09/03/2024
Kotun kolin ƙasar Saudiyya ta buƙaci al'ummar musulmi su halarci duban jinjirin watan Ramadan a yammacin Lahadi..
RIYADH — Kotun ƙolin ƙasar Saudiyya ta fitar da kira ga al’ummar musulmi a faɗin ƙasar da su halarci duban jinjirin watan Ramadan a yammacin ranar Lahadi 29 ga watan Sha’aban shekara ta 1445 bayan hijira, kamar yadda kalandar Umm al-Qura ta nuna a ranar 10 ga Maris, 2024.
A ƙoƙarin da kotun ƙolin ƙasar ke yi na tabbatar da ganin jinjirin watan azumin Ramadan daidai, ta ƙarfafa gwiwar waɗanda s**a samu damar ganin jinjirin watan, ko da ido ko kuma ta hanyar amfani da na’urar ɗaukar hoto da su fito su bayyana abubuwan da s**a gani. An yi kira ga mutanen da s**a ga jinjirin watan da su kai rahoto ga kotu mafi kusa, inda za su iya rubuta shaidarsu a hukumance. A madadin kotun, za su iya tuntuɓar cibiyar mafi kusa, wanda zai taimaka musu wajen isa kotu mafi kusa don rubuta abubuwan da s**a gani.
Wannan al’ada ta ganin wata al’ada ce kuma ta addinin Musulunci, domin ita ce ke tabbatar da ganin watan Ramadan, watan da aka keɓe domin ibada, da azumi daga alfijir har zuwa faɗuwar rana, da kuma ayyukan sadaƙa.