangare na jihar Kebbi,

A cewar shugaban karamar hukumar Zuru Hon Muhammad Bala Isah Gajere Skudu Talban Zuru ya ce an kubutar da mutanen ne da hadin gwiwar jami'an tsaro da taimakon Gwamnatin Jihar Kebbi,

Daga karshe Hon Bala Gajere ya ba mutanen da aka kubutar hakuri da kai su asibiti don duba lafiyar su tare da basu tabbacin cewa Gwamnatin jihar Kebbi tana iyakar bakin kokarinta wajen murkushe yan ta'adda,

Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke Bai Janye Takarar Shi Ba - Daga Comr Nura Siniya Labarin Da Wasu Batagari Maƙiya Cigaban Jih...
08/03/2023

Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke Bai Janye Takarar Shi Ba - Daga Comr Nura Siniya

Labarin Da Wasu Batagari Maƙiya Cigaban Jihar Katsina Suke Yaɗawa Cewa Sanata Yakubu Lado Ya Janye Takarar Shi Ba Gaskiya Bane Ƙaryane

Har yanzu Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke, shi ne ɗan takarar gwamnan jahar katsina na PDP wanda yake da cikakken goyon baya da hadin kan al'ummar jihar Katsina.

Wannan labarin ƙanzon kurege ne na sharri da yarfe da ɓatanci irin wanda jam'iyyar APC s**a saba yi domin ɓatawa Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke, suna a daidai lokacin da suke fuskantar barazanar faɗuwa zaɓe don cimma wata baƙar manufa tasu wanda labarin baya da tushe b***e mak**a.

Da wannan ake kira ga jami'an tsaro da su yi gaggawar ɗaukar mataki domin hakunta duk wani mutun da aka samu yana da hannu wajen yada irin wannan labarin na ƙarya.

“An yi kira ga al'ummar jihar Katsina da suyi watsi da da irin wannan labarin da wasu mutane mararsa kishi suke yadawa domin neman mulkin ta hanyar yaudara.

A ƙarshe Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke, ya nemi alfarmar al'ummar jihar Katsina da su fito ƙwansu da ƙwarkwata su zaɓi Jam’iyyar PDP tun daga zaɓen Gwamna zuwa ƴan majalissar dokoki, a ranar Asabar mai zuwa domin gina sabuwar jihar katsina.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when RCN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share


Other Social Media Agencies in Abuja

Show All