Da'irar Tudun Wadar Dankadai

Da'irar Tudun Wadar Dankadai Domin Samun Ingantattun
Rahoton Kasance da ABS CHANNEL. dakuma Sayyid Ibraheem Zakzaky Office

Gayyata! Gayyata!! Gayyata!!!Ana Gayyata Ƴan uwa Musulmi  Birthday na Shaheed Bilya faska Wanda za'ayi Tudun Wada ɗankad...
30/04/2024

Gayyata! Gayyata!! Gayyata!!!

Ana Gayyata Ƴan uwa Musulmi Birthday na Shaheed Bilya faska

Wanda za'ayi Tudun Wada ɗankade
Ranar Gobe Laraba
Lokaci 3:00 Pm

Wuri :-yan Awaki ss
Can wajejen Memorial kankwar Ikara wata makaranta mai jan bugun kwano

Babban Mawaki Shamsudden Fudiyyah
Malami mai jawabi Ibraheem Muhammad (Ya Malam)

A Iso lafiya

Aliyu S Ibraheem

ME YA SA JAMI'AN TSARO SUKAI HARBI A KADUNA? (1)Da yake su ƴan siyasa s**an yi shiru ne, ba su cewa komai, su ya k**ata ...
22/04/2024

ME YA SA JAMI'AN TSARO SUKAI HARBI A KADUNA? (1)

Da yake su ƴan siyasa s**an yi shiru ne, ba su cewa komai, su ya k**ata su yi magana, ya k**ata duk lokacin da aka yi harbi (aka harba bindiga) ko ba a kashe mutum ba, to lallai za ka ga a wasu ƙasashen sai ministan cikin gida ko wani a cikin ministoci ya yi magana, to amma anan kasar za a kashe mutane za ka ji tsit, kuma an san cewa ba yadda za a yi a harba bindiga haka kawai, to amma tambaya ita ce me yasa a Kaduna? Tambaya kenan, dayake su ƴan sanda su s**an yi magana, an ce mai magana da yawun ƴan sanda ya yi magana, maganar tasa ta rashin kan-gado; na farko yace wannan kungiya an haramta ta a jihar Kaduna, na biyu kuma yace su basu kashe kowa ba, na uku kuma yace sun yi amfani da hayaƙi mai sa hawaye ne, su ba su yi amfani da harsashi mai rai ba.

To in ka ga maganar tasa da karo, na farko doka ta hana Ƙungiya ne yace ko? Wannan kungiyar an haramta ta a jihar Kaduna, sai muce to idan aka haramta kungiya a jiha shi kenan kana iya kashe yan kungiyar kenan? Kana iya zuwa ka kashe su kenan? Mene ma'anar haramtawa ɗin in akwai doka? Ko ba a lura ba, ai dokar dole za ta ce in an haramta abu za ace wanda yake yi kila za a k**a shi ne a kai shi kotu ai masa hukunci, kotu ta ce ya yi kungiyar da aka haramta ko? Amma ba kashe shi za ka je ka yi ba ko?.

To sannan kuma muna bukatar mu ga dokar, wadda ta ce ainihin lallai wannan doka ta haramta maka kuma ka fito ka goyi bayan Falasdinu, ko ka yi Allah wadai da Isra'ila, don ya k**ata dokar ta fadi haka nan, don ya k**ata kuma dokar ta fadi mene ne aka hana wannan kungiyar, an hana su sallah ne? Ko An hana su azumi ne? An hana su daurin aure ne, ko juma'a ne? Da wannan fitowa a goyi bayan Falasdinu shi ma an hana su ne? Ko ba a lura ba? Sai dokar ta yi bayani.

Sannan kuma harwalayau wani abin mamaki jihar da ake ce mata Kaduna ba a Kaduna da Zariya kawai aka yi ba, an yi a Saminaka, da Birnin Gwari da Kafanchan, to tambaya, su kuma waɗannan ba jihar Kaduna bane? Aka yi na Saminaka lafiya lau? Birnin Gwari lafiya lau? Na Kafanchan lafiya lau? Me yasa to? Ai kaga ya k**ata suma aje, in wajibinku shi ne a harbi wayannan.

Sannan banda wayannan, hatta na Zariyan ma akwai wayanda aka yi a bangaren Zariya city, masu ibara suna cewa Zariya local government ko? Akwai wanda aka yi kuma aka dauko daga Sabon gari, Sabon gari local government kenan ko? To shi kuma shima ya halatta a yi a Zariya local government ne ya haramta ayi a Sabon gari local government? Saboda na Zariyan an yi an gama ba a yi harbi ba, sai na sabon gari aka yi harbi.

Wani bangare na jawabin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) a ganawarsa da wakilan yan'uwa a bikin karamar sallah ranar Talata (7/Shawwal/1445) a gidansa da ke Abuja.

Zan ci gaba Insha'Allahul Azeem.

Muhsin Shu'aibu Konkiyel
12/Shawwal/1445 (21/4/2024)

SUNJI TSORO A BASU RUWAN MADACI...."Muna ganin zai yi matukar wahala a sake maimaita gagarumin nasarar da muka samu waje...
16/04/2024

SUNJI TSORO A BASU RUWAN MADACI....

"Muna ganin zai yi matukar wahala a sake maimaita gagarumin nasarar da muka samu wajen dakile harin ranar Asabar, idan Iran ta sake harba daruruwan mak**ai masu linzami da UAV, kuma Isr**lawa sun san hakan,"

Inji wani babban jami'in Amurka da ya shaidawa Walla News.

Sakataren harkokin wajen Amurka a Lincoln ya shaidawa shugabannin yahudawan da ya gana da su a yau cewa, "takun saka da Iran ba zai cimma muradun Isra’ila ko Amurka ba".

Inji Blinken ya isar da wannan saƙon a wata tattaunawa da Benny Gantz jiya.

GAYYATA ! GAYYATA !! GAYYATA!!!    Da'irar Tudun Wadar Dankadai Suna farincikin Sanar Da yan'uwa Na yankin Tudun wada da...
16/04/2024

GAYYATA ! GAYYATA !! GAYYATA!!!

Da'irar Tudun Wadar Dankadai

Suna farincikin Sanar Da yan'uwa Na yankin Tudun wada da kewaye
Gagarumin MU'UTAMAR Wanda zata gabatar
Ma wuni Guda

Kudin Rtl:- #300
Ranar:-Alhamis
Lokaci:-8:00
Wuri:-Kazimiyya


Domin karin bayani
Atuntubi
Wannan Lambar waya:-
+2348063982779
08144925669
09037503448

Sanarwa daga
Dan dalin matasa

New Update
16/04/2024

New Update

BABU SOJA KAMAR SOJAN SHI'A. Shin kai Dan Shi'a ne?To Saurari Abinda ake Fada Akanka!! Idan Kai Ba Dan Shi'a Bane To Sau...
15/04/2024

BABU SOJA KAMAR SOJAN SHI'A.

Shin kai Dan Shi'a ne?
To Saurari Abinda ake Fada Akanka!! Idan Kai Ba Dan Shi'a Bane To Saurari Abinda Ake Fada Akanmu Mu 'Yan Shi'a
- Sarki Abdulazeez Yana Cewa:
Syria Bata Bukatar Jarumai domin Jarumanta 'yan Shi'a ne Wadanda Basa Gudu a Fagen Fama.
-Fedil Faransyun Yana Cewa:
Wawayene Wadanda S**a Mamayi Daular Da Jama'arta 'Yan Shi'a ne , Domin Basa Qosawa Basa rauni
-Saddam Hussain Yana Cewa: Duk digo daya na Jinin 'Yan Shi'a Yana haifar da Mujahidai
-Kasanjar Yana Cewa: Bazaka samu Jarumai Nagartattau Kamar Jaruman Shi'a ba.
-Hajjaj Yana Cewa:
Kada Haqurinsu Ya Rudeku , Kada Ku Zaci Rauninsu Rashin Karfi ne, Domin idan Sun Mike domin Taimakawa wani basa Barin sa sai Kambu Yazo Hannunsu , Ku nemi Taimako dasu Domin Sune Fiyayyun Jarumai a Bayan Qasa,
- Amma kuji tsoron taba Musu Abubuwa uku
- Matayensu
Idan Kuka Taba musu Mata Zasu Farauceku Tamkar Zakoki
-Gona-Gonakinsu
Idan Kuka Taba Gonakinsu Zasu Yaqeku Tamkar kafaffun duwatsu
- Addininsu Idan kuka Taba Addininsu Zasu Qone Wannan Duniyar Taku
-Wani malamin falsafa Daga Japan Yace:
' Yan Shi'a Suna Tashi Da Fukafukai Biyu
- Nafarko Shine Abinda Ya wuce Wato Waqiar Karbala
-Nabiyu Kuma Fatan Bayyanar Imam Mahdi AJf To ta Yaya Za'a Karya su

Allah Mun Godema Bisa Niimar Wilay-Nabiyu Kuma Fatan Bayyanar Imam Mahdi AJf To ta Yaya Za'a Karya su Allah Mun Godema Bisa Niimar Wilaya.

Ƙawancen Iran da Isra'ila da yadda s**a zama makiyan juna.Ƙasar Iran da Isra'la ƙarƙashin daular Pahlavi sun kasance ƙaw...
14/04/2024

Ƙawancen Iran da Isra'ila da yadda s**a zama makiyan juna.

Ƙasar Iran da Isra'la ƙarƙashin daular Pahlavi sun kasance ƙawayan juna tun daga 1925 har zuwa 1979, wato zuwa shekarar da akayi juyin juya hali ƙarƙashin jagorancin Imam Khomeini kenan.

Iran ba wai da Isra'ila kawai take ƙawance ba har da Amurika da ƙawayanta da sauran ƙasashen larabawa k**ar ƙasar Saudiyya, dss. Kai Iran ta ma kasance ƙasa ta biyu bayan ƙasar Turkiyya data amince da ƙasar Isra'ila bayan samar da ita a shekara ta 1948, wato shekara uku bayan yakin duniya na biyu kenan.

Iran na daya daga cikin mambobi 11 na kwamitin musamman na Majalisar Dinkin Duniya da aka kafa a shekara ta 1947 don samar da mafita ga Falasdinu bayan da Birtaniya ta ƙare iko da yankin a wancan lokacin.

Akwai wani masanin tarihi daga jami'ar Oxford mai suna Eirik Kvindesland ya taba shedawa Aljazeera a wata hira datai dashi inda yake cewa: "Iran, tare da Indiya da Yugoslavia, sun fito da wani tsari na daban, wanda zai zama mafita akan rikicin dake faruwa a gabas ta tsakiya. Sun nuna yadda ya k**ata a mayar da Falasdinu a matsayin kasa daya mai majalisar dokoki ɗaya amma wacce zata kasu gida biyu, wato kashin Larabawa da na Yahudawa."

Yaci gaba da cewa: "wannan shi ne salon sulhun ƙasar Iran a wancan kokarin duk domin taci gaba da kyautata alakarta da kasashen yamma masu goyon bayan sahyoniyawa da ita kanta kungiyar yahudawan sahyoniya, da ma kasashen Larabawa da musulmi makwabta."

Sannan idan muka sake waiwayar tarihi k**ar a 1970s, wato shima kafin 'revolution' na Iran za muga akwai alaƙa mai kyau tsakanin Iran da Saudiyya. Duk ƙasashen biyu a wannan lokacin sun kasance masu arzikin da duniya ta shedi suna da arzikin da ba'a taba ganin ba. Saboda haka akwai alaƙa mai kyan gaske tsakanin sarakunan ƙasashen biyu, wato Mohammed Reza Pahlavi da sarki Faisal na Saudiyya a waccan lokaci, sun ƙaddamar da tsare tsare a junansu na bunƙasa tattalin arziki da gina sojoji, zamantakewa kuma a wannan lokacin kowannensu ya babban birnin ƙasarsa, wato Riyadh da birnin Tehran, sannan duk ƙasashen biyu suna da alaƙa mai ƙarfi da ƙasar Amurika.

To amma mai ya faru bayan juyin juya halin Iran?

A shekara ta 1979, aka kifar da gwamnatin Shah ta hanyar juyin juya hali wanda ya haifar da Islamic Republic of Iran.

Jagoran juyin juya halin, wato Ayatullah Ruhollah Khomeini ya haifar da wani sabon ra'ayi ga duniya wajan ganin musulmi sun tsaya da ƙafafunsu dayin fafutukar ganin sun yi tsayin daka wajan kwatar ƴancinsu daga "masu girman kai" (world powers) da kuma abokansu na yankin (Isra'ila), dss, wadanda suke zaluntar masu rauni - ciki har da Palasdinawa - don biyan bukatunsu. Wanda a wannan lokacin har sai da Imam Khomeini ya kira Isr**la da "little Satan" ya kuma kira Amurika da "Great Satan"

To a saka makon haka, sai Tehran ta yanke duk wata alaka da Isra'ila; yan ƙasa ba za su iya tafiya zuwa can ba, s**a soke duk wasu hanyoyin tashi da saukar jiragen sama tsakanin ƙasashen; sannan kuma ofishin jakadancin Isra'ila da ke Tehran ya koma ofishin jakadancin Falasdinu. Sannan Imam Khomeini ya shelanta duk ranar Juma'ar ƙarshen Ramadan a matsayin Quds Day, da kira ga musulmin duniya akan su fita yin jerin gwano na lumana domin bayyana goyon bayan al'ummar palasdinawa da rashin amincewa da zalunci da ake musu.

Saboda haka mu fahimci babbar matsalar Iran a wajan yammacin duniya shine rashin amincewa da samuwar ƙasar Isra'ila da goyon bayan da take bawa Palasdinawa. Dan haka da yanzu Iran zata daina goyon bayan Palastine kuma ta yadda da samuwar Isra'ila to da tabbas Iran ta zama babbar ƙawa ga manyan ƙasashen duniya kuma da duk takunkumin karya tattalin arziki an dauke mata shi.

Saboda haka duk wani malami ko wani mara bibiyar lamura da k**anta adalci ya faɗa maka wani abu sabanin haka, to wallahi ƙungiyanci da siyasar addini da son ransa kawai yake cusawa kwakwalwarka. Amma wallahi, matsalar Iran a wajansu ita ce goyon bayan Palasdinawa, da ƙin amincewa da Sahyonyanci (zionism)

Jaafar A Sarki

A GAGGAUCE....Amurka ta bukaci Iran ta hanyar Qatar da ta gaggauta dakatar da harin da take kaiwa Isra'ila;  Iran ta yi ...
14/04/2024

A GAGGAUCE....

Amurka ta bukaci Iran ta hanyar Qatar da ta gaggauta dakatar da harin da take kaiwa Isra'ila; Iran ta yi watsi da bukatar, kuma ta yi barazanar kai hari kan sansanonin Amurka idan Amurka ta shiga tsakani.

Ƙarfin Soji da kayan faɗ*a tsakanin Iran da Isra'ila (Iran kwata-kwata ba sa'ar Isra'ila bace)Iran 🇮🇷 vs Israel 🇮🇱Yawan ...
14/04/2024

Ƙarfin Soji da kayan faɗ*a tsakanin Iran da Isra'ila (Iran kwata-kwata ba sa'ar Isra'ila bace)

Iran 🇮🇷 vs Israel 🇮🇱

Yawan Jama'a:
Iran 🇮🇷: mutum milyan 87.6M
Israel 🇮🇱: mutum milyan 9.04M

Yawan dakarun Soji:
Iran 🇮🇷: Sojoji milyan 49.05M
Israel 🇮🇱: Sojoji milyan 3.80M

Zaratan matasa masu jiran ko ta kwana:
Iran 🇮🇷: milyan 41.17M
Israel 🇮🇱: milyan 3.16M

Sojoji dake bakin aiki:
Iran 🇮🇷: dubu ɗari 610
Israel 🇮🇱: dubu ɗari 170K

Jami'an tsaro dake jiran ko ta kwana:
Iran 🇮🇷: dubu dari 350K
Israel 🇮🇱: dubu dari 465K

Kungiyoyin sa kai na tsaro:
Iran 🇮🇷: dubu dari 220K
Israel 🇮🇱: dubu 35K

Jiragen soji:
Iran 🇮🇷: 551
Israel 🇮🇱: 612

Tankokin yaƙi:
Iran 🇮🇷: 65,765
Israel 🇮🇱 : 43,407

Manyan Jiragen yaki:
Iran 🇮🇷: 101
Israel 🇮🇱: 67

Jiragen yaƙi na ƙarƙashin ruwa:
Iran 🇮🇷: 19
Israel 🇮🇱: 5

Filayen Jirage:
Iran 🇮🇷: 319
Israel 🇮🇱: 42

Jiragen sojin ruwa:
Iran 🇮🇷: 942
Israel 🇮🇱: 45

Tattalin arziki:
Iran 🇮🇷: Tana samar da gangan mai 3.45M bbl
Israel 🇮🇱: 0 bbl (babu)

ABIN LURA: Idan aka ce Isra'ila ana nufin duk da haɗaka da taimako da take samu daga Amurka (NATO) da Ingila da su Germany amma duk da haka Iran ba sa'ar Isra'ila bace....

MA'ANAR BAKIN HIJABI ( REVOLUTION) !Repost : ga sisters dasuke bada priority na coloured hijab lokacin bukukuwa .Shifa H...
13/04/2024

MA'ANAR BAKIN HIJABI ( REVOLUTION) !

Repost : ga sisters dasuke bada priority na coloured hijab lokacin bukukuwa .

Shifa HIJABI ba abune da yazo a al'ada ba b***e muke kallan al'ada ce tazo Mana dashi, wane Irin tunanine yazoma sisters a farkon gwagwarmaya suke Sanya hijabai kala-kala Amma daga baya s**a koma Sanya bakin hijabi. adaidai wannan lokacin abune mai wahala ka iya kirga goman sisters da wani kalan hijabi akasin Baki a wajen tarukan harka da wuraren buki, akwai wani tunani da yake shigo mana Wanda ake Kira da (mind control) fikirar mu ke canzuwa ba tare da mun saniba. a duk inda kaga sister da cikaken hijabi, zakaga lallai akwai addini a tattare da ita tare da cikakkiyar izzah, Amma ban san wane tunanine yazo mana ba ko na cigabane ko cibaya muka ajiye izzarmu da alamin addinin mu muka dauki wani abu daban.

Fahimtar imam Alkhumaini akan Al'amarin hijabi lallai ya bambamta da irin tunaninmu a yanzu, shi fa bakin hijabi alami na revolution inji imam Alkhumaini, da makiya zasu Shiga cikin kauyuka da birane suna hangen bakaken hijabai da lallai sun gaza bacci dajin cewa ana gab da murkushe su . a matsayinki na sister Yar gwagwarmaya Kuma revolutionary yak**ata ki kula da wannan.

Ra'ayin wani Matashin Ahlussuna mai Suna "Abu Huraira Abdullahi Nce" akan kashe 'Yan Shi'a.Dangane da lamarin shi'a, zan...
09/04/2024

Ra'ayin wani Matashin Ahlussuna mai Suna "Abu Huraira Abdullahi Nce" akan kashe 'Yan Shi'a.

Dangane da lamarin shi'a, zan ƙara bada wani labari. Sai dai na san shi wanda ke aikata hakan fahimtar sa ce ta sa yake haka. An kashe shi a zariya lokacin da aka yiwa ƴan shi'a zalunci shi da ƴaƴan sa mata guda biyu. Sunan sa Mallam shafiu, abinda yake yi shine; duk lokacin da aka yi albashi na aikin gwamnati da yake yi, sai ya irga kwanakin asabar da Lahadi wanda be je aiki ba ya mayar ta hanyar data dace. Yace shi ba zai iya cin kuɗin da bai yi gumi a kan su ba.
Wannnan ma ɗan shi'a ne!

Na biyu kisan ƙare dangin da ake yiwa Falasɗinawa, ba wata ƙasa ta musulunci da take raddi tare da basu gudummawa sai ƙasar da ake musu kallon ƴan shi'a. Ƴan shi'a suna jin cewa Falasɗinawa ƴan uwansu ne Musulmi. Wasu kuma sun ce kafirai ne.

Sai abinda ya shafi sojin Najeriya; me yasa ga ƴan ta'adda nan amma ba za'a iya amfani da harsashi a kan su ba sai ƴan shi'a waɗanda basu takawa kowa ba, basu zubarwa kowa ba? Ka ƙaddara ƴan shi'a da gaske yaƙar gwamanti suke son yi, a tunanin ku ba zasu fi kowane ɗan ta'adda a najeriya buwayar gwamnati ba ? Na san wani ze ce; ga gurin nan, su yi mana! Masu yin ta'addancin kullum ba sune da riba akan gwamnatin ƙasar ba, tunda kullum sai dai ace ayi sulhu?

Ƴan shi'a musulmai ne, tunda basu fito ƙarara sunce su ba musulmi bane. Basa kallan musulmi na wani ɓangare a matsayin wanda zai shiga wuta automatic ticket tunda yace shi ga akidar sa. Idan ka yiwa ɗan shi'a sallama zai amsa, yana karanta Qur'ani, da Qur'ani yake Shari'a.

Har gobe wallahi ina yiwa ɗan shi'a kallon ɗan uwana musulmi, akidar sa can ya je ya ji da ita, nima naji da tawa! Ba zan manta da wani karatun marigayi Sheikh Abubakar Gero argungun ba, yake cewa; gwara ɗan shi'a sau dubu da kafiri, domin ko ba komai zai kira sallah da asuba ka farka ka tafi masallacin da kake so. Allah ya kai rahama kabarin sa ameen. Anan me yasa Mallam bece ɗan shi'a kafiri bane ? Sai kai, saboda k fi shi ilimi ko me ?

RA’AYÍ: Shin Da Wace Irin Doka Akewa Mabiya Malam Zakzaky Húkunci A Najèriya Ne, Cewar Wani Babban Lauya A Kasar Nayi ma...
08/04/2024

RA’AYÍ: Shin Da Wace Irin Doka Akewa Mabiya Malam Zakzaky Húkunci A Najèriya Ne, Cewar Wani Babban Lauya A Kasar

Nayi mamaki irin yadda naga mabambantar ra'ayoyi akan haadisañ data faru a Zaria da Kaduna tsakanin Yan Shi'a mabiya Sheikh Zakzaky da jami'an tsar0n Najeriya wacce tayi sanadin ra$a rayúka da samun munanan raunúka daga bangaren mabiya Sheikh Zakzaky. Abun da ya fi bani mamaki shine yadda wasu lauyoyi suke ganin ahliyya ko shar'iyyar ki$an Yan Shi'a sab0da suna zagin Sahabbai da matan manz0n Allah (SAWW).

Ina wannan rubutun ne a matsayina na lauya saboda haka ina kallon abun ne ta mahangar shari'a matsalar zagin Sahabbai matsalace k0 ince tuhuma ce aqa'idiyya wacce shekaru fiye da dari bakwai ana tattauna ta a majaloli na ilimi daban daban tsakanin malamai wanda a zauren karatu ne kawai za'a iya hallale matsalar ba'a t**i ko a soshal midiya ba.

Muqaddara Yan Shi'a suna zagin Sahabbai da matan Manzan Allah (S.A.W.W.) wanda wannan tuhumar Yan Shi'ar sun dade suna musantata. Mu qaddara cewa suna zagin Kuma hukuncin zagin shine kisa. In dai da dokokin Najeriya za'a yi musu hukunci k**asu za'ayi sannan a gurfanar dasu a kotu in kotu ta samesu da laifi shine za'a kashe su. Dan neman karin bayani za'a iya duba sashi na 33 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 sannan za'a iya duba shari'ar da kotun koli tayi tsakanin Nasiru Bello da Attorney General na Jahar Oyo zaka Ga yadda a qayyama rai.

Qa'ida itace kowa ne matuhumi bari'un ne akan tuhumar da ake masa (wato duk wanda ake tuhuma da aikata wani laifi ana kallon sa k**ar bayyi bane) har sai mai tuhuma ya tabbatar da tuhumar sa. Sashi na 139 na kundin tafi da sheda na Najeriya na 2023 cewa yayi nauyin tabbatar da da'awa ko tuhuma tana wuyan mai tuhuma ne kuma sashi na 36 (5) na kundin tsarin mulkin Najeriya shima abun da ya tabbatar kenan bugu da kari malam Mai Tuhufah da sauran Malamai na musulunci suma maganar su kenan nauyin tabbatar da da'awa tana wuyan mai tuhuma ne.

Mutum Dan uwanka ne ko'a mut

Kyawawan Hotunan Ƙabarin Gwarazan Shahidan Harkar Musulunci a Nijeriya, Karkashin Jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)...
08/04/2024

Kyawawan Hotunan Ƙabarin Gwarazan Shahidan Harkar Musulunci a Nijeriya, Karkashin Jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H).Shahid Hamid Ibraheem Zakzaky da Shahid Ahmad Ibraheem Zakzaky sai kuma Shahid Mahmud Ibraheem Zakzaky.

Duk Cikarsu 'ya'ya ne ga Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

Hoto: Salisu Jibril Khidir
📸 Da'irar Tudun Wadar Dankadai

Kyawawan Hotunan Ƙabarin Shahidai 'yan uwa Musulmai Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) da ke Dambo, Zariya.Hoto: Sali...
08/04/2024

Kyawawan Hotunan Ƙabarin Shahidai 'yan uwa Musulmai Almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) da ke Dambo, Zariya.

Hoto: Salisu Jibril Khidir
📸 Da'irar Tudun Wadar Dankadai

CP AUDU DABIGIKwamishinan 'yan sandan jihar Kaduna, wanda ya jagoranci kisan 'yan uwa Musulmi shida, tare da jikkata gom...
08/04/2024

CP AUDU DABIGI

Kwamishinan 'yan sandan jihar Kaduna, wanda ya jagoranci kisan 'yan uwa Musulmi shida, tare da jikkata gomomi a ranar Juma'ar karshen Ramadan 1445 (5/4/2024).

Muna rokon Allah Ta'ala Ya tsine masa albarka. Ya sa ya yi mummunan karshe. Allah kar Ya raba shi da aikin dan sanda lafiya.

Insha Allah za mu karisa Ramadan da kai kokenmu wajen Allah Ta’ala akanka, da iyayen gidanka da s**a baka aikin kisan, da wadanda s**a taimaka maka wajen kashe Musulmi dauke da Azumi a bakinsu.

SANARWA: بِسْمِ اللَّـهِ الرَّحْمَـٰنِ الرَّحِيمِ اللهم صل على محمد وعلى آل محمد🌹 Daga: Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky ...
08/04/2024

SANARWA:

بِسْمِ اللَّـهِ الرَّحْمَـٰنِ الرَّحِيمِ

اللهم صل على محمد وعلى آل محمد🌹

Daga: Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).

Ana sanar da ƴan uwa da su fara duba jinjirin watan Shawwal daga Yau Litinin 29 ga Ramadan, 1445. Za a iya sanar da labarin ganin watan ta waɗannan lambobi:

07064194054
09036186572
08035686569

Wassalam




28/Ramadan/1445
07/04/2024

07/04/2024

Ta'aziyya Zuwa Ga Sahihul Asri Wazzaman

Cigaban «DAURA ILMIYYA THAQAFIYYA» zama na TakwasMai take: Ilimi linzamin ďan gwagwarmaya.cigaba da gudanar da Daura ili...
07/04/2024

Cigaban «DAURA ILMIYYA THAQAFIYYA» zama na Takwas

Mai take: Ilimi linzamin ďan gwagwarmaya.

cigaba da gudanar da Daura ilimiyya zama na shida sati na Hudu a ramadan 1445.

Darasinmu na yau shi ne:-
Tsarabar Mumini daga Watan Ramadan

Tare da: M.Ibraheem Yahuza Muhammad

2-Katama_Jawabi Kammala daura Ta Wannan Wata

Tare da :-Wakilin Yan Uwa Na Da'irar Tudun Wada Dan Kadai
Malam Yahya Rabi'u

A yau Lahadi 28/9/1445=07/4/2024 ýan uwa Almajiran Sayyid Ibrahim zakzaky (H) na yankin Tudun wadar Dankadai suke cigaba da gudanar da Daura ilmiyya wadda take gudana a ranakun Asabar da Lahadi na watan Ramadan mai alfarma.

Allah ta'ala ya amshi ibadunmu.

📸 Da'irar Tudun Wadar Dankadai

Muzarar Qudus 🇦🇪🇦🇪🇦🇪 Ke gudana A Da'irar Tudun Wadar Dankadai Domin nuna goyon Bayan Yan Uwanmu Musulmi Na duniya
06/04/2024

Muzarar Qudus 🇦🇪🇦🇪🇦🇪 Ke gudana A Da'irar Tudun Wadar Dankadai
Domin nuna goyon Bayan Yan Uwanmu Musulmi Na duniya

06/04/2024

Yanzu Haka :-Muzaharar Qudus🇦🇪🇦🇪 Ke gudana
A Garin
Tudun wadar Dankadai

04/04/2024

"Taimakon Falastinu a Wajanmu Lallai Addini ne."

-Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) wani yanki cikin jawabin nuna goyon baya ga Al'ummar Falastinu na bana 2024.

Raya daren 23Yadda Yan Uwa Almajiran Sayyid Zakzaky (H)     Nagarin Tudun wadar ƊankadaiSuke Addu'oin Bayan Kammala SALL...
02/04/2024

Raya daren 23
Yadda Yan Uwa Almajiran Sayyid Zakzaky (H)
Nagarin Tudun wadar Ɗankadai
Suke Addu'oin Bayan Kammala SALLAR raka 100 Daren
Yanzu Haka Bayan Kammala ( Jaush kabeer /Jaush Sageer dadai sauran Addu'oin da suke cikin Wannan Daren
Fatanmudai Allah Yasa muna daka Cikin Bayin Da Ake Yantawa Acikin Wannan Wata Mai Albarka BIHAQQI MUHAMMAD WA'ALI BAITY
📸 Da'irar Tudun Wadar Dankadai

Cigaban «DAURA ILMIYYA THAQAFIYYA» zama na ShidaMai take: Ilimi linzamin ďan gwagwarmaya.cigaba da gudanar da Daura ilim...
31/03/2024

Cigaban «DAURA ILMIYYA THAQAFIYYA» zama na Shida

Mai take: Ilimi linzamin ďan gwagwarmaya.

cigaba da gudanar da Daura ilimiyya zama na shida sati na uku a ramadan 1445.

Darasinmu na yau shi ne:-
Ilimin Zamantakewar na Rayuwar Malam Bahaushe
(Darasi Hausa

Tare da: M. Muhammad Shaheed Alhassan

A yau Lahadi 21/9/1445=30/3/2024 ýan uwa Almajiran Sayyid Ibrahim zakzaky (H) na yankin Tudun wadar Dankadai suke cigaba da gudanar da Daura ilmiyya wadda take gudana a ranakun Asabar da Lahadi na watan Ramadan mai alfarma.

Allah ta'ala ya amshi ibadunmu.

📸 Da'irar Tudun Wadar Dankadai

Daga Muhallin Yan Uwa Almajiran Sayyid Zakzaky (H)Yadda Malam Ibraheem Muhammad Yake jagorantar Addu'oin  📸 Da'irar Tudu...
31/03/2024

Daga Muhallin Yan Uwa Almajiran Sayyid Zakzaky (H)
Yadda Malam Ibraheem Muhammad Yake jagorantar Addu'oin

📸 Da'irar Tudun Wadar Dankadai

Yadda Yan Uwa Almajiran Sayyid Zakzaky {H}           Sukegabatar da Zaman Juyayi Shahadar IMAM ALI  Bayan Kammala AZAH  ...
30/03/2024

Yadda Yan Uwa Almajiran Sayyid Zakzaky {H}
Sukegabatar da Zaman Juyayi Shahadar IMAM ALI Bayan Kammala AZAH
Tare da Raya wannan Dare Na 21 Ga RAMADAN cikin Juyayi
Labari cikin Hotuna
Daga
📸 Da'irar Tudun Wadar Dankadai

30/03/2024

Ali Ya Ali Hydaraaaaa Nurul Ardi Wassamah
😭😭😭😭

Cigaban «DAURA ILMIYYA THAQAFIYYA» zama na biyar.Mai take: Ilimi linzamin ďan gwagwarmaya.cigaba da gudanar da Daura ili...
30/03/2024

Cigaban «DAURA ILMIYYA THAQAFIYYA» zama na biyar.

Mai take: Ilimi linzamin ďan gwagwarmaya.

cigaba da gudanar da Daura ilimiyya zama na biyar' sati na uku a ramadan 1445.

Darasinmu na yau shi ne:-
Siyasa Islamiyya a Mahangar
Imam Khomaini (QS) da
Da'awar Sayyid Zakzaky (H)

Tare da: M. Muhammad Bakir Salisu

A yau Asabar 20/9/1445=30/3/2024 ýan uwa Almajiran Sayyid Ibrahim zakzaky (H) na yankin Tudun wadar Dankadai suke cigaba da gudanar da Daura ilmiyya wadda take gudana a ranakun Asabar da Lahadi na watan Ramadan mai alfarma.

Allah ta'ala ya amshi ibadunmu.

📸 Da'irar Tudun Wadar Dankadai

29/03/2024
29/03/2024

Maula Ali

Address

Tudun Wada Local Government
Tudun Wada

Telephone

+2349069706764

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Da'irar Tudun Wadar Dankadai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Da'irar Tudun Wadar Dankadai:

Videos

Share


Other Digital creator in Tudun Wada

Show All

You may also like