Jimina Hausa

Jimina Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jimina Hausa, Media/News Company, .
(1)

Wani Matashi A Jihar  Gombe Ya Kirikiri Injin Bayin Ruwa Wanda Baya Amfani Da Man Fetur Ko Hasken RanaDaga Muhammad Kwai...
10/01/2024

Wani Matashi A Jihar Gombe Ya Kirikiri Injin Bayin Ruwa Wanda Baya Amfani Da Man Fetur Ko Hasken Rana

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Matashin mai suna Malik Muhammad Kumo, ɗan asalin jihar Gombe ya zabi samar da injin bayin ne domin hucewa al'ummar yankunan karkara takaicin tsadar man fetur da kuma tsadar inji mai amfani da hasken rana.

Malik Muhammad dai ya hada irin wannan inji da ke samar da ruwa ta hanyar amfani da batirin mota da wasu injuna da koyel, inji yana tashi da key kamar yadda ake tada mota, yana diri yana chajin batir har lokacin da ka gaji ka kashe shi, yana awa a shirin da huɗu bai mutu ba, a jikin sa harda wajen saka chaji na waya.

Wannan mataki nasa ya sa mutane da dama a yankunan karkara sha'awar noman rani, wanda ya zama sana'a a wajen mutane.

A cewar Malik Muhammad Kumo, abun alfahari ne a gare shi, wanda hakan wata babbar nasara ce da yake alfahari da ita ta sanadin mahaifinsa.

Sai dai duk da cewa wannan matashin ya ce ya samu nasarori masu yawa a baya a irin wannan fannin kirkire-kirkire, sai dai kuma akwai tarin kalubale da yake fuskanta musamman rashin kuɗi, wanda yasa ya share tsawon wata uku yana fama wajen ganin ya haɗa wannan injin a cewar sa.

Daga karshe dai yayi kira ga matasa da su yi amfani da basirar da suke da ita wajen dogoro da kansu ba tare da sai gomnati ta basu aiki ba.

Mai Buƙata Ko Ƙarin Bayani Yayi Mana Magana Ta Inbox.

07037611969

Ya Kamata Matasan Arewa Su Nisanci Shaye-shayen Miyagun Kwayoyi, Domin Yin Rayuwa Mai Inganci..Kiran kungiyar marubutan ...
09/01/2024

Ya Kamata Matasan Arewa Su Nisanci Shaye-shayen Miyagun Kwayoyi, Domin Yin Rayuwa Mai Inganci
..Kiran kungiyar marubutan Arewa "Arewa Media Writers" ga iyaye da su tashi tsaye wurin kula da tarbiyyar 'ya'yansu matasa maza da mata.

Shaye-shaye ya zama ruwan dare a tsakanin al'umma musamman ma matasa maza har da ma mata, masu Aure da wadanda ba su da shi.

Shaye-shaye na nufin duk wani yanayin da mutum zai sa kan shi don sauya yanayin tunaninsa ko nazarin shi ta yadda ba zai iya auna ya kamata da akasin haka ba.

Shaye-shaye na zuwa ne a yayin da mutum ya afka cikin shan ƙwayoyi, sabanin yadda likita ya ƙayyade a sha, shan giya ko tabar wiwi da dai sauran nau'ikan sinadarai masu bugar da mutum ko su kai shi ga maye, da aikata wasu abubuwa na rashin hankali.

Wasu daga cikin dalilan da ke angiza wasu shiga shaye-shayen sun hada da jahilci, matsalolin rayuwa, al'ada, hulda da abokan banza, sakacin iyaye, yanayin wurin zama, ko aikin karfi da kuma samun ƙwayoyin cikin sauƙi.

Shaye shaye na zubar da mutumci, janyo talauci da jahilci, ciwon huhu, ciwon hauka, ciwon hanta, ciwon kansa, ciwon suga, da kuma ciwon sanyin ƙashi, Sannan yana kawo lalaci, da rashin kuzari, yadda mai shaye shaye, ba ya iya yin wani kataɓus, tare da lalacewar mazakuta da sauran su. Yawan tunani mai tsanani ma na iya kai ga ciwon hawan jini da zuciya.

Kungiyar marubutan Arewa "Arewa Media Writers" karkashin jagorancin shugaban kungiyar na kasa Comr Haidar Hasheem, ta yi nazari wajen nemo hanyoyi da shawarwari da za'a bi wajen magance matsalar shaye shaye mussamman a Arewacin Najeriya.

Duk da irin hoɓɓasan da gwamnati da hukumomi a matakai daban-daban ke gudanarwa wajen hana shaye shaye, safarar ƙwayoyi da sauran kayan maye, har ila yau ya zama dole iyaye su tashi tsaye wurin kula da tarbiyyar yara da matasa, sannan su bai wa jami'an tsaro, 'yan banga, da 'yan kwamitin cigaban unguwanni, domin ganin an kawo sauyi ga rayuwar wadannan matasa.

Ko da yake akwai wasu iyaye da suke goya wa yaran su baya idan sun aikata ɓarna domin wasu iyayen ne ke ruwa da tsaki don hana doka ta yi aikinta a yayin da aka gano sun aikata ba daidai ba.

Sannan ya zama dole iyaye, manyan unguwa da duk wasu masu fada a ji a unguwanni su riƙa kula da harkokin yaransu na yau da kullum. Su kuma kula da irin abokai ko kawayen da yaransu suke hulda da su.

Dole ne gwamnati, sarakuna da malaman addinai na musulmi da kirista su ma su tashi tsaye wurin tsawatarwa da fadakar da al'umma illar shaye-shaye ta mahangar addini da rayuwa.

Dole ne kuma al'umma su ba da hadin kai wurin taimakawa jami'an tsaro da jami'an yaki da sha da fatauci da shan miyagun ƙwayoyi wurin gudanar da ayyukansu.

Sannan a daina ƙyamatar 'yan shaye shaye domin ba mu san ko wata rana za su shiriya, su yi watsi da muguwar halayyarsu ba.

Kungiyar "Arewa Media Writers" na yiwa dukkanin al'ummar yankin Arewa fatan Alkhairi, tare da Addu'ar Allah ya shiryar mana da matasanmu.

EFCC ta yi ram da shugabannin bankunan Zenith, Providus da Jaiz kan badakalar kudin da Betta Edu tayi
09/01/2024

EFCC ta yi ram da shugabannin bankunan Zenith, Providus da Jaiz kan badakalar kudin da Betta Edu tayi

Ko  Meya Sa Ba'a Samun Waɗannan Baburan A ƙauye ?
09/01/2024

Ko Meya Sa Ba'a Samun Waɗannan Baburan A ƙauye ?

Wadannan sune alkalan da za su yanke hukunci a shari'ar Kano da ake sa ran gudanarwa ranar Juma'a mai zuwa 12 ga Janairu...
09/01/2024

Wadannan sune alkalan da za su yanke hukunci a shari'ar Kano da ake sa ran gudanarwa ranar Juma'a mai zuwa 12 ga Janairun 2024

Alkalan sun hadar da

1-Justice John Inyang Okoro

2-Justice Kudirat Motonmori Olatokunbo

3-Justice Uwani Musa Abba Aji

4-Justice I.M.M. Saulawa

5-Justice Adamu Jauro

Duk wanda yake son ya fara sana'ar saida Data ko kuma yana son ya koyi yadda ake saka kudi a sayi Data ta Application di...
09/01/2024

Duk wanda yake son ya fara sana'ar saida Data ko kuma yana son ya koyi yadda ake saka kudi a sayi Data ta Application din ABBA PANTAMI DATA, ya tuntubi daya daga cikin wa 'yan nan lambobin kai tsaye ta WhatsApp
07061347599
07046868000
08126081967.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Hon Olubunmi  Tunji-Ojo ya karyata zargin da ake masa cewa kamfaninsa ya karbi kwangilar n...
09/01/2024

Ministan Harkokin Cikin Gida, Hon Olubunmi Tunji-Ojo ya karyata zargin da ake masa cewa kamfaninsa ya karbi kwangilar naira miliyan 438 daga ma aikatar jinkai ta kasa.

Inda ya ce ya yi murabus daga wannan kamfani tun shekaru 5 da s**a wuce Inda ya gabatar da ainihin kwafin murabus dinsa da takardar hukumar kula da alhakin kamfanoni wato CAC.

Ministan cikin gida bayi wani aibu akan abunda masu yada labaran karya ke sawa akansa.

Yanzu haka Betta Edu, tana hannun hukumar EFCC zata gudanar da bincike akanta, kan zargin handame biliyan 3 da doriya.
08/01/2024

Yanzu haka Betta Edu, tana hannun hukumar EFCC zata gudanar da bincike akanta, kan zargin handame biliyan 3 da doriya.

YANZU -YANZU: Shugaba Bola Ahmad Tinubu Ya Dakatar Da Ministan Harkokin Jinkai Dr. Better EduDaga Muhammad Kwairi Waziri...
08/01/2024

YANZU -YANZU: Shugaba Bola Ahmad Tinubu Ya Dakatar Da Ministan Harkokin Jinkai Dr. Better Edu

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Shugaban kasa Bola Tinubu ya dakatar da ministar harkokin jin kai da yaki da talauci, Dr. Betta Edu daga aiki ba tare da bata lokaci ba, kan badakalar N585m a ma’aikatar.

Mai baiwa shugaba Tinubu shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Ajuri Ngelale, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, ya ce hakan ya yi daidai da alkawarin da shugaban kasar ya dauka na tabbatar da mafi girman matsayin gaskiya, gaskiya, da rikon amana a tafiyar da mulkin tarayyar Najeriya.

Shugaban ya kuma umurci Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) da ya gudanar da cikakken bincike a kan duk wani abu da ya shafi hada-hadar kudi da ya shafi ma’aikatar jin kai da yaki da fatara ta tarayya, da kuma wata hukuma ko fiye da haka.

Tsohuwar Ministar Harkokin Agaji, Sadiya Umar Farouk ta isa hedikwatar EFCC domin amsa tambayoyi kan zargin karkatar da ...
08/01/2024

Tsohuwar Ministar Harkokin Agaji, Sadiya Umar Farouk ta isa hedikwatar EFCC domin amsa tambayoyi kan zargin karkatar da kudade Naira 37.1bn

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Shugaban kamfanin ABBA PANTAMI DATA, ya ziyarci Gwamnan jihar Jigawa. A yau Lahadi da dare, shugaban kamfanin ABBA PANTA...
07/01/2024

Shugaban kamfanin ABBA PANTAMI DATA, ya ziyarci Gwamnan jihar Jigawa.

A yau Lahadi da dare, shugaban kamfanin ABBA PANTAMI DATA, Comr Abba Sani Pantami, ya ziyarci mai Girma Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi, a gidanshi dake birnin Duste jihar Jigawa.

A yayin ziyarar, yana tare da Abokinsa SSA Student Affairs na Gwamnan jihar Amb Salisu, inda s**a tattauna muhimman batutuwa da mai girma Gwamna.

Haka zalika sun tattauna kan shirye-shiryen taron kaddamar da tallafin karatu ga dalibai 150 da SSA Student Affairs Amb Salisu Muhammad Seeker, zai kaddamar a ranar Talata mai zuwa da misalin karfe 11 na safe, a dakin taro na ManPower Development Institute, Dutse.

Hafiz Ali,
Babban daraktan yada labarai kuma mataimaki na musanman ga shugaban kamfanin Comr Abba Sani Pantami NIG LTD.

Labari Da Dumi-Duminsa: Shugaba Tinubu ya bada umarnin gudanar da cikakken bincike kan zargin biyan wasu kudade a wani a...
07/01/2024

Labari Da Dumi-Duminsa: Shugaba Tinubu ya bada umarnin gudanar da cikakken bincike kan zargin biyan wasu kudade a wani asusu na sirri da Ma'aikatar Agaji da Yaki da Talauci ta yi.

ABIN YABAWA: Kalli Hotunan Yadda ake Hada-Hadar cinikin ƴan wasa Na watan Janairu. A ƙaramar Hukumar Birnin Kudu Dake Ji...
07/01/2024

ABIN YABAWA: Kalli Hotunan Yadda ake Hada-Hadar cinikin ƴan wasa Na watan Janairu. A ƙaramar Hukumar Birnin Kudu Dake Jihar Jigawa.

Daga Abubakar Shehu Dokoki.

Gwamnan jihar Jigawa Mallam Umar A. Namadi FCA, ya halarci ɗaurin auren 'ya'yan Sanata Ahmed Abdulhamid Mallam Madori (N...
07/01/2024

Gwamnan jihar Jigawa Mallam Umar A. Namadi FCA, ya halarci ɗaurin auren 'ya'yan Sanata Ahmed Abdulhamid Mallam Madori (Nasiru Ahmed Abdulhamid da Amina Ahmad Abdulhamid) wadda a ka daura a jiya 6 ga watan Janairu na shekarar 2024 a masallacin Alfurqan da ke Alu Avenue, Nasarawa GRA Kano.

Gwamnan wadda shi ne alwalin Amina Ahmad Abdulhamid, ya bayar da aurenta kamar yadda addinin Musulunci ya tsara. Daga karshe limanin masallacin Dr. Bashir Aliyu Umar ya jogaranci ɗaura dukkan auren da aka daura a wannan lokacin; sannan daga karshe ya yi adduar Allah ya bawa ma'auratan zaman lafiya da ƙaruwar arziki.

Muhammad Isma'il
SA Publication and Photography.

Mun kawo sabbin tsare-tsare masu kyau, cikin Application na kamfanin ABBA PANTAMI DATA, zuwa gobe mutane zasu fara yin D...
07/01/2024

Mun kawo sabbin tsare-tsare masu kyau, cikin Application na kamfanin ABBA PANTAMI DATA, zuwa gobe mutane zasu fara yin Download din NIN Slip da NIN I'D Card da verify din BVN duk a cikin Application din mu a farashi mai sauki.

Duka wa 'yan nan abubuwan mun saka su ne a cikin upgrading din da muka yi, hatta Application dinmu da site din, ya kara sauri sosai,

Duk wanda yake da matsalar makalewar kudi ko yaga an kara mishi kudi a cikin Wallet din, don Allah ya gaggauta tuntubar daya daga cikin wa 'yan nan lambobin kai tsaye ta WhatsApp
07061347599
07046868000
08126081967.

Muna mai tabbatar muku da cewa Insha Allahu, wannan gyaran da muka yi, zaku ji dadin shi sosai.

Wanda bai yi ragista ba, ya shiga wannan link din yayi
👇
https://abbapantamidata.com/mobile/register/?referral=08130233375

Ko kuma ya shiga PlayStore ta wannan link din, yayi Download din Application din
👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.abbapantamidata.ng

06/01/2024

Yadda Wani Matashin Ya Hallaka Mahaifinsa Yau Da Safe A Unguwar Tudun Yola Dake Jihar Kano

Halin Da Wata Makabarta ta shiga sakamakon rashin kulawa a garin Gayawa dake karamar hukumar Ungogo a kano Wani  katon r...
06/01/2024

Halin Da Wata Makabarta ta shiga sakamakon rashin kulawa a garin Gayawa dake karamar hukumar Ungogo a kano

Wani katon rami ne a jikin wannan makabartar abin takaici kuma har yanzu masu jakuna da motoci suna shiga wannan makabartan da sunan diban kasa

Daga Ibn- Yusuf

Cikin satin da zamu shiga, ake tsammanin kotu zata yanke hukuncin karshe kan zaben Gwamnan jihar Kano. Tsakanin Gwamna A...
06/01/2024

Cikin satin da zamu shiga, ake tsammanin kotu zata yanke hukuncin karshe kan zaben Gwamnan jihar Kano. Tsakanin Gwamna Abba da Gawuna, wa kuke yiwa fatan Nasara?

Shin wai yanzu Jamila ta zama matar Direba kenan ?😭
05/01/2024

Shin wai yanzu Jamila ta zama matar Direba kenan ?😭

YANZU-YANZU : Mafi karancin kudin sadaki a Nijeriya ya koma Naira dubu tamanin da shida da dari biyu da goma (N86,210.00...
05/01/2024

YANZU-YANZU : Mafi karancin kudin sadaki a Nijeriya ya koma Naira dubu tamanin da shida da dari biyu da goma (N86,210.00).

ƘOSAI: Tun Kafin Zuwan Nescafe da BambitaƘOSAI yana ɗaya daga cikin abincin Hausawa wanda ake karin kumallo dashi, kosai...
05/01/2024

ƘOSAI: Tun Kafin Zuwan Nescafe da Bambita

ƘOSAI yana ɗaya daga cikin abincin Hausawa wanda ake karin kumallo dashi, kosai yanada daɗi, kuma yanada rike ciki, idan ka haɗa koko da ƙosai lokuta dayawa mutum yakan dade bai nemi abinci ba.

Wannan Yasa zuwa yanzu hatta a ƙasar wajema anayin ƙosai, akwai wanda daga Najeriya har ƙasar Amurka da Dubai suke zuwa suyi ƙosai, madallah da wannan abinci na Hausawa.

Kalli ƙosan nan dayake kan murhu, tsakani da Allah Yaburgeni, da ina kusa zansiya, kokuma nayi order ɗinsa nakaishi har gida, duk wanda yaga irin wannan ƙosan zai iya tahomin dashi, koda bamuyi magana ba, In shaa ALLAHU bazan Bashi kunya ba.

Inasonka ƙosai.

Inji: Abubakar Shehu Dokoki

Kamfanin ABBA PANTAMI DATA, ya dauki alkawarin koyar da 'yan kalare sama da mutum 80, kasuwancin yanar gizo da kuma bada...
04/01/2024

Kamfanin ABBA PANTAMI DATA, ya dauki alkawarin koyar da 'yan kalare sama da mutum 80, kasuwancin yanar gizo da kuma bada tallafin kudi na musamman don ganin an taimaki matasan.

Mun halarci taron da 'yan kalare sama da 80, s**a tuba s**a ajiye makaman su a jihar Gombe.

A yau Alhamis muka halarci taron da kwamishinan 'yan sanda na jihar Gombe CP Hayatu Usman, ya hada na karbar tuban tubabbun 'yan kalare sama da 80 da s**a tuba s**a ajiye makaman su, s**a daina fada da dabanci da sauran abubuwan da basu dace ba.

Na gabatar da jawabi a wurin, tare da bada shawarwari da kuma kira ga Gwamnatin jihar Gombe, domin ta kawo dauki na musamman ta yadda za'a samawa kowane daya daga cikin su aikin yi ko kuma jari akan sana'o'in da s**a iya don su tsaya da kafafun su.

Hakika kwamishinan 'yan sanda CP Hayatu Usman, yana matukar kokari don ganin ya gyara tarbiyar matasan jihar Gombe.

A matsayin mu na matasan jihar Gombe masu kishin jihar, dole mu jinjinawa PPRO Maheed Muazu Bauchi kan namijn kokarin da yayi wurin janyo hankalin dukkannin wa 'yan nan matasan tare da chanja musu tunani.

Yana da matukar muhimmanci ga Gwamnatin jihar Gombe, Sarakuna, Malamai, Attajirai da manyan 'yan kasuwa da su shigo cikin wannan lamarin don taimakon matasan, wanda Insha Allahu muke da yakinin hakan zai kawo chanji mai kyau a fadin jihar.

A yayin halartar taron, ina tare da abokanan aikina Adamu A. Babale Makera da Haji Shehu da Aliyu Babangida Nationall da kuma Hafizu Ali.

Yau Wata Guda Kenan Da Kisan 'Yan MAULUD Mutum Ɗari A Jihar Kaduna, Amma Shiru Kake Ji Babu Wani Abu Da Gomnati Tayi Shi...
04/01/2024

Yau Wata Guda Kenan Da Kisan 'Yan MAULUD Mutum Ɗari A Jihar Kaduna, Amma Shiru Kake Ji Babu Wani Abu Da Gomnati Tayi

Shiru an kashe mutane kamar dabbobi Kuma ance kuskure ne, babu batun biyan diyya da aka ce za'a Biya, babu batun bincike da aka ce za'a gudanar, yanzu gashi har anyi wata daya Kenan an fara mantawa.

Ni wallahi na fara tunanin cewa anya ba gomnati bace take daukar nauyi dukkanin irin matsalar tsari da take faru a wannan yanki namu na arewa ba ?

Domin mun gan cewa mutum daya kawai aka kashe a yankin kudancin Nigeria Wani mawaki ( MOHBAD ) Amma har shiru akayi na tsawon minti ɗaya, sabida sune mutanen Nigeria.

Dan haka, muma ba za muyi shiru da kisan 'yan uwan mu ba wa inda aka kashe a jihar kaduna naa gaarin tudun biri ( tudun malud) domin muna da hakki muma.

Sannan ku kuma jagororinmu muna sane da irin abun da kuke mana, kun mayar da mu tamkar dabbobi, kullun kuna kallon kawai abun da zaku samu, ba ruwan ku da irin halin da muke ciki.

Ya zamo dole a fito da mutanen da su kayi wannan aiki, kuma a hukunta su, Domin akwai rashin sanin aikin su.


✍️✍️ Abdurrahman Sani Mainagge

ALHAMDULILLAH: Mun kammala babban aikin gyaran Upgrading din site din kamfanin mu.  Bayan shafe daren jiya injiniyoyinmu...
03/01/2024

ALHAMDULILLAH: Mun kammala babban aikin gyaran Upgrading din site din kamfanin mu.

Bayan shafe daren jiya injiniyoyinmu suna aiki wanda yakai ga har sun kwana suna aiki, Alhamdulillah tun safe sun kammala Upgrading din komai ya cigaba da tafiya da kyau.

Duk wanda yake da matsalar makalewar kudi ko yaga an kara mishi kudi a cikin Wallet din, don Allah ya gaggauta tuntubar daya daga cikin wa 'yan nan lambobin kai tsaye ta WhatsApp
07061347599
07046868000
08126081967.

Muna mai tabbatar muku da cewa Insha Allahu, wannan gyaran da muka yi, zaku ji dadin shi sosai.

Shatu Garko Macen Da Tafi Kowacce Mace Kyau A Najeriya A Shekarar 2023Shin wa kuke yiwa fatan nasara a 2024 ?
03/01/2024

Shatu Garko Macen Da Tafi Kowacce Mace Kyau A Najeriya A Shekarar 2023

Shin wa kuke yiwa fatan nasara a 2024 ?

Dai-dai Da Sakan Daya Bantaba Sawa A Raina Gawuna Bazai Mulki Jahar Kano Ba, Yadda Al'ummar Jihar Kano S**a Zaɓe Shi,  K...
03/01/2024

Dai-dai Da Sakan Daya Bantaba Sawa A Raina Gawuna Bazai Mulki Jahar Kano Ba, Yadda Al'ummar Jihar Kano S**a Zaɓe Shi, Kuma Yanzu Haka Nayi Ɗinkin Rantsar Da Gawuna Lokaci Muke Jira, Cewar ~Arch Nura Zubair Yakub

Daga Shamsu Gwaska

EFCC Tana Tuhumar Babban jami’in gudanarwa na hukumar kula da harkokin zuba jari ta kasa (NSIPA), Haj. Halima Shehu, da ...
03/01/2024

EFCC Tana Tuhumar Babban jami’in gudanarwa na hukumar kula da harkokin zuba jari ta kasa (NSIPA), Haj. Halima Shehu, da Karkatar da Naira Biliyan 17 daga asusun NSIPA zuwa wasu asusu na daban cikin mako guda

DA ƊUMI-ƊUMI: Akwai Yiwuwar Man Fetur Zai Iya Komawa Naira 1,200 Kowacce Lita, Cewar NNPCMe zaku ce?
03/01/2024

DA ƊUMI-ƊUMI: Akwai Yiwuwar Man Fetur Zai Iya Komawa Naira 1,200 Kowacce Lita, Cewar NNPC

Me zaku ce?

Wallahi Sam Babu Alkairi !Wani abokina yana da fili a lokacin gwamnati ganduje har miliyan ashirin antaya masa yaki siya...
03/01/2024

Wallahi Sam Babu Alkairi !

Wani abokina yana da fili a lokacin gwamnati ganduje har miliyan ashirin antaya masa yaki siyarwa.

Yanzu yawo yake yana neman 5milion kai wallahi ko milion hudu akabashi zai karbe duk anje wajen masu siya sun ki siya sunce sai Abba Gida-gida ya sauka..

kai yan kasuwa suna tsoron abba yan siyasa suna tsoron abba.ma aikatan gwamnati suna tsoron abba kai kowama tsoron abba yake.allah karabamu da abba

Allah yakawo mana gawuna kano ta koma dai dai.mudawo bacci agidajenmu cikin nutsuwa.

Daga Shamsu Gwaska

A yanzu haka injiniyoyinmu suna sake gudanar da wani muhimmin gyara na Upgrading wanda ya zama dole a gudanar da wannan ...
02/01/2024

A yanzu haka injiniyoyinmu suna sake gudanar da wani muhimmin gyara na Upgrading wanda ya zama dole a gudanar da wannan gyaran a wannan lokacin, saboda yawan kwastomomin da muke dasu, shiyasa muka sake kulle duk wata hada-hada a Application din namu, da zaran sun kammala zamu bude a cigaba da hada-hada kamar yadda aka saba.

Muna ta kokari muna gudanar da wannan aikin ne, domin cigaba da inganta kamfaninmu domin jin dadin ku a matsayin ku na kwastomominmu.

Muna kara godiya a gareku, kan yadda kuke bamu hadin kai a kowane lokaci. Muna mai tabbatar muku da cewa Insha Allahu, wannan gyaran da muka yi, zaku ji dadin shi sosai.

Comr Abba Sani Pantami
CEO ABBA PANTAMI DATA.

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jimina Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Shortcuts

  • Address
  • Alerts
  • Videos
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share