Abu Ubaida Been Jarah.

  • Home
  • Abu Ubaida Been Jarah.

Abu Ubaida Been Jarah. SHAFIN ABU UBAIDA BIN JARAH PAGE NE DAYAKE YADDA SUNNAR ANNABIN RAHAMA S A W

Manzon Allah (SAW) yana cewa: "Shin ba na labarta muku addu'ar da ya kamata mutum ya yi ba lokacin da ya shiga cikin wat...
21/01/2024

Manzon Allah (SAW) yana cewa: "Shin ba na labarta muku addu'ar da ya kamata mutum ya yi ba lokacin da ya shiga cikin wata damuwa ko baƙin ciki ko jarabawar rayuwa?" Sai s**a ce: "Tabbas muna son sanin wannan addu'a ya RasulaAllah!" Sai ya ce: "Ita ce addu'ar Annabi Yunus (AS) lokacin da kifi ya haɗiye shi:

Write by Kabir Asgar

"(لا إله إلا أنت سبحانك إني كنت من الظالمين)

MALAMINA YA MAGANTU!!Ka je Mahaifiyarka Ta Yi Maka Addu’a:✍️ PROF. MUHAMMAD SANI UMAR R/LEMOAl-Imam Sulaim ɗan Ayyub Ar-...
18/01/2024

MALAMINA YA MAGANTU!!

Ka je Mahaifiyarka Ta Yi Maka Addu’a:

✍️ PROF. MUHAMMAD SANI UMAR R/LEMO

Al-Imam Sulaim ɗan Ayyub Ar-Razi, ɗaya daga cikin manyan malaman Mazhabar Shafi’iyya (Ya rasu a shekara ta 447 BH).
Yana ce wa:
“Lokacin da nake yaro ƙarami ɗan shekara goma a garinmu (Ar-Rayy) (Cikin ƙasar Iran a yanzu), sai wani baƙon malami ya ziyarci garin yana koya wa yara karatun Alƙur’ani.
Sai ya ce min: “Matso kai ma ka karanta”.
Sai na matsa, na yi ta ƙoƙarin in karanta Fatiha amma na kasa, domin harshena ya yi nauyi sosai.
Sai ya ce min: “Shin kana da mahaifiya a raye?”
Sai na ce masa, e, ina da ita.
Sai ya ce: “Ka je wurinta ta yi maka addu’a Allah ya arzutaka da karatun Alƙur'ani da na ilimi”.
Sai na ce, to.
Sai na koma gida na roƙe ta ta yi mini addu’a, sai ta yi min.

Sai ga shi na girma har na tafi garin Bagdaza na yi karatun harshen Larbaci da na Fiƙihu, sannan na dawo garinmu Ar-Rayy.

Wata rana ina zaune a masallacin Juma’a, muna karanta littafin ‘Muhktasar’ na Muzani, sai ga malamin nan mai koyar da karatun Alƙur’ani ya shigo masallacin, ya nufo inda muke ya yi mana sallama, muka amsa masa, amma bai gane ni ko wane ne ba, don ya manta abin da ya faru a can baya da jimawa.
Ya ga muna karatun Mukhtasar na Muzani, shi k*ma ga shi ba zai iya karantawa ba, sai ya tambaye ni cewa yaushe ne mutum zai iya koyon irin wannan ilimin?
Sai na ji kamar in ce masa idan mahaifiyarsa tana nan raye ya je ta yi masa addu’a, to amma sai na ji kunya na kasa faɗa masa.”

Kyakkyawar addu’a ta iyaye tana da albarka matuƙa.

Wannan mashahurin malami Al-Imam Sulaimu ya fara neman ilimi ne bayan ya haura shekara arbai’in a duniya. Amma ya zama ɗaya daga cikin hamshaƙan malamai a zamaninsa.

[Dubi, Az-Zahabi, Siyar Al-A’lam, Juzi’i na 3, Shafi na 18-19].

24/12/2023

KU DAN SAURARA KADAN ZAKU AMFANA!
DAN GANE DA MARTABAR MANZON ALLAH ZAKU AMFANA.

KU ƊAN SAURARA KAƊAN!Abdullahi ɗan Abbas ya ce: "Babu wata al'umma da SATA zata bayyana a cikinta face Allah (swt) ya je...
22/12/2023

KU ƊAN SAURARA KAƊAN!

Abdullahi ɗan Abbas ya ce:

"Babu wata al'umma da SATA zata bayyana a cikinta face Allah (swt) ya jefa tsoro da fargaba a cikin zukatan wannan al'ummar.

Babu wata al'umma da ZINA zata yaɗu a cikinta fa ce mace-mace sun yawaita.

Babu wata al'umma da zata TAUYE MUDU face an jarabceta da talauci.

Haka dai babu wata al'umma da za a rinƙa HUKUNCIN ZALINCI a cikinta face zubar da jini ya yawaita a cikinta.

Babu wata al'umma da zata daina KIYAYE ALƘAWARI face Allah (swt) ya ɗaura maƙiya a kanta".

(Imam Malik/al-Muwaɗɗa)

Rubutu
Sheikh Ibrahim Usman
Mabera .

11/04/2023

TALAFAWA MUSLIM DON BIYAN BUKATARSA....

manzon rahama salalahu alaiyhi wassalam : yace Muslim Dan uwan Muslim ne, don haka kada Wanda ya zalunceshi, Kara yabari a cuce shi.

wanda duk ya taimaka wajen biyan biyan bukatar Dan uwansa Allaah zai biya masa bukatarsa.

wanda k*ma ya yayewa wani Muslimi bakin ciki Allaah zai yaye Masa bakin ciki daga bakin cikin ranar tashin qiyama ,Wanda k*ma duk ya suturta Muslimi,Allaah zai suturta

ABU HURAIRA Allaah ya yarda shiya yace Annabi s a w yace Wanda duk ya yayewa wani Mumini bakin cikin daga bakin cikin duniya, Allaah zai yaye Masa bakin cikin daga bakin cikin ranar tashin qiyama

Wanda k*ma ya yalwata Wanda yake cikin kunci, Allaah zai yalwata Masa a duniya da lahira

Allaah ba zai gushe acikin taimakon bawansa ba ,matukar dai bawa Yana taimakon Dan uwansa.

Wanda ya k*ma ya K**a hanya ya tafi Neman ilimi Allaah zai saukaka Masa hanya zuwa Al-jannah k*ma duk lokacin da mutane s**a taru a wani daki daga dakunan Allaah suna karanta litafin Allaah,suna bita a kansa a tsakanisu, sai natsuwa ta sauka garesu ,rahama ta lullube su ,mala'iku su kewaye su k*ma Allaah ya ambaci su daga cikin wadanda ke tare da shi.

wanda kuwa duk iliminsa yayi lakaki dashi ,to nasabarsa zata ciyar dashiya gaba ba

05/04/2023
25/01/2023

Ibnul Qayyim (Rahimahullah) Ya ce: “Duk hadisan da suke nuni akan azumtan watan Rajab ko k*ma yin Sallah a wasu dararraki a cikinsa, hadisai ne na ƙarya da aka kagosu.

Almanaarul Muneeb: 96

LABARIN BARZAHUAl-Imam Ahmad Bin Hanbal ya ruwaito a cikin (Kitabuz Zuhud) da Tahawiy a cikin (Mushkilul Àthâr) da isnad...
26/12/2022

LABARIN BARZAHU
Al-Imam Ahmad Bin Hanbal ya ruwaito a cikin (Kitabuz Zuhud) da Tahawiy a cikin (Mushkilul Àthâr) da isnadi sahihi daga sahabi Jabir Ɗan Abdullahi ya ce: "Manzon Allah (SAW) ya ce: Wasu mutane cikin jama'ar Annabi Musa (AS) sun taɓa fita zuwa wata makabarta sai s**a ce: bari mu yi sallah sannan mu yi addu'a Allah ya fito mana da wani cikin ma'abota wannan maƙabarta ko ya labarta mana haƙiƙanin al'amarin mutuwa. Bayan sun yi sallah raka'a biyu tare da addu'a, sai ga wani mutum ya leƙo daga cikin wani ƙabari, fatar jikinsa ta rine ta yi duhu sannan k*ma ga tabon sallah a goshinsa. Sai ya ce da su: Me kuke nema a nan? Kun ganni? To yau shekara ɗari kenan da mutuwata, amma ban sami sauƙi daga magagin mutuwa ba sai ɗazu-ɗazun nan. Don Allah ku roƙar nuni Allah ya maishe Ni cikin kamannina na asali"

Dr kabir Asgar

SURATUL-FATIHA WARAKACE DAGA KOWACE CUTA.Daga Abdul Malik Ibn Umar (Rahmatullahi Alaihi) ya ce, Manzon Allah (S.A.W) ya ...
08/12/2022

SURATUL-FATIHA WARAKACE DAGA KOWACE CUTA.

Daga Abdul Malik Ibn Umar (Rahmatullahi Alaihi) ya ce, Manzon Allah (S.A.W) ya ce, 'A cikin Suratul-Fatiha Akwai waraka daga kowace cuta.' (Darami da Baihaki s**a ruwaito shi)

Sahihan littafan nan guda shida na Hadisi (wato Bukhari Muslim, Tirmizi, Abu-Dawud, Nasa'i da Ibn Majah), Sun kunshi Hadisi da s**a yi bayani cewa, Sahabban Manzon Allah (S.A.W), s**an karanta Suratul-Fatiha su hura a kan mutumin da maciji ko kunama s**a harba, harma da mai ciwon farfadiya da mai tabin -hankali. Manzon Allah (S.A.W) k*ma ya yarda da hakan.

Akwai wani Hadisi da aka ce, Manzon Allah (S.A.W) ya karanta wannan Surah, k*ma ya hura ta a kan As-sa'ib Ibn Yazid, sannan k*ma ya shafa masa yawunsa a wurin da ke masa ciwo.

Ya zo a cikin wani Hadisi cewa, idan mutum ya karanta Suratul-Fatiha da Suratul - Ikhlas ya hura a jikinsa, lokacin da zai yi barci, zai sami kariya daga kowane hadari sai dai mutuwa.
Wani Hadisi ya zo da bayanin cewa, Ladar karatun Suratul-Fatiha daidai yake da ta karatun kashi biyu cikin uku (2/3) na AlQur'ani.

An ruwaito a cikin wani Hadisi, cewa Shaidan yayi kururuwa, ya yi kuka, ya watsa wa kansa kasa, a lokuta hudu. Lokutan su ne :
1. Lokacin da aka tsine masa.
2. Lokacin da aka fitar da shi daga Aljannah
3. Lokacin da aka bayar da Annabta ga Muhammadur-Rasulullahi (S.A.W)
4. Lokacin da aka saukar da Suratul-Fatiha

Dan Allah mucigaba da tura wannan sakon zuwa wani group ko abokanmu domin mu samu ladan Amru bil ma'aruf.

Ya Allah muna tawassili da sunayenKa da k*ma AnnabinKa (Muhammad s.a.w)da k*ma wannan aiki da mukayi ka yaye mana masifar duniya da Lahira kasa k*ma sai Aljannar Firdausi itace makomarmu. Aameen.

18/11/2022

Addu'ar Tafiyar Da Kuncin Zuciya لاَ إلَهَ إِلاَّ اللَّهُ الْعَظِيمُ الْحَلِيمْ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ رَبُّ العَرْشِ العَظِيمِ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهْ رَبُّ السَّمَوَّاتِ ورّبُّ الأَرْضِ ورَبُّ العَرْشِ الْكَرِيمُ. La ilaha illal-lahul-'azeemul-haleem, la ilaha illal-lahu rabbul-'arshil-'azeem, la ilaha illal-lahu rabbus-samawati warabbul-ardi warabbul-'arshil-kareem. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, mai girma (wanda babu abin da yake girmama a gare shi), mai hakuri (mai jinkirin azaba tare da ickakken ikon aiwatar da ita). Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Al'arshi, mai girma. Babu abin bautgawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin sammai Ubangijin kasa, Ubangijin Al'arshi, mai yawan baiwa. اَللَّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُوفَلا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِي طَرْفَةَ عَيْن، وَأَصْلِحْ لِي شَأْنِي كُلَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ أنْتَ. Allahumma rahmataka arjoo fala takilnee ila nafsee tarfata 'ayn, wa-aslih lee sha'nee kullah, la ilaha illa ant. Ya Allah! Rahamarka nake kauna, don haka kar ka kyale ni da kaina ko da kiftawar ido ne, k*ma ka kyautata mini sha'ainina dukkansa; babu abin bautawa da gaskiya sai kai. لاَ إِلَهَ إِلاَّ أنْتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظَّالِمِينَ. La ilaha illa anta subhanaka innee kuntu minaz-zalimeen. Babu abin bautawa da gaskiya sai kai. Tsarki ya tabbata gare ka, lallai ni na kasance daga cikin azzalumai. اَللهُ اللهُ رَبِّ لاَ أُشْرِكُ بِهِ شَيْئاً. Allahu Allahu rabbi la oshriku bihi shaya. Allah! Allah ne ubangijina, ba na yin tarayya da shi da wani abu a cikin bauta.

Annabi S a w yace: "Na rantse da Wanda raina Yake hannunsa,lallai ne kuyi umarni da kyakyawan aiki, Kuma lallai ku Yi ha...
15/11/2022

Annabi S a w yace: "Na rantse da Wanda raina Yake hannunsa,lallai ne kuyi umarni da kyakyawan aiki, Kuma lallai ku Yi hani ga mummunan aiki, ko Allah ya Aiko muku ukuba Daga gareshi, Sannan k*m ku roke shi ya ki amsa muku".
Tirmizi ne ya rawaito shi

وَعَنْ أَبِي سَعِيدٍ الْخُدْرِيِّ - رضي الله عنه - قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ - صلى الله عليه وسلم: «مَا مِنْ عَبْدٍ ي...
10/11/2022

وَعَنْ أَبِي سَعِيدٍ الْخُدْرِيِّ - رضي الله عنه - قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ - صلى الله عليه وسلم: «مَا مِنْ عَبْدٍ يَصُومُ يَوْمًا فِي سَبِيلِ اللَّهِ إِلَّا بَاعَدَ اللَّهُ بِذَلِكَ الْيَوْمِ عَنْ وَجْهِهِ (1) النَّارَ سَبْعِينَ
خَرِيفًا». مُتَّفَقٌ عَلَيْهِ, وَاللَّفْظُ لِمُسْلِمٍ.

08/11/2022

FALALAR YIN ZIKIRI BAYAN SALLAR SUBHI

Sunnah ce mustahabbiya mutum ya zauna awajen da ya sallaci sallarsa ta asubahi ya ambaci Allah har zuwa hudowar rana.

Imamun Nawawiy (rah) ya fada acikin littafinsa "Al Azkar" cewa :."Kai sani cewar hakika mafifici acikin lokutan zikiri acikin wuni, shine yin zikiri bayan sallar asubah.

Hadisi daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace Manzon Allah ﷺ yace : ""Wanda ya sallaci sallar safe acikin Jam'i sannan ya zauna yana ambaton Allah (wato zikiri) har sai da rana ta fito sannan ya sallaci raka'o'i biyu, to ladansa kamar ladan aikin Hajji ne da Umrah" ya Qara da cewa "Cikakkiya, cikakkiya, cikakkiya".

Imamut Tirmidhiy ne ya ruwaitoshi. Kuma yace isnadinsa mai kyau ne.

Ma'anar hadisin wato shine wanda ya sallaci sallar asubahi acikin jam'i sannan ya zauna adaidai wajen da yayi sallar, yana zikirin Allah har sai da gari ya waye sosai rana ta fito har zuwa lokacin walaha, sannan ya sallaci walaha (Salatudh Dhuha) to ladansa awajen Allah kamar wanda yayi hajji da Umrah ne na nafilah.

Shi kansa (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya kasance duk sanda ya idar da sallar asubah yakan zauna awajen yana zikirin Allah har zuwa lokacin da rana zata fito.

Kuma acikin wani hadisin ma Manzon Allah ﷺ yace "Wallahi in zauna tare da mutanen dake ambaton Allah bayan sallar asubah, ahinyafi soyuwa gareni fiye da duniya da abin cikinta"

Shi yasa Malamai suke kwadaitarwa akan muhimmancin ribatar wannan lokacin tare da ambaton Allah har zuwa fitowar rana domin riskar wannan falalar. Domin hakika yazo acikin wani hadisi Annabi ﷺ yana cewa : "Ya Allah ka sanya wa al'ummata albarka alokacin sammakonta".

Kuma saboda wannan ne Malamai s**a karhanta komawa barci bayan sallar asubah domin hakika lokaci ne da ake rabon arziki don haka bai dace mutum yayi barci acikinta ba. An fi son mutum ya shafe lokacin cikin ambaton Allah da k*ma addu'a..

17/10/2022

HADISIN YAU NA (154)

(FALALAR YAWAN ISTIGFARI)

MANZON ALLAH SAW YACE: BAN TAƁA WAYEWAR GARI BA, FACE SAI NA YI ISTIGFARI ƊARI (100)

FA'IDA
WANNAN HADISI YANA KOYA MANA MAHIMMANCIN YAWAN ISTIGFARI A KOWANNE LOKACI,
MUSAMMAN SAFE DA YAMMA, A ƘALLA ƘAFA ƊARI.
ALLAH MUNA NEMAN GAFARARKA MUN TUBA ZUWA GARE KA,
استغفر الله العظيم واتوب اليه

14/10/2022

FA'IDA DAGA AL-ƘUR'ANI (2)

Allah s.w.a Yace:
{وَنُنَزِّلُ مِنَ الْقُرْآنِ مَا هُوَ شِفَاءٌ وَرَحْمَةٌ لِّلْمُؤْمِنِينَ} سورة الإسراء، آية ٨٢.
{Kuma Munã sassaukarwa daga Alƙur'ãni, abin da yake waraka ne da rahama ga mũminai}. Suratul-isra'i, aya ta 82.

Ya k*ma sake cewa:
{قُلْ هُوَ لِلَّذِينَ آمَنُوا هُدًى وَشِفَاء} سورة فصلت، آية ٤٤.
{Ka ce: "Shi, shiriya ne da waraka ga waɗanda s**a yi ĩmãni}. Suratu fussilat, aya ta 44.

Allah Yace a cikin Al-ƙur'ani akwai waraka, bal ma Yace shi ɗin waraka ne, wanda a cikin hakan akwai gagarumar fa'ida!!
Da Allah Ya so sai Yace
"فيه دواء"
Wato akwai magani madadin
" فيه شفاء".

Amma Yace waraka ne domin shi magani za a iya dacewa yayi silar waraka ko k*ma akasin hakan, dan haka Yace AL-QUR'ANI WARAKA ne ga kowacce irin cuta kai tsaye domin mutane su tabbatar da aikin na shi matuƙar anyi amfani da shi ta tsarkakakkiyar hanya k*ma yadda ya dace!

Cikakkken yaƙini da tawakkali ga Allah, da bin hanya mai tsafta shine zai ba ka damar samun warakar dake cikin AL-ƘUR'ANI MAI GIRMA.

Ku nemi waraka daga Al-ƙur'ani kuna masu yaƙinin cewa Allah zai sauƙaƙa wannan damuwa ko lalurar da ake ciki, domin dai Allah ba Ya tozarta bayinSA masu biyayya da neman falala daga gareSHI.
Allah Ka bamu dacewa da aikata daidai amin.

- Zainab Ja'afar Mahmud.
27th March 2017

14/10/2022
14/10/2022

" Mafi alkhairi acikin mutane sune wadanda s**a San Sharrin harshe , Kuma s**a kiyayeshi da ambaton laifuffukan mutane "

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abu Ubaida Been Jarah. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Shortcuts

  • Address
  • Alerts
  • Videos
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share