26/03/2023
Wannan shine Dokta Sani, mazaunin unguwar Malam Goje Bauchi. mai digirin digirgir , wato PhD holder, a ilmin tsirrai. Kuma Darakta mai ritaya ne a ma'aikatar gona ta tarayya.
Saboda gudun duniya da ra'ayi kan rayuwar talaka, an bashi mota, toh amma ya kyautar da ita. Ya zauna a kasashe irin su Kuwait da Amerika da sauran su, amma har yanzu akwalar keke yake hawa. Yace idan talakan Najeriya bai samu ingancin rayuba, har abada ba zai daina hawa keke ba. Zai ci gaba da yin rayuwa irin wacce talaka ke yi. Kuma har yanzu a gidan gado yake zaune, ginin kasa a kusa da masallacin ajiya a Bauchi.
Allah ya taimaki Dokta Sani dan, gwagwarmayar kishin talakan Najeriya. Amin ya Rabbi 🙏
Marubuci: Muazu Hardawa Edita Jaridar Alheri Bauchi Dandalkura radio reporter 08062333065
Daga shafin: Muhammad Hussein Arab