World news
- Home
- World news
Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from World news, Media/News Company, .
01/12/2022
TSAKANIN SHUGABA BUHARI DA GWAMNONI WAYE MAI GASKIYA?
Maigirma Shugaban Kasar 'yan Nigeria masu sharholiya Muhammad Buhari ya zargi Gwamnonin Nigeria da jefa talakawan Nigeria cikin mawuyacin hali
Shugaba Buhari yace Gwamnonin suna sace kason dukiyar kananan hukumomin Nigeria inda mafi akasarin talakawa suke, hakan ya jefa rayukansu cikin mawuyacin hali, inji Baba Buhari
To sai mu duba mu gani👇👇
Ina tuna wani lokaci da Maigirma Shugaban Kasa ya gabatar da kuduri ga Majalisar dokoki na kasa akan abu guda biyu zuwa uku:-
Na farko: Tsame hannun Gwamnoni daga shiga lamarin Kotunan jiha
Na biyu: Samarwa Kananan hukumomi asusun banki daga tarayya, ta yadda daga Federal za'a ke tura musu kudin bajet
Na uku: Haramtawa Gwamnoni iko akan Shugabannin kananan hukumomi
Amma bana tunanin cikin wannan kuduri da Buhari ya kai gaban majalisa yayi tsayuwar daka wajen ganin sun tabbata, maciya amana sun sa shi ya shashantar da abin, wanda da ace yayi hakan shikenan ya samawa Kananan hukumomi 'yanci, talakawa zasu amfana, don haka anan zamuce laifin maciya amana ne ko laifin Baba Buhari
Abinda ya sake jefa rayukan talakawan Nigeria da suke rayuwa a kananan hukumomi cikin mawuyacin hali musamman a yankin Arewa maso yamma shine rashin tsaro, da fitinar garkuwa da mutane, an gaza wajen samar da tsaro, talaka baya iya noma sai ya biya 'yan ta'adda kudin haraji, wasu kauyukan noman ya gagara, tsakani da Allah Gwamnatin tarayya ita ke da alhakkin samar da tsaro da kawar da ta'addanci ba Gwamnoni ba, kowa ya san mai laifi anan
Daga cikin abinda ya jefa rayukan talakawan Arewa cikin tsananin yunwa da bakin talauci shine rufe boda da haramta shigo da abinci musamman Shinkafa daga Kasar waje, alhali an tsananta wa talaka kudin taki da maganin kashe ciyawa, noman ya gagara, wannan laifin Gwamnatin tarayya ne ba na jihohi ba
Don haka duk tsarin Gwamnatin APC na a cutar da talakawan Arewa ne ba komai ba, sun jefa rayukan talakawa cikin tsananin yunwa da talauci da fatara, tsoro da fargaba
24/11/2022
BAUCHI DA GOMBE DAYA NE
'Yan uwa Gombawa diban fari ku ajiye wukar, ku sanya wa zukatanku ruwan sanyi akan batun rijiyar man fetur dake Kolmani
Kolmani yana kan iyaka da karamar hukumar Alkaleri a jihar Bauchi da kuma Akko a jihar Gombe, wato zamu ce wannan albarka yana tsakanin Bauchi da Gombe ne, shine maganata ta gaskiya
Tabbas da jihar Bauchi da jihar Gombe mallakin Gwamnatin tarayya ne, kuma Gwamnatin tarayya ita ke da iko akan rijiyar man,, don haka jihar Bauchi da Gombe zasu shiga cikin jihohin Nigeria da s**a mallaki arzikin man fetur (Oil States) wanda za'a ware musu kaso na musamman k**ar yadda yake a tsarin Gwamnatin tarayya
Rijiyoyin man fetur dake Kolmani zai amfani dukkan jihohin tarayyar Nigeria ne ba Gombe da Bauchi ba
Zamu iya yin raha, idan Gombawa s**ace Kolmani mallakinsu ne daidai ne, hakanan idan mutanen Bauchi s**ace nasu ne daidai ne, domin tabbas yankin Kolmani ya shafi jihar Bauchi da Gombe
Shiyasa lokacin da Maigirma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Maigaskiya yazo kaddamar da rijiyar man Kolmani, sai da Gwamnan Bauchi da Gwamnan Gombe s**a halarta, kuma duk sunyi jawabi, sun tabbatar rijiyar ya shafi jihar Bauchi da Gombe
Ni banga abin fada da cacar baki tsakanin Gombe da Bauchi ba, mu 'yan uwan juna ne tamkar jini da hanta, sai dai muyi wasa da raha, amma duka arzikin namu ne
Ina alfahari da Bauchi k**ar yadda nake alfahari da Gombe, Bauchi da Gombe a gareni duk abu daya ne
Muna rokon Allah Ya albarkaci jihar Bauchi, Gombe da sauran jihohin Arewan Nigeria, Allah Ya sa mu amfana da rijiyar man fetur na Kolmani
24/11/2022
Daya daga cikin rijiyoyin mai na farko da aka gano a arewacin Najeriya kenan a kauyen Barambu da ke karamar hukumar Alkaleri. Rijiyar mai lamba KR2 ita ce ta biyu cikin uku da aka kammala aikinsu.
24/11/2022
Me ye ra'ayinku kan kalaman Shuagaban Jam'iyyar APC na Kano Alhaji Abdullahi Abbas na "Ko da TSIYA KO DA TSIYA-TSIYA a zaɓe mai zuwa?
👉 https://bit.ly/3EzYUnZ
17/11/2022
JOSAWA
Jama'ar jihar Pilato sun fito mazansu da matansu tare da tankokin ruwa s**a wanke gurin da jam'iyyar da taci amanar talakawan Nigeria s**a gudanar da kamfen jiya a birnin Jos
Atiku kawai Insha Allah
15/11/2022
YANA TSAKA MAI WUYA
Sanarwa daga hukumar zabe na Kasa (INEC) akan zargin da wata Kotu a Kasar Amurka take yiwa Bola Tinubu na safaran miyagun kwayoyi da mallakar kudaden haram
Hukumar zabe tace yanzu haka tana tattaunawa da Kotun Northern Illinois District Court dake Amurka domin ta samu tabbaci akan zargin da take yiwa Tinubu kafin ta dauki matakin da ya dace
Sannan hukumar zabe na Kasa tace tana nazari da karanta hukuncin Kotun Amurka akan Tinubu don ganin abinda ya aikata ko yaci karo da dokokin zaben Nigeria na shekarar 2022
INEC tace duk abinda ta tabbatar zata yiwa jama'ar Nigeria bayani
Kar ku manta jama'a, kwanaki maciya amana sunyi yunkurin koran shugaban hukumar zabe na Kasa k**ar yadda s**a kori Alkalin Alkalai, amma bukatar bata biya ba, saboda sun hango wannan abin
Lallai nima a fahimtata daga cikin gida aka kunno wa Tinubu wannan wuta na batun safaran miyagun kwayoyi da mallakar kudaden haram na Dalar Amurka, domin a cikin tawagar APC akwai manyan da basa kaunar Tinubu sam
Tabbas daga yanzu zuwa nan da kowani lokaci za'a iya haramtawa Tinubu takara idan an tabbatar da tuhumar da ake masa
Allah Ka daukaka darajar Nigeria, Ka bamu shugabanni na kwarai أمين
15/11/2022
Ash-Sheikh Jingre kenan yayin da yake karbar bakuncin Dan Takarar Shugaban Kasa na Jam'iyar APC ,Tare da Shugabanin Jam'iyar .A gidan shi dake garin Jos.
Kuma wanan ziyarar tazo ne a yayin da s**a zo garin don yin taron su na Siyasa .
Muna addu'ah Sheikh Allah yaqara girma.
14/11/2022
AL-QUR'ANI RAHAMA NE
Sanadiyar yin karatu Al-Qur'ani Maigirma a gidan sarkin Katsinan Gusau, wannan yaro ya samu kyautar kudi har naira dubu dari (N100,000) daga tsohon gwamnan jihar Imo Rochas Okorocha (Dan Jikan Sokoto)
Sannan kuma Okorocha yayi alkawarin daukar nauyin karatun yaron tun daga Secondary har zuwa Jami'ah
Rochas Okorocha inyamuri ne iyayensa s**a haifeshi a Arewa ya girma, ya koma garinsu ya shiga siyasa har ya zama Gwamna
Yana daya daga cikin manyan 'yan siyasar Inyamurai da suke mutunta 'yan Arewacin Nigeria da kuma addinin mu na Musulunci
Muna fatan Allah Ya shiryar dashi addinin Musulunci
12/11/2022
KOWA YAYI DA KYAU ZAI GA DA KYAU, IDAN KA SHUKA ALKAIRI ZAKA GIRBI ALKAIRI.
Ɗan Sandan Da Yaƙi Karɓar Cin Hanci Ya Samu Ƙarin Girma Da Kyautar Naira Milyan Guda...
Hukumar kula da ayyukan ƴansanda ta ɗaga likkafar Haziƙin ɗansandan nan wato DPOn Nassarawa jihar Kano CSP Daniel Amah daga Muƙamin CSP zuwa mataimakin ƙwamishinan ƴansanda (ACP) tare da bashi kyautar kuɗi Naira Milyan Ɗaya.
ACP Daniel ya samu wannan ƙarin girma ne bisa ƙoƙarin da ya nuna na tona asirin wasu batagari na abokan aiki waɗanda s**a yi yunƙurin bashi cin hanci na miliyoyin kuɗi amma yace yaji tsoron Allah ya kuma yadda arziki da talauci da mutuwa da rayuwa duk a hannun Allah suke domin hakane yace ba zai karɓi wannan kuɗi ba, adalci kawai yake buƙata yayi.
Dalilin haka ne ma ƙwanakin baya shugaban kasa Muhammad Buhari ya karrama shi da lambar girmamawa ta Public Service Award, kazalika shima Shugaban Ƴansandan na ƙasa ya bashi Lambar Girma haɗi kuma da wadda Hukumar kula da aikin Ƴansanda ta bashi.
Ƙasa da wata biyu kenan da samun ƙarin girmansa na CSP sai gashi hukumar kula da ayyukan ƴansanda tayi masa ƙarin girma na musamman daga mukamin CSP da ya samu bada dadewa ba zuwa mataimakin ƙwamishinan ƴansanda (ACP)
Muna taya shi murna na sanya tsoron Allah a aikinsa fiye da komai.
Allah ya taya shi riƙo yasa sauran Ƴansanda suyi koyi da abinda ya aikata na gudun duniya da ƙin goyan bayan zalinci.
09/11/2022
KOTU TA BAYAR DA UMARNIN K**A SHUGABAN HUKUMAR EFCC
Kotun FCT High Court Abuja ta bada umarni wa Shugaban 'yan Sandan Nigeria IGP Usman Baba Alkali ya gaggauta k**a shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) Abdulrashid Bawa
Alkaliyar da ta jagoranci zaman Kotun Justice Chizoba Oji tace Abdulrashid Bawa yayi biris da umarnin Kotu na ranar 21-11-2018 inda Kotu ta umarni hukumar EFCC ta dawo da wata Mota kirar Range Rover da kuma kudi kimanin Naira Miliyan 40 ma wanda ya shigar da kara amma hukumar taki
Don haka Abdulrashid Bawa da yake shugabantar hukumar a yanzu shima ya bijire wa umarni Kotu tare da raina kotu, don haka Alkaliyar tace a k**ashi sannan a turashi gidan yarin Kuje dake Abuja
Nigeria kenan, watakila maciya amana sun juyo kan wannan dan uwa matashi mai kokarin kwatanta gaskiya zasu kawar da shi don suyi abinda s**a saba, amma ni kam ina kyautata masa zato sosai
Har ga Allah wannan abin bai kai Kotu ta zartar da irin wannan hukunci ba, tabbas akwai wata boyayyar manufa, tun da aka kafa EFCC ba'a yi shugabanta da ya wanye lafiya ba
Allah Ya kyauta
06/11/2022
Tsaleliyar Budurwa Ƴar kasar Indiya ta Angwance da wani Kare.
Me zeku ce
04/11/2022
AN FARA YIWA TINUBU WATSEWAR ZABI
Hajiya Sanata Aishatu Binani ta ajiye mukaminta na jagoran yiwa Tinubu yakin neman zabe a jihar Adamawa
Tace ta ajiye mukamin ne saboda tana jiran sak**akon hukuncin da kotun daukaka kara zata yanke akan takaran Gwamnan na APC da Kotu ta rushe
Sannan ta sanar da Kwamitin yakin neman zaben Tinubu su gaggaunlta nada wani ko wata a madadinta
Wannan ma babban illa ne ga takaran Tinubu, sun rasa wannan mata mai farin jini a jihar Adamawa, yanzu aka fara masa tawaye a Arewa
Atiku kawai Insha Allah
02/11/2022
SIYASAR KANÓ: An Bawa Hammata Iska Tsakanin Murtala Sule Garo Da Alhassan Ado Doguwa
Ricíkí ya barké tsakanìn Murtala Sulen Garó da shugaban masú rinjayé a majalisar wakilai ta Nìgeria Alhasan Ado Doguwa a wanì zaman jiga-jigan Jam'iyar APC a jìhar Kanó.
Jaridar Daily Nígeriá ta rawaitó cewa wanì rikici ya barke tsakanin jiga-jigan jam'iyar APC na jihar Kano, a wani zama da akayi a gidan ɗan takarar gwamnan jihar wato Nasiru Gawuna, inda Alhasan Ado Doguwa ya jefi Murtala Sulen Garo da kofin shayi a darén jiya Litinin.
- Mé za kúce ?
02/11/2022
KARYEWAR DARAJAR NAIRA
Tun bayan da maciya amanar tattalin arzikin Nigeria s**a bawa Shugaba Muhammadu Buhari shawara a canza fasalin kudin Nigeria, sai darajar kudin Nigeria ya kara karyewa a kasuwar canjin kudi na duniya
A yau Laraba ana canza kudin Ingila Pound daya (£1) akan farashin Naira 928, sannan dalar Amurka daya ($1) ya kara tashi zuwa Naira Naira 839, kuma masana sunce babu abinda zai hana cigaba da karyewar darajar Naira, ku dubi rahoton BBC na yau da safe
Na saurari hiran da akayi da wani masanin tattalin arziki a tashar RFI Hausa Dr Qasim Garba Kurfi, inda yayi bayani akan amfani da illar canjin kudin da Gwamnatin Buhari zatayi
Dr Qasim Kurfi yace: "sama da Kananan hukumomi 400 cikin 774 a fadin tarayyar Nigeria ba su da Banki ko guda, don haka ta yaya za su canza kudin su?" - Dr. Qasim Garba Kurfi
Za'a kara jefa rayukan talakawan Nigeria cikin kunci da wahala, kwana a layin banki kadai ya ishi al'umma damuwa, wannan shine abinda manyan Malamai irinsu Sheikh Dr Ahmad Gumi da Sheikh Dr Muhammad Bin Usman s**a hango s**a bayyana ake jin haushinsa har wawaye na cewa jahilai ne basu da masaniya akan tattalin arziki
Tsarin Gwamnatin nan ba na tausayin talakawa bane, akwai zalunci da rashin imani, wannan lokacin bai dace a ce za'a canza fasalin kudi ba, a tarihin Nigeria darajar kudin Kasar bai taba karyewa ba k**ar a wannan karon
Allah Ka canza mana shugabannin azzalumai maciya amana, Ka maye mana gurbinsu da masu tausayi ba don halin mu ba
02/11/2022
ATIKU KAWAI
Maigirma dan takaran shugaban Kasarmu Nigeria Alhaji Atiku Abubakar ya amsa gayyatar da gidan rediyo sashin hausa na muryan Amurka VOA Hausa dake birnin Washington DC a Kasar Amurka s**a masa
Sun yiwa Atiku tambayoyi masu yawa akan manufarsa da matsalolin Nigeria kuma ya basu amsa masu gamsarwa da k**a hankali, sannan Atiku ya fadi wasu daga cikin tsarinsa da zai bi domin ya farfado da Nigeria idan Allah Ya bashi nasara
VOA Hausa zasu saki cikakken zantawar da s**ayi dashi daga yau zuwa gobe Insha Allah
Allah Ka dawo mana da jagoran mu gida lafiya Amin
01/11/2022
YANZÚ-YANZÚ: Rahotanni daga jíhar Kanó na céwa ana ta yagé Hotuna da Billboard na Majority Leader Rt Hon. Alhassn Dan Ado Doguwa dake cikin bírnín Kanó.
A daren jiya Litinin ne daí rikici ya barke tsakanin jiga-jigan jam'iyar APC na jihar Kano, a wani zama da akayi a gidan ɗan takarar gwamnan jihar wato Nasiru Gawuna, inda Alhasan Ado Doguwa ya jefi Murtala Sulen Garo da kofin shayi.
- Mé za kúce ?
23/10/2022
LABARINA SERIES:
Ana tsegumi cewa Rigar dake cikin babbar rigar Alhaji Dangaske ita ce Kuma rigar da sarkin gida Baba Rabi'u ya saka...
ME ZAKU CE
21/10/2022
Governor Zulum Attends The Funeral Prayer Of Late Hajja Falmata Mustapharam Mafoni.
🙏🙏🙏
His Excellency the Executive Governor of Borno state Prof.Babagana Umara Zulum attended the funeral prayer of late Hajja Falmata Mustapharam, mother the mother of Sheikh Modu Mustafa special adviser to the Governor on religious affairs.
Hajja Falmata Mustapharam died at the age of eighty-five (85), and the funeral prayer took place at Imam Bukhari Mosque.
The Governor prayed for Allah to forgive the deceased and for the family the fortitude to bear the lost.
BORNO COMMUNITY WATCH (BCW)
18/10/2022
ZABEN KABILANCI
Dan takaran shugabancin Nigeria a jam'iyyar APC Bola Ahmad Tinubu ya je jihar Ekiti inda ya fadi wasu kalmomi na kabilanci wa 'yan uwansa Yarbawa
Tinubu yace dole kabilar yarbawa su bashi kuri'ah da kaso 95 cikin 100, kar su kuskura su zabi Atiku da Peter Obi
Wannan kalubale ne garemu jama'ar Arewacin Nigeria, zaben 2023 zabe na da za'a baje kolin kabilanci, kabilanci ne zaiyi matukar tasiri
Bangaren Inyamurai masu rajin kafa Kasar Biyafara zasu zabi Peter Obi, bangaren Yarbawa zasu zabi Peter Obi, ya k**ata bangaren Arewa mu zabi Atiku
Duniya ta sani jama'ar Arewacin Nigeria mu ke da kaso mafi yawa, idan zaben bangaranci ko kabilanci za'a yi k**ar yadda Tinubu yake ikrari to har a tashi duniya mulki zai tabbata a yankin Arewa
18/10/2022
MALAM YA BURGENI
Wato wani al'amari na tarihi ya faru a Kaduna jiya, kusan dukkan 'yan takaran shugabancin Nigeria a jam'iyyar APC, PDP da LP sun ziyarci Kaduna
Maigirma Gwamnan Kaduna Malam Nasir El-Rufai yana tare da dan takaran shugaban Kasa a jam'iyyar APC Bola Ahmad Tinubu, sai ya fadi wani abu na tarihi da ya faru dashi
Malam yace: a shekarar 2013 lokacin da jam'iyyar APC ta turashi wakilci jihar Anambra domin saka ido akan zaben Gwamnan jihar Anambra na Bye-election, a lokacin Peter Obi shine Gwamnan Anambra kuma yana neman tazarce, sai yasa jami'an DSS s**a k**a Malam Nasir El-rufai s**a kulleshi tsawon kwana 2
Malam Nasir El-rufai yaci gaba da cewa; yau nine Gwamna a Kaduna, ga Peter Obi yazo Kaduna kamfen din takaran shugaban kasa, bayan wasu hukumomin tsaro da nake da su a Kaduna, rundinar sojojin Nigeria na farko (Number One Division) tana nan garin Kaduna, amma ba zan sa a k**a Peter Obi ba, saboda mu 'yan Arewa wayayyu ne, inji Malam Nasir El-rufai
Na ji dadi da Malam ya yiwa Peter Obi irin wannan martani, musamman ma da yace mu 'yan Arewa wayayyu ne, tabbas hakane, mun waye ne saboda Musulunci, Musulunci ya wayar damu, Musulunci ya karantar damu martaba baki tare da basu kariya, ko ba komai Malam ya fito da martaban 'yan Arewa, domin wannan labarin yaja hankali sosai yana ta yaduwa
Yaa Allah Ka daukaka darajar Arewa da Musulunci
18/10/2022
MALAM YA BURGENI
Wato wani al'amari na tarihi ya faru a Kaduna jiya, kusan dukkan 'yan takaran shugabancin Nigeria a jam'iyyar APC, PDP da LP sun ziyarci Kaduna
Maigirma Gwamnan Kaduna Malam Nasir El-Rufai yana tare da dan takaran shugaban Kasa a jam'iyyar APC Bola Ahmad Tinubu, sai ya fadi wani abu na tarihi da ya faru dashi
Malam yace: a shekarar 2013 lokacin da jam'iyyar APC ta turashi wakilci jihar Anambra domin saka ido akan zaben Gwamnan jihar Anambra na Bye-election, a lokacin Peter Obi shine Gwamnan Anambra kuma yana neman tazarce, sai yasa jami'an DSS s**a k**a Malam Nasir El-rufai s**a kulleshi tsawon kwana 2
Malam Nasir El-rufai yaci gaba da cewa; yau nine Gwamna a Kaduna, ga Peter Obi yazo Kaduna kamfen din takaran shugaban kasa, bayan wasu hukumomin tsaro da nake da su a Kaduna, rundinar sojojin Nigeria na farko (Number One Division) tana nan garin Kaduna, amma ba zan sa a k**a Peter Obi ba, saboda mu 'yan Arewa wayayyu ne, inji Malam Nasir El-rufai
Na ji dadi da Malam ya yiwa Peter Obi irin wannan martani, musamman ma da yace mu 'yan Arewa wayayyu ne, tabbas hakane, mun waye ne saboda Musulunci, Musulunci ya wayar damu, Musulunci ya karantar damu martaba baki tare da basu kariya, ko ba komai Malam ya fito da martaban 'yan Arewa, domin wannan labarin yaja hankali sosai yana ta yaduwa
Yaa Allah Ka daukaka darajar Arewa da Musulunci
16/10/2022
ALHERIN ALLAH YA KAI WA ATIKU ABUBAKAR
Jihar Yobe tana daya daga cikin jihohin da Allah Ya jarrabesu da ambaliyar ruwa wanda ya cinye gidaje, dukiya da gonakin mutane har ma da asaran rayuka
Malamina Sheikh Dr Idriss Muhammad Saleh yana daya daga cikin masu bawa Maigirma Atiku Abubakar shawara akan harkokin addinin Musulunci, Dr Idris ya fito daga jihar Yobe, sai ya sanar da Atiku abinda ya faru na iftila'i a jiharsu na Yobe
Nan take Atiku ya kafa kwamiti, yace su duba abinda ya k**ata ayi na tallafi s**a kawo masa rahoto, ba tare da bata lokaci ba Atiku ya fitar da kudi Naira Miliyan hamsin (50,000,000) domin a tallafa wa mutanen da ambaliyar ruwan ya shafa
Gashi nan an sayo kayan abinci da sauran kayan bukata da kudin da Atiku ya fitar, zuwa ranar Monday za'a fara rabawa
Inda ace sauran shugabannin siyasa da masu neman takaran shugabancin Nigeria zasu bada irin wannan tallafi da Atiku ya bayar to da an saukaka mawuyacin halin da mutanen da ambaliyar ruwa ya shafa suke ciki, saboda Wallahi suna da tsananin bukatar tallafi daga al'umma da Gwamnati
'Yan siyasa duk sun san da wannan abin, sun ji sun gani, amma ba zasu tallafa ba saboda watakila basu da tausayin talaka, anan zamu ce Atiku ya fi su tausayin talaka
Muna rokon Allah Ya Ya cika wa Atiku burinsa na alheri akan rayuwar talakawan Nigeria
16/10/2022
SAI DA TALLAFI
Shima Kaka Tinubu ya je Kaduna taron KADINVEST
Bayan Kaka Tinubu ya gama jawabi na 'yan mintoci a tsaye da kyar, sai da Maigirma Gwamna Malam Nasiru El-rufai yazo ya k**ashi ya tallafa masa domin kar ya fadi
Allah Ka kara wa Kaka Tinubu lafiya
14/10/2022
Saboda Gasar Alqur'ani taci shiyasa babu wanda yake yabonta, ko labarin ta a shafin Facebook. Da ace Safara'u ce ta saki sabuwar waka ko wata wadda tayi fitar banza, da yanzu an karade shafukan sadarwa da labarin ta.
Wannan ita ce Aisha Abubakar Hussain, yar jihar Kano wadda tayi nasarar zama ta Biyu a gasar karatun Alqur'ani mai tsarki ta duniya wanda aka yi a kasar Dubai.
Ya Allah Kasa Alqur'ani yacece mu Ranar Lahira
Wanne fata kukeyi mata
12/10/2022
BUHARI BA SHINE MATSALAR BA
Maigirma Shugaban Kasarmu Nigeria Alhaji Muhammadu Buhari Maigaskiya yace zai kawar da matsalar tsaro kafin ya mika mulki ga sabuwar Gwamnati
Ina da yakini a cikin zuciyata shugaba Buhari da gaske yake wannan maganar, yana da burin ya kawar da duk matsalar tsaro, don haka shugaba Buhari ba shine matsalar ba
Inda Matsalar take shine wadanda ya basu amanar su kula masa da harkan tsaron, shin suna yin abinda ya dace?, mutanen da suke biyan 'yan jaridu su saye kafofin watsa labarai domin a boye gaskiya game da sha'anin tsaro saboda suna samun kudi makudai sune zasu kawar da matsalar k**ar yadda Buhari yake fata?
Koma yaya ne duk wani 'dan Nigeria yana ji yana gani, matsalar tsaron Nigeria ya koma harka ta neman kudi kawai
Don haka manyan azzalumai maciya amanar tsaro ba zasu taba bari a kawar da matsalar ba, matsalar zata kauce ne kawai idan shugaba Buhari yayi babban garambawul wa harkan tsaro mafi girma irin wanda ba'a taba yinsa a tarihin Nigeria ba
Wato a kakkabe duk wani azzalumi maciyin amana daga cikin sha'anin tsaro, imba haka Buhari yayi ba ko wanda zai gaje shi yayi ba; to babu abinda zai canza
Muna fatan Allah Ya bamu mafita na alheri
09/10/2022
MASHA ALLAH
Sunanta Aisha Abubakar Hussain daga jihar Kano, tazo na biyu a gasar Karatun Qur'ani na duniya izu sittin da ya gudana a Daular Larabawa Kasar Sudan
Allah Ya sa Qur'ani Ya cecemu ranar Hisabi
Address
Telephone
Website
Alerts
Be the first to know and let us send you an email when World news posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.
Shortcuts
- Address
- Telephone
- Alerts
- Claim ownership or report listing
-
Want your business to be the top-listed Media Company?