Hasamid Spotlight

Hasamid Spotlight Burin mu shi ne zama kafar yada labarai wacce zata kasance mai kima da nagarta.
(3)

HGTV ingantacciyar majiya ce dake yada shirye-shirye da s**a hada da labarai da dumi-dumin su, siyasa, shirin mata, wasanni, nishadi, tsaro, kiwon lafiya da dai sauran su.

22/12/2025

An miƙa ɗalibai ɗari da talatin da aka ceto daga hannun masu garkuwa da su zuwa hannun hukumomi a Jihar Neja.

Gwamnan Jihar da wasu manyan jam'ian Gwamnati ne s**a tarbe su a fadar Gwamnati da ke babban birnin Jihar bayan da s**a iso a motoci shida tare da rakiyar jami'an tsaro.

Hukumomi a Kasar sun ce an ceto yaran ne yayin wani aiki na musamman da jami'an tsaro s**a yi duk da ba su bayar da karin bayani ba.

Hukumomi sun ce ɗaliban da malamai bakwai da aka ceto su kadai ne s**a rage a hannun ƴan bindigar cikin waɗanda aka sace daga makarantar kwana ta Katolika ta St. Mary da ke Papiri a watan Nuwamba.

22/12/2025

Amurka ta rattaɓa hannu kan wata yarjejeniya ta haɗin gwiwa a fannin inganta kiwon lafiya mai ɗore wa na tsawon shekaru biyar da Najeriya, wadda ta kai kimanin dala biliyan 5.1 don inganta tsarin lafiya karkashin tsarin Amurka na samar da lafiya ga al'ummar duniya ta America First Global Health Strategy.

A karkashin wannan yarjejeniyar, Amurka za ta bayar da tallafi na dala biliyan 2.1, yayin da Najeriya za ta zuba dala biliyan 3.0 a kiwon lafiya a cikin shekaru biyar.

Daga cikin tallafin, za a ware kimanin dala miliyan 200 domin tallafa wa sama da cibiyoyin lafiya na addinin Kirista guda 900 don fadada damar samun kulawa ga cututtuka k**ar HIV da TB da zazzabin cizon sauro da kuma kula da uwa da jariri.

Wannan shi ne mafi girman haɗin gwiwa da kowace ƙasa ta yi tun bayan kaddamar da tsarin.

22/12/2025

’Yan bindiga sun sace mutane 28 a garin Zak da ke Ƙaramar Hukumar Wase a Jihar Filato a kan hanyar su ta zuwa taron Mauludi.

Rahotanni na nuni da cewa a cikin waɗanda aka sace akwai malamin addini da kuma ’ya’yan sarki 2.

22/12/2025

Kocin tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya, Eric Chelle ya ce a halin yanzu ƴan wasan sa sun mayar da hankali ne kan wasan su na farko a gasar cin kofin nahiyar Afrika wato AFCON inda za su fafata da tawagar ƙasar Tanzania ranar Talata.

Da ya ke jawabi a taron maneman labarai da aka yi a filin wasan birnin Fez Chelle ya bayyana cewa tawagar sa ta yi baƙin cikin rasa gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026 amma hakan ba zai sa ta yi ƙasa a gwiwa ba wajan neman yin nasara a gasar AFCON.

22/12/2025

A cikin SHIRIN mu na AL'ADUN GARGAJIYA, min kawo muku bayanai akan TSAGEN FUSKA da yanda ya samo asali.

An sako sauran ɗaliban makarantar St. Mary's ta Papiri da aka yi garkuwa da su.An sako sauran ɗaliban ne dai da malaman ...
21/12/2025

An sako sauran ɗaliban makarantar St. Mary's ta Papiri da aka yi garkuwa da su.

An sako sauran ɗaliban ne dai da malaman da aka sace daga makarantar Katolika ta St. Mary’s da ke Papiri a karamar hukumar Rafi ta Jihar Neja, k**ar yadda mazauna yankin da kuma majiyoyin tsaro s**a tabbatar.

21/12/2025

Sakon babban Ministan Tsaro, Christopher Musa ga yan Najeriya musamman yan Arewa akan tsaro.

Ababen hawa sun yi ƙaranci a tashar mota ta Jabi da ke babbar birnin tarayya Abuja sak**akon tafiye-tafiyen hutun ƙarshe...
21/12/2025

Ababen hawa sun yi ƙaranci a tashar mota ta Jabi da ke babbar birnin tarayya Abuja sak**akon tafiye-tafiyen hutun ƙarshen shekara.

Hukumar dake kula da ingancin abinci da magunguna ta Ƙasa-NAFDAC ta ayyana taliyar Indomie mai dandanon ganyayyaki wato ...
21/12/2025

Hukumar dake kula da ingancin abinci da magunguna ta Ƙasa-NAFDAC ta ayyana taliyar Indomie mai dandanon ganyayyaki wato Vegetable Flavour a matsayin abinci mai hadari ga lafiyar mutane inda ta bada umarnin a bi kasuwanni a kwashe su kaff don kiyaye lafiyar jama'a.

A cikin wata sanarwa mai Lamba 041/2025 da ta wallafa, NAFDAC ta ce hukumar kare lafiyar masu saye ta Faransa, Rappel Conso ta bayar da umarnin janye Indomie mai ɗanɗanon kayan lambu bayan gwaje-gwaje sun tabbatar da kasancewar sinadaran da ba a bayyana ba, musamman madara da ƙwai, a cikin samfurin.

Waɗannan sinadaran ba a ambace su a jikin lakabin samfurin ba, lamarin da ke haifar da barazana ga lafiyar mutanen da ke da samun matsala da wasu abinci wato allergy ko matsalar jure wasu sinadarai, inda hakan ka iya jawo mummunan lahani ga lafiyar su.

Janyewar ta shafi dukkan rukunan samfurin da ke da ranar ƙarewa ta 6 ga Fabrairu, 2026 duk da cewa sanarwar ba ta fayyace ƙasar da aka yi samfurin ba.

NAFDAC ta bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne a matsayin kariyar lafiyar jama’a, domin rage haɗarin da samfurin ke haifar wa ga masu fama da matsalar rashin jituwa da wasu abinci.

Hukumar ta ƙara da cewa ko da yake yiwuwar shigowar wannan samfurin cikin Najeriya tana da tsauri, sak**akon haramcin shigo da taliya wato noodles da Gwamnatin tarayya ta yi amma ba za a iya kawar da yiwuwar shigowar sa ta hanyoyi haramtattu ba, k**ar saye ta yanar gizo ko shigowar mutum daga ƙasashen waje.

Domin hana yaduwar Indomie mai ɗanɗanon kayan lambu a cikin ƙasar, NAFDAC ta umurci dukkan daraktocin shiya-shiya da masu kula da Jihohi da su ƙara sa ido tare da gaggauta kwace wa da kwashe duk wani samfurin da aka samu a kasuwanni da rumbunan ajiya ko wajan masu rarrabawa.

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana cewa yanayin kasuwanci da tsarin doka a Najeriya ba...
21/12/2025

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana cewa yanayin kasuwanci da tsarin doka a Najeriya ba su dace da yadda wani mai zuba jari zai nuna sha’awar sayen matatun man fetur da Kamfanin NNPC ke da su ko da Gwamnati ta sa su a kasuwa.

Dangote ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya yi a Legas ranar Lahadi, inda ya ce ko a yau NNPC ta yanke shawarar sayar da matatun man fetur babu wanda zai zo ya saya, saboda yanayin aiki da tsare-tsaren da ke gudana a ɓangaren man fetur ba su ƙarfafa jarin masu zuba jari.

Ya ce matsalolin da ke tattare da dokoki da tsari da yanayin kasuwanci sun sanya zuba jari a harkar tace mai ya zama abin mai wahala, ba wai ga ‘yan ƙasashen waje kaɗai ba har ma da ‘yan cikin gida.

Darajar naira ta rufe mako cikin ƙarfi a ranar Juma’a, bayan ta samu ƙarin naira 1.65 kan dalar Amurka a kasuwar canji t...
21/12/2025

Darajar naira ta rufe mako cikin ƙarfi a ranar Juma’a, bayan ta samu ƙarin naira 1.65 kan dalar Amurka a kasuwar canji ta hukuma, inda aka sayar da ita kan naira 1,454.41.

Bayanan da babban bankin Najeriya ya fitar ta shafin sa na hukuma sun nuna cewa wannan sauyin ya wakilci ƙarin kashi 0.11 cikin 100 idan aka kwatanta da ranar Alhamis, lokacin da naira ta tsaya a kan naira 1,456.06 kan kowace dala.

A farkon makon cinikayyar, naira ta fuskanci ɗan raguwar daraja a tsawon makon.

A ranar Laraba, an sayar da kuɗin a kan naira 1,455.38, abin da ya nuna cewa kasuwar na cikin yanayin da ba a samu manyan sauye-sauye ba.

Rundunar ’yan sandan Jihar Imo ta tabbatar da cafke wani mutum mai shekaru 58, Vitalis Nwoko ɗan asalin Umuagba da ke ƙa...
21/12/2025

Rundunar ’yan sandan Jihar Imo ta tabbatar da cafke wani mutum mai shekaru 58, Vitalis Nwoko ɗan asalin Umuagba da ke ƙaramar hukumar Ahiazu Mbaise bisa zargin dukan matar sa Uloma Vitalis, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar ta.

Mai magana da yawun Rundunar, DSP Henry Okoye ya bayyana cewa jami’an ’yan sanda daga sashen Ahiazu Mbaise ne s**a k**a wanda ake zargin, bayan ’yar uwar mamaciyar ta kai rahoton lamarin ofishin ’yan sanda.

A cewar rahoton, ana zargin Vitalis da yi wa matar sa duka yayin wata saɓani na cikin gida.

Okoye ya ce binciken farko ya nuna cewa rikicin da ya faru a ranar 11 ga watan Disamba ya rikiɗe zuwa fada, inda matar ta faɗi ta suma.

Daga bisani aka garzaya da ita asibiti, inda likita ya tabbatar da rasuwar ta.

Rundunar ta ƙara da cewa, an miƙa wanda ake zargin zuwa sashen binciken manyan laifuka na Jiha-SCID da ke Owerri domin zurfafa bincike da kuma ɗaukar matakin shari’a da ya dace.

Adres

Kado
Amsterdam
900108

Meldingen

Wees de eerste die het weet en laat ons u een e-mail sturen wanneer Hasamid Spotlight nieuws en promoties plaatst. Uw e-mailadres wordt niet voor andere doeleinden gebruikt en u kunt zich op elk gewenst moment afmelden.

Contact

Stuur een bericht naar Hasamid Spotlight:

Uitgelicht

Delen