Hasamid Spotlight

Hasamid Spotlight Burin mu shi ne zama kafar yada labarai wacce zata kasance mai kima da nagarta.
(3)

HGTV ingantacciyar majiya ce dake yada shirye-shirye da s**a hada da labarai da dumi-dumin su, siyasa, shirin mata, wasanni, nishadi, tsaro, kiwon lafiya da dai sauran su.

30/12/2025

SPONSORED...
CBN ya gargaɗi ’yan Najeriya kan guje wa wulaƙanta naira a lokacin shagulgulan karshen shekara.

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi gargaɗi ga ’yan ƙasa da su guji duk wani aiki da zai haifar da wulaƙanta takardar kuɗin Naira, musamman a wannan lokaci na shagulgulan ƙarshen shekara.

CBN ya bayyana hakan ne yayin da ake shirin bukukuwa daban-daban da s**a haɗa da aure, suna, bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara, inda wasu ke amfani da kuɗin Naira ta hanyoyin da s**a saɓa wa doka, k**ar jefawa, taka wa, yaga wa ko yayyafa kuɗi a fili.

Bankin ya jaddada cewa Naira alama ce ta martabar ƙasa, kuma duk wanda ya wulaƙanta ta yana keta dokokin kuɗi na Nijeriya.

CBN ya tunatar da jama’a cewa dokar ƙasa ta haramta duk wani abu da zai lalata ko rage mutuncin takardar kuɗi.

Haka kuma, CBN ya yi kira ga shugabannin al’umma, malamai, masu shirya bukukuwa da kafafen yaɗa labarai da su taimaka wajen wayar da kan jama’a kan illolin wulaƙanta Naira, tare da ƙarfafa amfani da hanyoyin biyan kuɗi na zamani k**ar canja wuri ta banki (transfer) da POS.

Bankin ya ƙara da cewa hukumomin tsaro za su ɗauki mataki kan duk wanda aka samu da laifin wulaƙanta Naira, ba tare da la’akari da matsayinsa ba.

A ƙarshe, CBN ya buƙaci ’yan Nijeriya da su nuna kishin ƙasa ta hanyar kare mutuncin Naira, musamman a wannan lokaci na shagulgula, domin Naira mallakin kowa ce kuma alhakin kowa ne ya kare ta.

Wani abin fashewa ya tashi a babban asibitin  Bagudu dake Kebbi.Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi ta tabbatar da cewa wan...
30/12/2025

Wani abin fashewa ya tashi a babban asibitin Bagudu dake Kebbi.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi ta tabbatar da cewa wani abin fashewa ya tashi a Babban Asibitin Bagudu da ke Jihar.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya auku ne a safiyar ranar Talata a cikin asibitin.

Sai dai ba a samu asarar rai ko ɗaya ba.

29/12/2025

Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu ya aika da saƙon sa na jaje ga fitaccen ɗan damben duniya, Anthony Joshua, wanda ya yi hatsari a Najeriya, inda mutum biyu abokan rakiyar sa s**a mutu.

A wata sanarwa da Shugaba Tinubu ya wallafa a shafukan sa na sada zumunta, ya bayyana alhinin sa kan lamarin, sannan ya masa fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

29/12/2025

Babbar cibiyar wutar lantarki ta Ƙasa wato National grid ta lalace.

29/12/2025

Kwamishinoni da Shugabannin Ƙananan Hukumomi sun goyi bayan sauya sheƙar Abba zuwa APC.

’Yan majalisa za su gana da Gwamna Abba domin bayyana goyon bayan su ga sauya sheƙar sa daga NNPP zuwa APC.

Tsohon Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Rt. Hon. Kabiru Alhassan Rurum ne ya tabbatar wa manema labaru cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf tare da shugabannin ƙananan hukumomi da kwamishinoni za su shiga APC nan ba da jimawa ba.

29/12/2025

Jam'iyyar NNPP ta roki Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf kar ya bar Jam'iyyar ya koma Jam'iyyar APC.

Shugaban Jam'iyyar NNPP na Jihar Kano, Suleiman Hashim Dungurawa ne ya roƙi gwamnan da ya mayar da wuƙar sa kube.

Dungurawa ya ce Gwamnan Jihar Kano da duk waɗanda za su bi shi zuwa Jam'iyyar APC za su yi hakan ne domin raɗin kan su kuma sun yi iya yin su wajen ganin ba su ɗauki matakin ba.

28/12/2025

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya bar Jihar Legas domin ci gaba da hutun ƙarshen shekara a Turai inda daga bisani zai wuce Haɗaɗɗiyar daular larabawa.

An gayyaci Shugaba Tinubu ne don ya halarci taron Abu Dhabi Sustainability Week 2026, wanda ake shirin gudanar wa a farkon watan Janairu.

Gwamnatin Jihar Katsina ta ce za ta kafa dokoki ga masu sana’ar gwangwan a Jihar.Kwamishinan ciniki da masana’antu da ya...
28/12/2025

Gwamnatin Jihar Katsina ta ce za ta kafa dokoki ga masu sana’ar gwangwan a Jihar.

Kwamishinan ciniki da masana’antu da yawon shaƙatawa na Jihar Katsina, Alhaji Yusuf Rabi’u Jirdede ne ya sanar da hakan yayin taron shugabanin Ƙungiyar masu sana’ar gwangwan na ƙananan hukumomi 34 dake faɗin Jihar.

Kwamishinan ya gabatar masu da kundin dokokin ta hannun lauyan ma’aikatar shari’a, Aliyu Isa domin tsaftace masu sana’ar tare da tantance ya’yan Ƙungiyar da irin kallon da wasu jama’a ke yiwa sana’r tasu.

Alhaji Yusuf Rabi’u Jirdede ya ƙara da cewa za a buɗe ofis a kowace ƙaramar hukuma domin kula da yadda ake tafiyar da wannan sana’ar ta gwangwan.

Shugaban Ƙungiyar na Jihar, Alhaji Mustapha Sulaiman Rimi ya bayyana jin daɗin sa dangane da yadda maigirma Gwamnan Jihar ya tina dasu ya kuma kawo masu gyare-gyare a cikin sana’ar tasu, inda ya tabbatar da goyon bayan su ga wannan ƙudirin doka.

Wani ma’aikaci da ke aiki a gidan Gwamnatin Jihar Gombe, mai suna Shuaibu Adamu ya kashe abokin aikin sa, Malam Umar.Mar...
28/12/2025

Wani ma’aikaci da ke aiki a gidan Gwamnatin Jihar Gombe, mai suna Shuaibu Adamu ya kashe abokin aikin sa, Malam Umar.

Marigayin, wanda aka fi sani da Baba Usama yana aiki a gidan Gwamnatin a matsayin mai kula da rijiyar burtsatsi.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Gombe, DSP Buhari Abdullahi ya ce an tarar da Malam Umar kwance babu rai a harabar gidan Gwamnatin.

Ya ce an ɗaure wuyan sa da mazagin wandon sa sannan aka saka wani abu aka rufe bakin sa.

DSP Abdullahi ya kara da cewar 'yan sanda sun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3:50 na yammacin ranar Juma’a.

An garzaya da marigayin zuwa asibitin Ƙwararru na Gombe, inda likita ya tabbatar da mutuwar sa.

Daga nan aka ajiye gawar sa a ɗakin ajiyar gawarwaki na asibitin domin yin bincike.

Bayan faruwar lamarin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, CP Umar Ahmed Chuso ya kai ziyara wajen da abin ya faru tare da bayar da umarnin gudanar da bincike.

Binciken ’yan sanda, ciki har da duba na’urar CCTV a harabar gidan Gwamnatin, ya nuna wani matashi mai shekara 19, Shuaibu Adamu wanda aka fi sani da Yaya Mama, an gan shi yana dukan marigayin kafin rasuwar sa.

**ai

27/12/2025

Takaitattun labaru na HG TV, wanda ya kunshi labaran gida dana ƙetare da na wasanni.

27/12/2025

Jami'an sashen tattara bayanan sirri na Rundunar ƴan sandan Najeriya sun ce sun k**a wasu riƙakkun ƴan bindiga biyu waɗanda ake zargi da kai munanan hare-hare a Jihohin Katsina, Zamfara, Neja da kuma Kwara.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Rundunar, Benjamin Hundeyin ya fitar, ya ce an k**a waɗanda ake zargin ne bayan wani samame mai girma da s**a kai a Jihar Kwara.

A cewar sanarwar, an ga ɗaya daga cikin ƴan bindigar mai suna Abubakar Usman wanda aka fi sani da Siddi yana wasa da maƙudan kuɗaɗe da kuma riƙe da mak**ai a wani bidiyo.

Ɗayan kuma an bayyana sunan sa da Shehu Muhammadu wanda aka kuma sani da Gide.

Hundeyin ya ce jami'an sun ƙwato wata sabuwar mota ƙirar Hinda Ace da babura 125 da bindigar AK-47 cike da tarin harsasai da kuma zunzurutun kuɗi da ya kai naira 500,000.

**ai

26/12/2025

Gwamnatin Sokoto ta ce tana maraba da duk haɗin gwiwa da zai kawo ƙarshen matsalar tsaro.

Gwamnatin ta ce an yi haɗin gwiwa ne tsakanin sojojin Amurka da na Najeriya wajen ƙaddamar da harin, wanda ta ce ba a rasa rai ba.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Abubakar Bawa ya fitar, ya ce ba za a iya tantance haƙiƙanin sak**akon harin ba a cikin ƙanƙanin lokaci, saboda har yanzu suna jiran cikakken rahoton aikin na musamman.

Sai dai sanarwar ta bayyana cewa babu fararen hula da harin na garin Jabo ya kashe ko ya jikkata.

Sanarwar ta ƙara da cewa a shekaru biyu da s**a gabata, Gwamnatin Jihar ta yi ƙoƙarin ta wajen magance matsalar ta hanyar ba jami'an tsaro duk goyon bayan da suke buƙata domin su gudanar da aikin su da kyau.

A ƙarshe Gwamnatin Jihar ta yi kira ga mazauna yankunan da abin ya shafa da su ci gaba da ba Gwamnatin tarayya da ta Jiha hadin kai ta hanyar fitar da bayanan sirri ga jami'an tsaro domin hakan ne zai taimaka wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

Sannan a ci gaba da addu'ar neman agajin Allah wajen magance matsalar.

Adres

Kado
Amsterdam
900108

Meldingen

Wees de eerste die het weet en laat ons u een e-mail sturen wanneer Hasamid Spotlight nieuws en promoties plaatst. Uw e-mailadres wordt niet voor andere doeleinden gebruikt en u kunt zich op elk gewenst moment afmelden.

Contact

Stuur een bericht naar Hasamid Spotlight:

Uitgelicht

Delen