03/07/2023
MUHIMMIYAR SANARWAR GARGAƊI ZUWA GA MASU ANFANI DA SUNAN KATSINA POST A DANDALIN FACEBOOK
Muna yi ma ɗaukacin al'umma musamman masu bibiyar KATSINA POST gaisuwa irin ta addinin Musulunci.
Bayan haka, mu a KATSINA POST, muna matuƙar nuna rashin jin daɗin mu kan yadda ake cigaba da samun wasu marassa ƙima da mutunci da ke cigaba da anfani da suna da alamar kamfanin mu suna gudanar da ayyukan su na rashin kyautawa a wannan kafar ta FACEBOOK.
Misali, akwai wani mai suna Anas Suleiman (https://www.facebook.com/anas.sulaiman.9615566) da ya buɗe wani dandali (Group) mai suna Katsina Post Group 2 (https://www.facebook.com/groups/1064637617835697/?ref=share&mibextid=NSMWBT) kuma suke anfani da sunan mu da alamar kamfanin mu (logo) suna gudanar da shi ta hanyar da ba ta dace ba wadda ba mu da alaka ta kusa ko ta nesa da shi.
Haka zalika akwai wani mutum da muke kyautata zaton ɗan ƙaramar hukumar Kankia ne ta jihar Katsina da ya buɗe turaka (account) da sunan Katsina Post (https://www.facebook.com/profile.php?id=100086452748284&mibextid=ZbWKwL) yana yin rubuce rubucen da ba su dace da aikin jarida ba.
A dukkan wannan, ayyukan mutanen da muka lissafa a sama su na sa kamfanin mu a cikin tsaka-mai-wuya ta yadda wasu ke tunanin mu ne ke yin su.
Da wannan ne muke kira gare su da su gaggauta rufe dandalin da kuma shafin na su domin kaucewa jefa kan su cikin matsala da kuma fushin hukuma.
Domin kaucewa duk wani shakku, shafin KATSINA POST na Facebook guda ɗaya (1) ne (https://www.facebook.com/katsinapost?mibextid=ZbWKwL) kuma muna da dandali mai suna Katsina Post Group (https://m.facebook.com/groups/1972924576330045/?ref=share&mibextid=NSMWBT).
Baya ga waɗannan, duk wani shafi ko dandalin da kuka gani, to ba namu bane kuma ba mu da alaƙa ta kusa ko ta nesa da su.
Mun gode kwarai da gaske.
Mustapha Saddiq,
Shugaban kamfanin jaridar KATSINA POST.
08067205524.