Turakar Hausa

Turakar Hausa Jaridar Internet mai kawo sahihan labarai a ciki da wajen Najeriya

Atiku Abubakar Dan Kishin Dumokradiyya ne-Yasir Ramadan Gwale Hukuncin kotun koli a ranar Alhamis ya nuna cewa duk wata ...
26/10/2023

Atiku Abubakar Dan Kishin Dumokradiyya ne-Yasir Ramadan Gwale

Hukuncin kotun koli a ranar Alhamis ya nuna cewa duk wata Shariah da ta ke da alaka da zaben shigaban kasa na 2023 a Najeriya ta zo karshe, kuma shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu shi ne halastaccen shugaban Najeriya. Don haka babu wani batun sabon zaben shugaban kasa ko zuwa kotu har sai nan da shekarar zabe ta 2027. Nan da shekaru hudu masu zuwa, Alhaji Atiku Abubakar zai cika shekaru 81 a duniya, bana zaton a wannan lokacin idan Allah yasa yana nan zai iya samun damar tsayawa takarar shugabancin Najeriya a karo na biyar.

Babu mamaki Allah bai kaddarawa Alhaji Atiku Abubakar zama shugaban Najeriya ba, wannan kuma ba wata tawaya bace a gare shi, watakila nan gaba cikin zuri'arsa a samun wanda za su yi shugabanci har zuwa matakin shugaban kasa. Amma sanin kowa ne cewar Alhaji Atiku Abubakar yana daga cikin manya kuma fitattun 'yan siyasa a Najeriya da tarihi ba zai manta da su ba. Na taba jin dan Masanin Kano ya fada cewar mutum biyu a Arewa ba a yi 'yan siyasa k**arsu ba, idan ka cire Sa Ahamadu Bello to babu k**ar Shehu Musa YarAdua da kuma Atiku Abubakar. Kamar yadda yace a kudu idan ka cire Awolowo, babu wasu 'yan siyasa k**ar MKO Abiyola da Bola Ahmed Tinubu ba a cewarsa.

Ba shakka Alhaji Atiku Abubakar jajirtaccen dan siyasa ne maras tsoro kuma jarumi. A yanzu a Arewa babu wani dan siyasa da ya kai Atiku kashe kudi wajen yin hidima ga al'umma sarakuna da attajirai da talakawa, yana kashe kudi k**ar baya tsoron talauci, wadan da duk s**a yi mu'amala ta kurkusa da shi suna bayyana shi a matsayin mutum mai karamci da taakawa ga kuma tsoron Allah, mutum ne ance mai girmama mutane da son yi musu hidima da aljihunsa. Abu guda daya da ba zaka taba zargin Alhaji Atiku Abubakar da shi ba shi ne rashin kishin demokaradiyyar Najeriya. Zaka iya zarginsa da komai, amma ba zaka zarge shi da rashin kishin demokaradiyya a Najeriya ba.

Ko shakka babu Atiku Abubakar mutum ne da ya yadda kuma ya gamsu da samar da dunkulalliyar Najeriya da kowa zai yi alfahari da ita a matsayin dan kasarta, bugu da kari kuma gashi cikakken dan demokaradiyyar da ya yadda da hidimtawa alumma fama kasa baki daya a ko da yaushe. Shi ne dan siyasa guda daya tilo a wannan zamanin daga yankin Arewa da zai yi maka kyautar da baka taba tsammani ba, mutane su zage shi suci mutuncinsa gobe su dawo wajensa kuma ya dauki kudi ya basu yana murna yana fara'a, samun dan siyasa kwararre irinsa sai an tona kwarai da gaske muna yiwa Alhaji Atiku Abubakar fatan alheri da fatan Allah ya karbi kyawawan ayyukansa na alheri ya kuma yafe kurakuransa baki daya Amin.

Muna fatan alheri ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, Allah yayi masa jagoranci ya tafiyar da kasarnan cikin Aminci da gaskiya da kuma rikon amana. Halin da ake ciki na tsanani da kuma tsada da hauhawar farashi, muna fatan Allah ya bashi basirar dawo da Najeriya cikin hayyacinta ta zama kasar da zamu dinga alfahari da ita a ko da yaushe. Muna kuma fatan shugaban a wannan lokacin zai rage nuna bambanci da kabilanci wajen rabon manyan muk**ai musamman wanda suke da maiko sosai.

Muna fatan ya mayar da hankali akan batun rashin tsaro musamman a yankin Arewa Maso yamma da kuma fatara da talauci da ta yi katutu a wannan yankin namu. Muna bukatar ayyukan cigaba da raya kasa ba tare da nuna mana bambanci ko wariya ba. Allah ya taimaki kasarmu Najeriya Amin.

Yasir Ramadan Gwale
26.10.2023

23/08/2023

Mubarak Ibrahim Lawan

Halin ƙunci da talauci da a ke ciki ba zai misaltu ba a cikin kalmomi. Hauhawar farashi sak**akon cire tallafin man fetur ya tabbatar da cewa akwai mugunta ko jahilci cikin cire tallafin nan. A iya fahimtata, yanda a ka shiga ɗimuwa da fagabniya, wallahi babu wani abu da zai dawo da ƙasar kan turba a yanzu in ba dawo da subsidy ba.

Sai dai gaa Musulmi na ƙwarai, akwai hanyar samun sauƙi a cikin kowane irin tsanani! Ƴan uwa, a lazimci abubuwa k**ar haka don samun sauƙi:

1. A bazama neman arziƙi ta duk hanyar halal da ta bayyana a gare ku.

2. A lazimci karatun Al-Ƙur'ani.

3. A lazimci Istigfari

4. A lazimci Salatin Annabi Sallallahu alaihi Wasallam

5. A kuma kaucewa zunubai

Wallahi babu wanda zai mayar da hankali kan waɗannan abubuwan fa ce ya samu nutsuwa da rufin asiri. Ba a rubuta cewa kowa zai yi arziƙi na tarin dukiya ba, amma an rubuta kowa zai ci abinci a rayuwarsa. Bisa ƙa'ida ta Al-Ƙur'ani (ayar ƙarshe ta Suratul Ankabut) cewa wanda duk ya jajirce, Allah zai taimake shi, to in a ka jajirce ɗin, za a ga da kyau, tunda tabbas Allah ba ya saɓa alƙawali.

Ya Allah Ka rufa mana asiri, Ka buɗe mana ƙofofin alkhairi! Ya Allah Ka ba mu ikon tsaya wa a kan ayyukan alkhairi da za su kusanta mu da Kai! Allah Ka yaye mana ƙunci, Ka yi mana arziƙi mara yankewa! Allah Ka tausaya mana, Allah Ka tausaya mana, Allah Ka tausaya mana!Allahumma Amin!

Mubarak!

Daga ,  Mubarak Ibrahim Lawan Halin ƙunci da talauci da a ke ciki ba zai misaltu ba a cikin kalmomi. Hauhawar farashi sa...
23/08/2023

Daga , Mubarak Ibrahim Lawan

Halin ƙunci da talauci da a ke ciki ba zai misaltu ba a cikin kalmomi. Hauhawar farashi sak**akon cire tallafin man fetur ya tabbatar da cewa akwai mugunta ko jahilci cikin cire tallafin nan. A iya fahimtata, yanda a ka shiga ɗimuwa da fagabniya, wallahi babu wani abu da zai dawo da ƙasar kan turba a yanzu in ba dawo da subsidy ba.

Sai dai gaa Musulmi na ƙwarai, akwai hanyar samun sauƙi a cikin kowane irin tsanani! Ƴan uwa, a lazimci abubuwa k**ar haka don samun sauƙi:

1. A bazama neman arziƙi ta duk hanyar halal da ta bayyana a gare ku.

2. A lazimci karatun Al-Ƙur'ani.

3. A lazimci Istigfari

4. A lazimci Salatin Annabi Sallallahu alaihi Wasallam

5. A kuma kaucewa zunubai

Wallahi babu wanda zai mayar da hankali kan waɗannan abubuwan fa ce ya samu nutsuwa da rufin asiri. Ba a rubuta cewa kowa zai yi arziƙi na tarin dukiya ba, amma an rubuta kowa zai ci abinci a rayuwarsa. Bisa ƙa'ida ta Al-Ƙur'ani (ayar ƙarshe ta Suratul Ankabut) cewa wanda duk ya jajirce, Allah zai taimake shi, to in a ka jajirce ɗin, za a ga da kyau, tunda tabbas Allah ba ya saɓa alƙawali.

Ya Allah Ka rufa mana asiri, Ka buɗe mana ƙofofin alkhairi! Ya Allah Ka ba mu ikon tsaya wa a kan ayyukan alkhairi da za su kusanta mu da Kai! Allah Ka yaye mana ƙunci, Ka yi mana arziƙi mara yankewa! Allah Ka tausaya mana, Allah Ka tausaya mana, Allah Ka tausaya mana!Allahumma Amin!

Mubarak!

Ohanaeze Group to EFCC Chair: Step aside from your position, face probe
23/05/2023

Ohanaeze Group to EFCC Chair: Step aside from your position, face probe

The Ohanaeze Youths Group has called on Chairman of the Economic and Financial Crimes Commission (EFCCThe Ohanaeze Youths Group has called on Chairman of the Economic and Financial Crimes Commission (EFCC), AbThe Ohanaeze Youths Group has called on Chairman of the Economic and Financial Crimes Commi...

13/07/2022

Agha Muhammad Al-Afari ,Daya daga cikin tsofaffin masu yiwa masallacin manzon Allah Sallallahu Alaihi wasallam hidima da Kuma makwancin fiyayyen halitta ya rasu yau laraba.

Zaa Yi janaizarsa bayan Sallar Maghriba a Masallacin Manzon Allah Sallallahu Alaihi wasallam

إنا لله وإنا إليه راجعون

Inna lillahi Wainna Ilaihi Raji'un: Asma'u ta rasu a wajen haihuwaMun samu labarin rasuwar Asmau Mustapha Adam, a yau 05...
05/07/2022

Inna lillahi Wainna Ilaihi Raji'un: Asma'u ta rasu a wajen haihuwa

Mun samu labarin rasuwar Asmau Mustapha Adam, a yau 05/7/2022 bayan yi mata tiyata a wajen haihuwa.

Ita da abunda ta haifa duka s**a rasu. Ta rasu ta bar mijinta da diyar ta yar shekara 2.

Asmau Mustafa Adam yard uwa ce ga sananniyar yard jaridar nan ta gidan Rediyan DuetchWelle na Kasar Jamus wato Lateefa Mustafa Jaafar.

Allah ya gafarta mata yasa Aljannah ce makoma

Tsohon Shugaban Kasa Janar Olusegun Obasanjo na tuka Babur din Adaidaita sahu a Birnin Abeokuta inda ya rika daukar fasi...
02/07/2022

Tsohon Shugaban Kasa Janar Olusegun Obasanjo na tuka Babur din Adaidaita sahu a Birnin Abeokuta inda ya rika daukar fasinjoji daga guri zuwa guri ,shugaba Obasanjo yayi Hakan ne a shagalin bikin zagayowar ranar haihuwar sa ta 85

Zuwa Gareku Yan UwanaBello Muhammad SharadaA cikin kwana uku da s**a gabata nayi rubutu akan matsayin da na dauka a kan ...
13/06/2022

Zuwa Gareku Yan Uwana

Bello Muhammad Sharada

A cikin kwana uku da s**a gabata nayi rubutu akan matsayin da na dauka a kan jam'iyyar APC. Ban wuce kwanaki 16 da fita daga cikinta ba. Na dade ina da damuwa a cikin yadda APC take gudanar da gwamnati da mulki a Kano da duk sauran jihohin Najeriya.

Tsakanina da Allah, har zuciyata ban gamsu da mulkin shekara bakwai na shugaba Muhammad Buhari ba. Na san dan adam tara yake bai cika goma ba, amma a tsawon wannan shekaru ban gamsu da Buhari da mataimakinsa da ministocinsa da sauran na kusa da shi kan yadda suke tafiyar da al'umma ba.

Raina ya gama gamsuwa da cewa APC an zabeta domin ta kawo canji da gyara, amma abin damuwa ban samu nutsuwa ko da ta kashi 40 cikin yadda ake tafiyar da al'umma ba. Wallahil azim na yi farin ciki da faduwar Goodluck Jonathan a 2015 duk da ina PDP, saboda a kowane ma'auni gazawarsa ta bayyana. Amma a gaskiya ban yi zaton PMB zai tsinana mana wani abu ba. Na samu karaya ne tun a kwana 100 na farko na Buhari akan mulki.

Magana ta hakika, al'ummar Najeriya sun bawa Buhari amana da babu wani dan siyasar da ya fito daga kudu ko arewa da ya sameta tun daga 1954 har zuwa 2015. A yadda na lissafa a shekarar 2015 da aka rantsar da Buhari a Eagle Square, da ya dora matarsa Aisha Buhari a matsayin Chief of Staff dinsa, ya kuma sanya Yusuf Buhari a matsayin Chief Protocol, a baiwa Sabiu Tunde PA ko rantsuwa nayi ba zan yi kaffara ba, babu mai tankawa. Saboda me? an gamsu da shi. An yarda da shi. An bashi wuka da nama. An yi masa biyayya. An yi masa zaton alheri. An bashi kariya. An yi hakuri da shi. Sannan an yi masa addu'a a gabansa da bayan idonsa har a dakin Ka'aba.

Shekara bakwai da hawan Buhari, saura shekara daya zai sauka, amma kwarjininsa da haibarsa ya kwaranye. Soyayyarsa ta gushe a gurin 'yan amutunsa. Farin jininsa ya tafi. Dokin a ganshi an daina. Maganar da muke yi a yanzu an daina hada fasta da Buhari.

Yau da muke magana a mulkin Buhari jini da ran dan adam ya zama banza da wofi. Ana yi wa mata fyade a kauye. Ana kone gonakai kuma a hana noma. A mulkin Buhari na garkuwa da mata da maza da yara. Ana tare mota a kone ta da fasinjojin da suke cikinta. Ana fashi a jeji. Ana fashi akan t**i. Ana fashi a filin tashi da saukar jirgin sama. Ana fashi a jirgin kasa na gwamnati. A wannan mulkin an yi garkuwa da dan sanda. An yi garkuwa da soja. An yi garkuwa da duk wani jami'in tsaro. Ba wanda ba a kashe ba. An yi garkuwa da 'yan makaranta. Babu wata jiha cikin jihohi 36 na kasar nan har da Abuja da suke zaune lafiya. Ko ina an fito da sojoji, amma ko ina babu tsaro. Hatta a Villa.

Jama'a da kuke bibiyata a wannan shafin ku yi min shaida a yau ko a gobe, a gurina Buhari ya gaza. Buhari ya kasa. Bai yi wata bajinta ba, kuma hukuncin kawai da zan iya yi, shi ne na taimaka da ikon da Allah ya yi min na koya masa hankali da duk wanda saboda wata manufarsa zai bi shi. Zan yaki duk wata ajandar Buhari a kowanne mataki har sai an samu canjin gwamnati ba zarcewar APC ba.

Babu yadda za a yi APC da Buhari sun yi wannan gangancin da sakarcin, wallahi na yi shiru kuma na bi su. Haba !!! An wuce nan, karya ne, muna da rai da lafiya da hankali a raina mana hankali.

Idan na yi haka, na tabbatar da 'yancina, na yi amfani da damata. Na sauke farali na. Nasara kuma akan tafarkin da na dauka na sameta don kuwa na gabatar da uzurina. Ribar kafa kuwa wannan sai mu bar wa Allah. Jama'a ku sani dan takarata Najeriya. Burina Najeriya.

Matashin da ya lashe zaben fidda da Gwani na jamiyyar APC a mazabar Shugaban Majalisar dattijai Ahmad Lawan yaki janyewa...
13/06/2022

Matashin da ya lashe zaben fidda da Gwani na jamiyyar APC a mazabar Shugaban Majalisar dattijai Ahmad Lawan yaki janyewa shugaban Majalisar.

Ahmad Lawan dai ya tsaya takarar futar da Gwani na Shugaban Kasa a ranar 8 ga watan Yuni Inda tsohon Gwamnan Jihar Legas Bola Tinubu yayi Nasara.

Komawar Ahmad Lawan Dan ya karbai kujerarsa matsahin da ya lashe zaben fidda Gwani yayi kemadagas yaki janyewa Ahmad Lawan

Dattawan yankin sun shiga Maganar amma Machina yaki janyewa.

Idan yaki janyewa zaman Ahmad Lawan na tsawon Shekaru 23 a Majalisar kasa zai zo karshe kenan

BARAZANA DA GORIN TINUBUDaga Ibrahim Aliyu AbubakarAbindaTinubu yayi a Ogun, ga Gwamnan su Dapo Abiodun ga Gwamnan Kano ...
12/06/2022

BARAZANA DA GORIN TINUBU

Daga Ibrahim Aliyu Abubakar

AbindaTinubu yayi a Ogun, ga Gwamnan su Dapo Abiodun ga Gwamnan Kano Ganduje ga gwamnan Lagos Babajide sanya Olu ga kuma wasu jiga-jigan APC yayi magana da yarbanci. Yayi abinda zaiyi ya chashe yayiwa mutane gori yayiwa Shugaban Kasa gori yayi barazana ga kasa.

Cewar k**an dole ne ma a bashi wannan takarar, zabin son ransa da yayi na yin magana da yarbanci bayan ga wadanda wasu ke zaune a wurin basu jin yarbanci ya ishi laifi kuma da ache wani dan Arewa ne yayi irin wannan taron yayi magana da Hausa bayan akwai yarbawa da ke zaune cikin Hausawa kai! Ko suna jin hausar kayi magana da Hausa da duk jaridun kasar nan makon abinda gaba daya za'a dinga magana akai kenan ana chachchakar sa.

Akwai baturen nan Moffid yana daya daga cikin wadanda s**a rubuta littattafai kan yakin Basasan Najeriya (Yakin Biafra) yace daya daga cikin hujjar Nzeogwu Kaduna da ya zabi cewa da akayi Kuu (coup d'etat) shi zai kashe Sardauna da kansa, shine wai sardauna ya taba zuwa ingila lokacin suna karbar horo a makarantar sojoji, sardauna ya kai musu ziyara yayi musu magana da hausa saboda haka tun a sannan ya kullace shi. Kuma dukkan su suna jin hausa don me zai je yayi musu magana da hausa irin abinda wadansu suke daukar tsanani a Najeriya kenan.

Amma ache Tinubu yazo yana neman shugaban kasa amma yayiwa mutane magana da yarbanci bayan akwai wadanda basa jin yarbanci awajen. To haka nan barazanar da yayi da gori ya bada gudunmawa sosai a 2015, babbar gudunmawar itace ta yarda ayi wannan maja din (Merger) saboda jam'iyyar buhari baza ta iya kafa shugaban kasa ba. Haka nan jam'iyyar da akayi maja da ita, ko kuma guntayen da s**a hadu. Amma wannan haduwar ta taimaka musu sosai

Haka nan kuma ya kashe kudi ya dauko kwangilar wato (Consultant) kwararru daga Amerika wadanda s**a yiwa Obama Kamfain s**a siyar da shi, bayan ba'a taba tunanin Amurkawa zasu iya zaben bakar fata ba, izuwa shugaban kasar su ba. Amma sai ake alakanta irin kwarewar wadannan kwararrun da s**a tallata shi, shine yasa yaci zabe. Sai Tinubu ya dauko nauyin su da makudan kudade s**a zo s**a tsara yadda za'a yi tallan Buhari a kasar yarbawa musamman ta yadda bayan sun dade ta bata shi, s**a dawo kuma suna gyara shi a jaridun su. Sun dade jaridun su suna bata shi, s**a dawo suna gyara shi akayi zabe, amma ba wannan ne kadai dalilin da yasa akayi wannan nasarar a 2015.

Gwamnoni biyar na PDP da s**a fice s**a kassara ta koda basu karawa APC komai ba sun ragewa PDP wani abu ballantana ma sun kara musu. Saboda abinda ake bukata na lalura na kudi kuma duk inda gwamna yake lalitar jahar tana hannun sa. Suma idan haka ne sai su shigo s**e da ba don su ba, ba za'a yi nasara ba.

Ko kuma ka dauki malamai da s**a dinga hawa kan mambari suna motsa imanin mutane suna cewa a zabi Buhari suma zasu iya gori s**e da ba don su ba har da wannan majar da wannan kwangilar da ya dauko ta Amerika da baza'a ci zaben ba. Ko kuma ka dauki ku 'yan jarida da hadin gwiwar mu da muke muku fashin baki karara zaku dinga yin tambaya kuna saita mai yin fashin baki yadda zai dora mutane akan layin cewa mafi akasari a zabi APC a wannan lokacin. Da mu da ku sai mu hadu muce dabadan mu ba da ba za'ayi nasara ba.

Ba'a son ayiwa mulki barazana, ba'a yiwa shugaba barazana ba'a so ko kadan saboda kada kayi idan kayi gobe ma wani yayi, sai a bude kofa sai shugabanci ya lalace. Amma ya zauna yayiwa mutane barazana.

Yaya za'a yi kazo ka tara mutane kayiwa shugaba barazana yayi kusa yayi k**a da tawaye, domin irin sa Ojukwu yayi lokacin da zai ce sun b***e daga Najeriya ya kirkiri Biafra irin wannan jawabin yayi irin wannan sigar ya bi ga wanda ya sanya ko ya karanta ita fa Tinubu yayi. Kuskure yayi babba.

Kadan kenan daga wani abu da nayi nazari da daga shirin zube ban kwarya na Arewa Radio tare da Dr. Saidu Dukawa .

Ibrahim Aliyu Abubakar©
11 June, 2022

DUK LAIFIN BUHARI NEDaga Bello Muhammad SharadaDazu da rana Sanata Abdullahi Adamu, shugaban jam'iyya na kasa na APC ya ...
06/06/2022

DUK LAIFIN BUHARI NE

Daga Bello Muhammad Sharada

Dazu da rana Sanata Abdullahi Adamu, shugaban jam'iyya na kasa na APC ya bada sanarwar, "Consensus Candidate" wato wanda APC ta amince a zaba a wajen fidda gwani a gobe shi ne shugaban majalisar dattijai Sanata Ahmed Lawan, dan jihar Yobe daga yankin North East.

YAU Litinin kwamitin ayyukan yau da kullum na jam'iyyar APC na kasa wato National Working Committee NWC ya zauna domin zartar da wanda za a mara wa baya a matsayin dan takarar shugabancin Najeriya a APC. A wajen zaman ne Sanata Abdullahi Adamu ya shaida wa membobi cewa ga matsayin shugaban kasa Muhammad Buhari na wanda yake so a tsayar. Nan take kuwa, wasu cikin mahalarta zaman s**a bijire, tare da cewa, bar kowa cikin masu takara tasa ta fidda shi.

AI kuwa a kankanin lokaci da fitar wannan labarin, gwamnoni sha Daya na APC s**a yi watsi da shi. Da gaggawa shugaban kasa Muhammad Buhari ya kira zama da su, ya basu hakuri kuma ya karyata Sanata Abdullahi Adamu. A cewar Garba Shehu, ba yawun PMB a cikin wannan magana.

Shekara bakwai Buhari ya yi yana mulki, saura wata tara a yi zaben barinsa kan gwamnati, amma zakulo wanda zai gaje shi ya faskara. Tun bara ake jagwalgwalo, yanzu ana kadamin da komai ya dagule. Sa'insa ya barke a tsakanin gwamnoni, rashin aminci ya shiga a tsakanin shugaban kasa da mukarabbansa, jam'iyyar APC kullum kwan-gaba, kwan-baya sai kwalo-kwalo, mulkin jama'a ya shiga lahaula kowa sai kuka, kadan ne ke cikin walwala.

Ba kowa ya jawo wannan ba sai Buhari da kansa. A kasar nan, yau abin da aka zabi APC akansa ta gaza yin ko guda daya. Kowane yanki na kasar nan babu tsaro. Cin hanci da rashawa ba abin da aka fasa. Darajar kudinmu ya karye. Farashin kayan masarufi kullum sai dada hawa yake. Mak**ashi ya tsefe. Abinci da taki sun yi tsada. Da harkar lafiya da ilimi duk sun tabarbare. Siyasarma da dimokuradiyya, albarkarsu ta gushe. APCin ta rikice. Shi kansa Buharin ya dimauce, a kowane lokaci yana cikin jirgin sama, yana yawo kasa-kasa. An kasa shawo kan komai.

Idan Buhari ya ci gaba da zura ido, shi da kansa zai rusa kansa kuma ya rusa Najeriya. Ni ina son Najeriya kuma ina fata da shaukin ta koma daidai, amma Wallahi tsarin Buhari, tsarin kawai ne.

EFCC ta cafke tsohon Gwamnan Jahar Zamfara Abdul Aziz Yari sak**akon Zargin Alaka da almundahanar Naira Biliyan 80 da ak...
29/05/2022

EFCC ta cafke tsohon Gwamnan Jahar Zamfara Abdul Aziz Yari sak**akon Zargin Alaka da almundahanar Naira Biliyan 80 da ake Zargin tsohon Babban akanta na kasa Ahmad Idris

Hukumar EFCC ta cafke Babban Akanta Janar sak**akon Zargin Mallakar kudin Haram Naira Biliyan Tamanin
16/05/2022

Hukumar EFCC ta cafke Babban Akanta Janar sak**akon Zargin Mallakar kudin Haram Naira Biliyan Tamanin

2023:Da Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna Da Abba Kabir Yusuf Wa Zaku Zaba a matsayin Gwamnan Jihar Kano
08/05/2022

2023:Da Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna Da Abba Kabir Yusuf Wa Zaku Zaba a matsayin Gwamnan Jihar Kano

Bata Gari Lokacin Buda Baki A Kano: Jama'a A Yi HattaraDaga Yasir Ramadan GwaleJiya wani abokina yake bani labarin abind...
28/04/2022

Bata Gari Lokacin Buda Baki A Kano: Jama'a A Yi Hattara

Daga Yasir Ramadan Gwale

Jiya wani abokina yake bani labarin abinda ya faru da shi mai cike da tashin hankali. Yana tafiya da yamma akan t**in Dorayi, sai aka fara Kiran Sallar Magriba, nan da nan ya samu waje ya tsaya ya bude motarsa ya fita domin ya sayi Kankana don yayi buda baki.

Bayan ya bude mota ya fita, ya dawo bayan ya sayi kankana, da yake yana gaggawaa lokacin da zai fita, bai rufe gilasan motarsa ba, kuma gilasan suna da duhu wato tinted, yana shiga mota, ya tayar da ita zai fara tafiya kenan, kawai sai yaga mutum biyu tare da wani yaro a bayan motar a zaune! Cikin mamaki da firgici yace musu ku kuma fa? Kawai s**a nuna masa bindiga s**a ce ya tuka motar su tafi.

Haka abokin nawa cikin tsoro da firgita ya fara tuka mota. S**a tsorata shi cewar idan ya yi yukurin tsayawa ko yin ihu zasu harbe shi, haka nan yabi umarninsu, s**a ce yabi t**in BUK, haka yabi har s**a zo Gadon kaya, daga nan s**a ce yayi ta tafiya, da yake an yi Kiran Sallah a lokacin kusan tituna duk sun yi fayau babu kowa, kowa ya hanga yana gaggawa yaje yayi Buda baki.

Haka s**a dinga tafiya t**i babu motoci kuma babu mutane. Abokina yace, yana ta fatan Allah yasa su sami wajen da yake da cunkoso dan ya Ankara da mutane, Amma ina haka har s**a zo Hotoro suna ta bin hanya babu motoci sai tsalli tsalli.

Ganin duhu ya fara yi, kuma motoci sun dan fara karuwa a kan hanya, sai s**a sa shi ya dinga bin lunguna da kananan hanyoyi, a haka har sai da s**a kewayo t**in zuwa Wudil.

Bayan da s**a hau kan babban t**i kuma duhu ya fara ga ababen hawa sun fara yawa a hanya, s**a sa ya shiga wani layi a wajen Mariri, nan dai s**a sa ya tsaya, s**a bude motar s**a fita cikin hanzari, suna Gaya masa kada ya kuskura ya waigo su, a haka s**a sulale s**a gudu.

Yace tabbas yana zargin wannan yaron dake tare da su, Sato shi s**a yi, ma'ana suna son yin garkuwa da shi, domin karamin yaro ne sosai. Nan dai s**a gudu basu yi masa komai ba, kuma basu dauki komai a motar ba, alamun cewar su kam bukatarsu ta biya tun da sun dauki yaron da suke da bukata.

Allah ya kubutar da wannan yaro da s**a daukeya bashi aminci. Lallai mutanan shegu ne, sun yi amfani da lokacin da hanyoyi duk s**a zama free, kuma mutane s**a shaga da Buda baki, ta yadda cikin kankanin lokaci zasu je duk inda suke so ba tare da an farga an cimmusu ba. Wannan kuma yana nuna cewar lallai muna cikin barazana musamman iyaye masu yara kanana.

Lallai dole a kula a sanya ido akan yara, musamman a lokacin bukuwan Sallah. Bayanai na nuna cewar akwai yuwuwar miyagun mutane su aikata ayyukan ta'addanci a lokacin bukuwan Sallah, Allah ya kiyaye mu ya kare mu, lallai ayi kaffa kaffa da yara, a kula sannan a lura da duk wasu bakin fuska da ba a gamsu da su ba. Allah ya tsare mu, ya Toni asirin miyagun mutanen nan. Amin.

Yasir Ramadan Gwale
28-04-2023

Hukumar manyan masallatan Makka da Madina ta ce sama da mutane miliyan biyu (2 million) ne s**a halarci sallar dare (tah...
28/04/2022

Hukumar manyan masallatan Makka da Madina ta ce sama da mutane miliyan biyu (2 million) ne s**a halarci sallar dare (tahajjudi) a yau 27 ga Ramadan.

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un 😭😭😭Mun Samu labarin rasuwar Alaramma Muhammad Sani Lawal, ya rasu cikin daren nan a y...
24/04/2022

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un 😭😭😭

Mun Samu labarin rasuwar Alaramma Muhammad Sani Lawal, ya rasu cikin daren nan a yayin da yake jagorantar Sallar Tahajjud cikin Sujada.

Allah muke roko ya jikansa ya gafarta mishi Allahumma Amin 🤲

Shugaban kasar Nijeriya, Alhaji Shehu Usman Aliyu Shagari a wata fita cikin shekarar 1981.Lugude
21/04/2022

Shugaban kasar Nijeriya, Alhaji Shehu Usman Aliyu Shagari a wata fita cikin shekarar 1981.

Lugude

A cikin shekarar 1959, aka bude ginin babbar Kotun Daukaka Kara da ke Kaduna. A nan ana iya ganin Cif Joji Sir Algernon ...
21/04/2022

A cikin shekarar 1959, aka bude ginin babbar Kotun Daukaka Kara da ke Kaduna. A nan ana iya ganin Cif Joji Sir Algernon Brown, tare da Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato kuma Firimiyan Jihar Arewa wajen budewar. Elliott Elisofon yana wurin.:Lugude

Bashir Jantile Ya Bukaci Gwamna Ganduje da ayiwa masu Neman takarar Majalisar Tarayya Gwajin Turanci.Alhaji Bashir Hayat...
19/04/2022

Bashir Jantile Ya Bukaci Gwamna Ganduje da ayiwa masu Neman takarar Majalisar Tarayya Gwajin Turanci.

Alhaji Bashir Hayatu Gentile ya Bukaci Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da ya yiwa masu Neman zuwa Majalisar Kasa a kakar zaben Shekarar 2023 gwajin Turanci.

Bashir Jantile ya ce akwai abun takaici yadda wasu daga cikin Yan Majalisar Kasa da s**a fito daga jihar Kano ke zama Yan daukar jakar takwarorin su na kudancin Najeriya sak**akon rashin iya Turanci.

Yace k**ata yayi Gwamna Ganduje ya samu wasu kwararrun Yan jaridu suyi hirar tsawon awa daya da masu Neman takarar Majalisar ta Kasa a yi musu tambayoyi da Turanci domin gano kwarewar su domin su wakilci Jihar Kano yadda ya k**ata.

Gwamna Ganduje Da Taken Nasara Sai Za Shi GidaDaga Yasir Ramadan GwaleWato maganar gaskiya Moddibo Ganduje ya shammaci '...
18/04/2022

Gwamna Ganduje Da Taken Nasara Sai Za Shi Gida

Daga Yasir Ramadan Gwale

Wato maganar gaskiya Moddibo Ganduje ya shammaci 'yan takara. A cikin weekend ya basu awa is ishirin da hudu su aje aiki? Gaskiya wannan dibar kafa da yawa take, bai bari sun kai Monday ba, b***e su dan gama 'yan cuku cukunsu a office, kawai ya buga musu kararrawar tashi 😅

Akwai ktakkyawan zaton cewar dukkan mutanan da Gwamna ya umarta su aje aiki in suna son yin takara, a cikinsu babu dan takararsa na Gwamna. Na tabbata idan da yana da dan takara a cikin wadan da s**a sauka, da ba zai masa wannan shammatar ba.

'Yan takara duk sun saki jiki cewar an ki karbar resignation din Jan zakara, dan haka suma zasu Mike kafa, su cigaba da wadaka suna warisa a cikin lalitar Gwamnati, ashe ashe basu san cewar Moddibo idonsa biyu akansu ba, kar yake kallon kowa.

Koma dai meye Moddibo yace tsiyar Nasara sai zashi gida. Kun san ai da Nasara ya tashi, yana da ma'aikata da yawa, masu dafa abinci da direbobi da masu shara da masu ban ruwan fulawa da masu gadi da sikiuriti da sauran barori. Da lokacin tafiyar Nasara ya kusa, ma'aikatansa s**ai ta murna zai koma garinsu.

Kan kace kwabo ma'aikatan Nasara sun shiga yin watanda da kayan gidan Nasara. Wani yace ai idan Nasara ya tafi shi zai dau kujeru, wani yace kufunan shayi, wani yace talabijin da radio, wani kuma yace ai mota kaza zai dauka, haka dai s**ai ta rabo tsakanin su, har lokacin tafiyar nasara yayi.

Ma'aikata basu sani ba, ashe Nasara ya sayar da komai na gidansa. Ranar da zai tafi baki s**a cika gidansa, can sai Nasara ya leko yace ina wanda ya sayi kujeru, ace gani nan, sai yace zo ka dauka, haka nan, ina wanda ya sayi mota, Shima yace gani, haka nan, Nasarar ya sayar da komai na gidan, sai ya zama daga shi sai jakarsa ta tafiya. Nan dai Nasara ya bar ma'aikatansa da sallallami. Ashe basu san tsiyar Nasara sai zashi gida ba. Dan haka, a kiyayi tsiyar Moddibo Nasara.

Yasir Ramadan Gwale
18-04-2022

Abba Gida-Gida ya koma NNPP daga PDPƊan takar gwamna a Jihar Kano a Jam'iyar PDP a zaɓen 2019, Abba Kabir Yusuf, ya sauy...
27/03/2022

Abba Gida-Gida ya koma NNPP daga PDP

Ɗan takar gwamna a Jihar Kano a Jam'iyar PDP a zaɓen 2019, Abba Kabir Yusuf, ya sauya sheka daga PDP zuwa NNPP a hukumance.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa Yusuf, wanda a ka fi sani da Abba Gida-Gida, ya sanar da sauya sheƙar ne a yau Lahadi a mazaɓarsa ta Diso, Ƙaramar Hukumar Gwale a Jihar Kano.

A jawabinsa, Yusuf ya ce PDP da APC duk kanwar ja ce, inda ya ce jam'iyar ta ci amanar al'ummar Kano da jagoran ta, tsohon gwamna Rabi'u Musa Kwankwaso duk da irin ɗimbin ƙuri'ar da su ka kaɗa mata a zaɓen 2019.

A cewar sa, matakin sauya sheƙar ya zamto mai muhimmanci duba da irin kiraye-kirayen da miliyoyin al'umma su ke yi na ya sauya jam'iyyar NNPP, wacce ta ke da manufofi na gaskiya na tserar da ƴan ƙasa da ga mawuyacin halin da su ke ciki.

Daily Nigerian Hausa ta fahimci cewa sauya sheƙar ta Abba Gida-Gida ta zamto sharar hanya ga Kwankwaso, wanda a ke tsammanin shima a ranar 30 ga watan Maris zai fice daga PDP zuwa jam'iyar NNPP, inda da ga nan zai tsaya takarar shugaban ƙasa.

Gangaran Kafi Gwani: Alaramman daya rubuta al-Qur'ani sama da dari (100)Gangaran Mallam Abdu dan Gwani Sulaimanu. Asalin...
26/03/2022

Gangaran Kafi Gwani: Alaramman daya rubuta al-Qur'ani sama da dari (100)

Gangaran Mallam Abdu dan Gwani Sulaimanu. Asalin mahaifinsa mutumin kasar Katsina ne, Amma a yanzu yana zaune a wani gari da ake cewa Mallam Bukarti, a gabas da garin Nguru ta jihar Yobe.
Ya haddace qur'ani da tilawarsa tun sama da shekaru Hamsin (50) da s**a wuce. Ya rubuta al-Qur'ani sama da guda dari (100) da hannunsa.
A cikin 'ya'yansa akwai Gwanayen al-Qur'ani da mahardata birjik.
Allah ya karawa Gangaran Audu lafiya.

Source: Ashiru M Al-Qasim Assufy

JAM'IYYAR APC: NEMAN MULKI DA RASHIN KWAREWADaga Kwamared  Mallam  Usman Bin-Affan A cikin kasa da awanni 72, Shugaba Bu...
25/03/2022

JAM'IYYAR APC: NEMAN MULKI DA RASHIN KWAREWA

Daga Kwamared Mallam Usman Bin-Affan

A cikin kasa da awanni 72, Shugaba Buhari da Jam'iyarsa ta APC sun gudanar da zama (ciki har da na gaggawa) akalla sau uku. Wannan ba don komai ba, sai don kokarinsu na magance barakar dake kokarin kunnowa lokacin babban taron Jam'iyar ko bayan taron da za'ayi gobe Asabar.

Irin wannan karfi da jam'iyar APC dama Shugaban Kasa ke sakawa saboda nasarar wannan taro, bamu taba kallon sun kwatanta shi kan wani al-amari da ya shafi Talakan Najeriya ba, a cikin shekarun da s**ayi suna mulkin Kasarnan.

Alal misali, a halin yanzu Kungiyar Malaman Jami'o'i ta Kasa (ASUU) na cikin mako na shida cikin yajin aiki. Har yau bamu ji Ministan Ilmi ko Shugaban Kasa ya kira wani taron gaggawa don samo maslaha akai ba. Ko yajin aikin ASUU bashi da muhimmanci ne da ya k**ata a saka karfi don magance sa?

Hakazalika a wani bangaren, Karanci da Tsadar Man Fetur har Abuja bai bari ba, b***e sauran garuruwa, musamman a makonnin nan da s**a shude, amma mun kasa jin wani taron gaggawa da Shugaban Kasa ya kira don tunkarar matsalar da nufin magance ta. Wannan a hakanma shine Babban Ministan Man Fetur.

Akwai matsaloli da dama da muka shiga a Kasarnan, da a wani lokaci sai ka rasa gane cewa anya ma akwai masu mulki a kasarnan, saboda irin halin ko in kula daga bangaren Shugabanninta.

Duk tsanani da Talakawa ke ciki, ban taba ji jam'iyar APC a matsayinta na mai mulki tayi wani zama a bangarenta ba, domin ta nuna kulawa da halin da Talakawan da s**a zabe ta ke ciki ba. Kullum abinda s**a kware wajen iya fada shine, jam'iyar PDP ne ta jefa Talakawa cikin halin. To wa ya sani ko mun zabi APC ne saboda suyi ta fada mana abinda PDP tayi, da yasa muka koreta a mulki, su Kuma APC muka zabe su? Na tabbata mun zabi APC ne saboda warware mana jagwalgwalon PDP, amma da alamu sun gaza, domin har ta kai Talakawa na maraba da dawowar PDP yanzu.

Kamar yadda muke fada a kullum, ita Jam'iyar APC bata da burin da ya wuce na son tayi mulki, koda kuwa bata da kwarewar iya gudanar dashi. Hakika a cikinta akwai nagartattu kalilan, amma gari-ba-amfanin cikinsu, sun rinjaye su.

Zabi dai ya ragewa Talakawa idan ALLAH ya kaimu shekara mai zuwa. Nidai tuni na yiwa kaina zabi bisa abinda na fahimta da kuma kyakyawar fatana ga Kasarnan.

Usman
Tsohon Magoyin Bayan Jam'iyar APC.

Da Dumi Dumi:Kotu Ta Bayar da Umarnin a Sake Kame DansarauniyaKotu Mai Lamba 58 dake Kano ta bayar da Umarnin sake Kame ...
14/03/2022

Da Dumi Dumi:Kotu Ta Bayar da Umarnin a Sake Kame Dansarauniya

Kotu Mai Lamba 58 dake Kano ta bayar da Umarnin sake Kame Muazu Magaji Dansarauniya.

Kotun ta kuma bawa wadanda s**a tsaya masa da su bayyana a gabanta ranar 28 ga watan Maris da muke ciki

R U Ɗ A Ɗ Ɗ I Y A R  A L 'U M M A   1/2Sunanka Allah za na sa farkon batuKa tsareni faɗawa kadarkon zamaniSannan salati ...
10/03/2022

R U Ɗ A Ɗ Ɗ I Y A R
A L 'U M M A 1/2

Sunanka Allah za na sa farkon batu
Ka tsareni faɗawa kadarkon zamani

Sannan salati gun mafi kyawun batu
Cetonka ran ma'ashar kayi mini lamuni

Wata Al'umma ni kanta yau zan himmatu
Fatana nake na fitar da ƙaumu a razani

Ita Al'umma ce malama a fagen sani
Amma a aiki na gwada ta da jahili

Ruɗunta ya kai bata girmama mai sani
B***e a ce a wajenta ga wani kamili

Kowa cikin Ummar ga komai ya sani
Mai arziƙi a cikinta shi ne adali

Ba shugaba a cikinta babu matsawaci
Ba babba ba yaro bare a faɗi a ji

In mas'ala tazo taho kaji shirbici
Cece-kuce da kace-nace shi za kaji

Ga shugabanni nan ciki da maƙetaci
Bai tausayin mabiya bare yayi agaji

In yayi umarni biyayya bata yi
Dan ya yi ƙarya gunta tafi dubu ɗari

In malami, masani ciki ya cane a yi
Sai jahilai su fito su ce 'kaji almiri'

'Ba malamin fada bane ba manauyayi?
Wallahi ƙaryar wane tafi ta kafiri'

Wancan yace Shi'a yake wancan yace-
Ai ɗan Izala ne marar son Sayyadi

Wasu ko su ce ai ɗan Ɗarika wance ce
Wa za ya ɗau zancen marar kyan tanadi

Wannan irin lamari da bulƙarar ta ce
Haka zata ƙare rayuwa da tanaƙudi?

In lokacin zaɓe ya zo ku tsaya ku ji
Nan yan siyasa za su sa ta a yamutsi

Wancan ya ce canji mafarar agaji
Wancan yace 'yanci maƙarar Mattsatsi

Kafin ka ce uffan fa sai kaga ta gaji
Kowa ta samu sai ta yi masa warwatsi

Ƙuri'a ta sawa kare; ta sawa mahaukaci
Ta sakawa jemage; ta sawa mahandami

Wataran a ruɗewa ta sawa maƙetaci
Mugu marar tausai baƙin algungumi

Ƙarshe ya zo ya saka ta kogin firgici
Tsoro da babu da razani gagarimi

Wannan kaɗan a cikin irin ruɗunta ne
Ka biyo ni Mamman, zana kaika a sauƙaƙe

Zan kaika can kaji rayuwar 'ya'yanta ne
Da sarakunanta da tajiranta dake maƙe

Ruɗaɗɗiya ce in ka ganta a razane
Ta haukace ta yamutse ta raƙƙaƙe

Zan ci gaba insha Allahu

©Nasir Ahmad Sadiq
(Mamman Naso)
23-05-2020

Address

Suite No. 5 Eastern Bye Pass, Adjacent Majiya Filling Station
Station
700223

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Turakar Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share


Other News & Media Websites in Station

Show All