Mu'asasatu Aliyul Akbar.

Mu'asasatu Aliyul Akbar. Shafin Mu'asasatu Sayyid Aliyul Akbar (As)

MUJI WANNAN DA KYAU MATASA...Bisa dabi'a ko'ina ne matasa sune s**afi yawa kuma sune suke a shekarun fafatawa. Domin hak...
16/06/2024

MUJI WANNAN DA KYAU MATASA...

Bisa dabi'a ko'ina ne matasa sune s**afi yawa kuma sune suke a shekarun fafatawa. Domin haka idan matasa basuyi abinda yak**ataba toh babu wani fata, don duk lokacinda wasu s**a so gurbata matasa sune suke hari musamman 'yan mata ansan sune fata ansan in aka lalatasu toh shikenan komai ya lalace.

-Cikin jawabin sheikh zakzaky wajan rufe mu'utamar na matasa a shekarar 2013.

Yau Juma'a 7 ga Zulhijja 1445 Gobe Asabar 8 ga wata ne, ranar Lahadi shi ne 9 ga watan Zulhijja 1445 a Nijeriya, bisa ta...
14/06/2024

Yau Juma'a 7 ga Zulhijja 1445
Gobe Asabar 8 ga wata ne, ranar Lahadi shi ne 9 ga watan Zulhijja 1445 a Nijeriya, bisa tabbacin cewa ba a ga wata ranar Alhamis 29 ga Zulka'ada ba, don haka tunda ba a ga wata a rannan ba, Juma'a 30 ga wata ne, Asabar ne 1 ga wata. Kenan ranar Lahadin jibi 9 ga wata ne, kuma rannan ne ranar Arfa a wajenmu.

Abin nufi da ranar Arfa a wajenmu shi ne, ranar ne mutum zai yi Azumin ranar Arfa mai falala idan yana da nufi da halin yi. Sannan kuma rannan ne mutum zai yi addu'oi da aka ruwaito da ayyukan Ma'asurai na yinin Arfa.

Ranar Litini, shi zai zama ranar Idin Layya. A rannan ne wanda Allah Ya h**e ma abin Layya, kuma ya kudiri aniyar yin wannan sadaukarwa mai dimbin lada, zai gabatar.
Ranar Arfa a wajen mutum shi ne ranar 9 ga watan Zulhijja a inda yake. Kuma ba dole ne sai Arfa din Nijeriya ya dace da na Saudiyya ba, k**ar yadda ba dole sai ranar Ashura a Iraqi ya dace da ranar a Nigeria ba, in sun dace shikenan, in ba su dace ba, mutum na daukan lissafin inda yake ne a bisa tabbaci ya yi aiki da shi.
Ko sanarwar mahukuntan Nijeriya, akan watan Zulhijja ba su dogara da cewa an ga wata a wani yanki a Nijeriya ko wata kasa da suke Ufuqi guda da Nijeriya ba, sun dogara ne da Saudiyya ta sanar da cewa ranar Asabar ne Arfa. Wannan kuma a wajenmu sam ba hujja ba ne a shari'a.
Allah Ya karbi ibadunmu. Ya yafe gazawarmu bakidaya.

13/06/2024

Manzon Allah (S) yace "mutum daya ya shiriya ta sanadinka yafi ka yi kyautar jajayen Rakuma dubu saba'in.

MANUFAR DA'AWAR SHEIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H).Da'awar Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) wani yunkuri ne na sauke hakkin Allah Ta...
13/06/2024

MANUFAR DA'AWAR SHEIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H).

Da'awar Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) wani yunkuri ne na sauke hakkin Allah Ta'ala, ta hanyar biyayya ga umarninsa da hanuwa ga hane-henensa, da kuma kokarin kawo gyara a cikin al'umma don a gudu tare a tsira tare gobe kiyama.

Al'umma ta yi nisa cikin dimuwa da rashin sanin hakkokin Allah a kanta, an ajiye umarnin Allah a gefe ana ta rayuwa cikin son zuciya da makanta, wannan ya jaza dimbin matsaloli a tafarkin rayuwar al'umma, k**a daga munanan dabi'u da halaye, keta da fin karfi, zalunci da danniya, jahilci da makanta, rashin sanin addini da rashin sanin alkibla, da kuma uwa uba fuskantar mummunar makoma a gobe kiyama wa'iyazubillah.

Wannan ya sa Sheikh Zakzaky (H) ya tashi don kiran mutane zuwa ga addini wanda a cikinsa ne kawai mafitarsu ta ke, a cikinsa ne kawai al'umma za su samu duk abin da suke nema na kwanciyar hankali, yalwar arziki, tarbiyya da kuma kyakkyawar makoma a gobe kiyama. Dan haka manufar Da'awar Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ita ce dora mutane akan koyarwar addinin musulunci da kyautata hali da dabi'unsu.

A jumlace kuma a dunkule, manufar Da'awar Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) shi ne kawo gyara don kyautata rayuwar al'umma, da kuma neman uzuri da tsira gaba ga Allah a ranar alkiyama.

~Ahmad Assaminaky

ZHUL QA'DAH BAI YI NUƘUSAN BA!بِسْمِ اللَّـهِ الرَّحْمَـٰنِ الرَّحِيمِ اللهم صل على محمد وعلى آل محمدDaga: Ofishin Sayyi...
10/06/2024

ZHUL QA'DAH BAI YI NUƘUSAN BA!

بِسْمِ اللَّـهِ الرَّحْمَـٰنِ الرَّحِيمِ

اللهم صل على محمد وعلى آل محمد

Daga: Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Saboda ayyanawar da Ƙasar Saudiyya ta yi na cewa ranar Asabat mai zuwa ita ce ranar Arfa, to, k**ar yadda ya faru bara, muna ta samun saƙonni na tambayar yaushe ne ranar Layya?

Mafi yawan kalandodi sun ƙiyasta ranar Lahadi ne a matsayin 10 ga watan Zhul Hijjah 1445. Irin wannan ma'auni a kan riƙa amfani da shi a ayyukan yau da kullum, amma don ayyukan ibadodi, k**ar fara azumin watan Ramadan da Sallah Ƙarama (Idil Fitir) da Layya, dole sai an ga jaririn wata ranar 29, ko kuma a cika watan kwana 30.

A ranar Alhamis ɗin da ta gabata mun sa an duba wata a kusan ko'ina a faɗin ƙasar nan, amma labarin da muka samu shi ne: ba a ga wata ba. Don haka ne ma muka bayar da sanarwa ranar Juma'a ceawa watan Zhul Qa'adah ya cika kwana talatin (30) cur.

Saboda haka a bisa yaƙini ba ƙiyasi ba ranar Litinin mai zuwa ita ce ranar Layya. Ƴan'uwa suna iya halartar idi ranar Lahadi tare da sauran mutane, amma idan su a karan kansu ne za su yi idin, to, sai ran Litinin. Yanka kuwa tilas sai ranar Litinin.

Za mu iya canza wannan matsayi idan muka sami tabbacin ganin jinjirin watan Zhul Hijjah a ranar Alhamis da ta gabata. In ba haka ba kuwa matsayin namu na nan daram.

Kada a manta da ayyukan kwanuka goma na farkon wannan wata mai alfarma. Waɗannan ayyuka sun haɗa da azumi, salloli da addu'o'i. Har wa yau kuma a kiyaye ladubban layya don tunawa da sadaukarwar Annabi Ibrahim (AS).

تقبل الله منا ومنكم صالح الأعمال.

Wassalam




03/ZulHijja/1445
10/06/2024

YUNKURIN SAYYID ZAKZAKY  WAJEN HADA KAN AL’UMMAR MUSULMI!Hada kan al’ummar Musulmi na wannan nahiya da muke ciki, da ma ...
06/06/2024

YUNKURIN SAYYID ZAKZAKY WAJEN HADA KAN AL’UMMAR MUSULMI!

Hada kan al’ummar Musulmi na wannan nahiya da muke ciki, da ma sauran duniya baki daya, yana daya daga cikin abubuwan da Sayyid Zakzaky (H) yake karfafawa da kuma kwadaitarwa a kai. Duk wanda yake cikin wannan da’awa zai tabbatar da haka.

Duk wani abin da zai kawo rarraba tsakankanin Musulmi, Sayyid Zakzaky (H) yakan kyamaci abin, yakan kuma yi kashedi a kan haka. Abin da kuma zai karfafa hadin kan Musulmi, yakan tsayu da shi. Akwai misalai da dama na abubuwa da Sayyid Zakzaky (H) ya yi a aikace, ya kuma tarbiyantar da ’yan uwa a kai, na ganin cewa al’ummar Musulmi sun samu ha]in kai a tsakaninsu, ga wasu daga ciki!

Kai wa Malamai na wasu kungiyoyi ziyara. Rashin fitar da Musulmi cikin Musulunci, wato kafirta su. Gina ’yan uwa a kan yin Salla a masallatai na Musulmi, ba tare da bambancewa ba. Wato na a ce sai ’yan masallacin kaza mutum zai yi Salla, Gina ’yan'uwa a kan yi wa Musulunci hidima ta fuskoki daban-daban ba tare da bambancewa ba, Wato na cewa suna tare da mu, ko ba su tare da mu. Misali wasu ayyuka na ’yan Medical Team, Aikin gayya da Hurras suke yi na gyaran makabarta da dai sauran ayyuka ga Musulmi baki daya,Yin taron Makon Hadin Kai, wato wanda ake yi a watan Maulidi wanda a kan gayyato Malamai, wadanda suke a kan fahimta daban-daban domin gabatar da jawabai da nufin samun kusanci da juna da kuma fahimtar juna da dai sauran hanyoyi da Sayyid Zakzaky (H) ya gina ’yan uwa a kai, domin hadin kan al’ummar Musulmi da ke wannan nahiyar.

Wannan baki daya a tadaice, dangane da darussa ne daga rayuwar Sayyid Zakzaky (H) sai dai kafin kullewa da godiya ga Allah (T) da kuma addu’a ga Sayyid Zakzaky (H). Wasu nasihohi guda biyar wadanda Sayyid (H) yana yawan magana a kansu a jawabansa.

Istik**a da kuma sabati a wannan tafiya ta gwagwarmaya, har ya zuwa saukar ajalin mutum. Wato ko mutum ya mutu yana kan tafarkin, ko kuma a kashe shi a kan tafarkin.

Dauriya a kan jarabawoyi da kuma fitinoni da suke gudana na cikin gida da na waje. Wato cikin gwagwarmayar da kuma wajenta. Domin wadannan jarabawowi da fitinoni in mutum ya daure masu hanya ce ta samun lada gare shi. Kuma Aljanna sak**ako ne na dauriya.

Iltizami da addini, wato mutum ya ga cewa ya siffatu da addini a zantukansa, dabi’unsa da kuma ayyukansa. Wato dai ya kasance alami na addini. In an gan shi an ga addini, in an ji shi a ji addini, in an yi mu’amala da shi a ga addini. To idan mutum ya samu wannan, ko da Allah (T) bai raye shi ba ya ga tabbatar addini, to ya samu babbar nasara.

Ba da gudummawa a wannan Harka ta gwagwarmaya, wato kowannenmu dan uwa ne ko ’yar uwa ya duba ya ga wace gudummawa zai bayar. Kuma ya tsayu da ba da wannan gudummawa har zuwa komawarsa ga Allah (T). Kuma Alhamdulillah a cikin wannan gwagwarmaya ga sashe na ayyuka nan daban-daban. To mutum ya duba ta wane sashe ne shi zai dinga ba da gudummawa. Domin k**ar yadda aka sani daidai gudummawar da kowa ya bayar, daidai sak**akon da zai samu gobe kiyama.

Ikhlasi:- Wato ya kasance kowannenmu duk abubuwan da zai yi, ya yi su ne saboda Allah (T) da kuma neman yardarsa. Misali wannan iltizami da addini, da ba da gudummawarsa a tafarkin, da kuma dakewa a tafarkin, duk su kasance a kan asasin ikhlasi ne, ba akasin iklasi ba. Domin shi ikhlasi shi ne ruhin ayyuka.

Daga karshe muna godiya ga Allah (T) da wannan baiwa da kyauta a wannan nahiyar da muke ciki. Kuma muna kara godiya ga Allah (T) da ya yi wannan baiwa da kyauta a zamaninmu. Kuma muna kara godiya ga Allah (T) da ya azurta mu da amsar wannan baiwa da kyauta da baiwa da ya ba mu. Addu’armu ga Sayyid Zakzaky (H), Allah (T) ya saka masa da alheri, ya dada kare shi, ya dada ba shi lafiya, ya kuma dada masa yawancin kwana, ya kuma dada masa darajoji. Elaheey ajib.

MATAKIN DA A KE DAUKA A KAN WAWAYEN MUTANEA yau sahar facebook da sauran shafukan sada zumunta, sun cika da wawaye da ke...
02/06/2024

MATAKIN DA A KE DAUKA A KAN WAWAYEN MUTANE

A yau sahar facebook da sauran shafukan sada zumunta, sun cika da wawaye da ke wahalar da wadanda basu san yadda ake mu'amala da su ba. Na jima da yin wani rubutu akan yadda ake mu'amala da "wawa" mara tarbiyya wanda bai iya magana ba. Yanzun ma dai zan so na kara ankarar da 'Yan Uwa ma'abota wulaya masu hadafi a rayuwa. Da farko akwai bukatar mutum ya san waye wawa kafin sanin yadda zai magance zama dashi. Malamai masana sun yi bahsi akan wannan maudu'i mai muhimmancin gaske.

Sheikh Hussein Najad (H) ya yi ta'arifin wawa da cewa:
ﺍﻟﺴﻔﻴﻪ ﻃﻮﻳﻞ ﺍﻟﻠﺴﺎﻥ، ﺳﻲﺀ ﺍﻟﻜﻼﻡ، ﻗﺒﻴﺢ ﺍﻟﺠﻮﺍﺏ ﻟﻢ ﻳﺄﺧﺬ ﻧﺼﻴﺒﻪ ﻣﻦ ﺍﻟﺘﺮﺑﻴﺔ ﻓﻲ ﺑﻴﺖ ﺃﺑﻴﻪ ﺃﻭ ﻓﻲ ﻣﺪﺭﺳﺘﻪ ﺃﻭ ﻓﻲ ﻣﺠﺘﻤﻌﻪ، ﺃﻭ ﺇﻧﻪ ﻟﻤﺎ ﻳﻔﻬﻢ ﻣﻌﻨﻰ ﺍﻟﺤﻴﺎﺓ ﺑﻌﺪ، ﻭﻟﺬﻟﻚ ﻓﻬﻮ ﻻ ﻳﻌﺮﻑ ﻛﻴﻒ ﻳﺘﻌﺎﻣﻞ ﻣﻊ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻟﺠﻬﻠﻪ
Ma'ana:
Wawa Shine Mutum mai yawan magana, mai maganganun banza, dake bada mummunan amsa. Shi wawa baya daukar nasiha daga tarbiyyar Mahaifi ko makarantar, ko kuma cikin al'ummar da yake rayuwa dasu. Haka yake bai san ma'anar rayuwa ba, saboda haka ne ma bai san yadda zai dunga mu'amala da mutane ba sak**akon tsabar jahilcin sa. Daga nan idan ka fahimci cewa a cikin abokanka akwai mutum mai irin wannan siffar to ka iya gane cewa shi "wawa" ne don haka sai masana s**a ci gaba da bada shawarar yadda za'a magance cutarwar sa.

Sheikh Abu Gaffar cewa ya yi:
ﻓﺈﺫﺍ ﺍﺑﺘﻠﻴﺖ ﺑﺴﻔﻴﻪ، ﻓﺄﻓﻀﻞ ﻭﺳﻴﻠﺔ ﻟﻠﺘﻌﺎﻣﻞ ﻣﻌﻪ ﻫﻲ ﺗﺠﺎﻫﻠﻪ ﻭﻋﺪﻡ ﺍﻟﺮﺩ ﻋﻠﻴﻪ، ﻓﻼ ﺗﻀﺮﻙ ﺃﺫﻳﺘﻪ، ﺑﻞ ﺍﻷﻓﻀﻞ ﺃﻻ ﺗﻠﻘﻲ ﻟﻪ ﺑﺎﻻً ﺣﺘﻰ ﻻ ﺗﺸﻐﻠﻚ ﻛﻠﻤﺎﺗﻪ
Ma'ana:
Idan aka jarabce ka da wawa, hanya mafi kyau wajan mu'amala itace kada ka tanka shi, sannan kada ka dunga bashi amsa, ba zaka taba cutuwa daga cutarwar sa ba, haka kuma mafi alkhairi kar ka bashi dama domin kada ka shagaltu da zantukan sa.

Malam Shafi'i kuwa da ya tashi bada tashi shawarar cewa ya yi:
ﺍﺫﺍ ﻧﻄﻖ ﺍﻟﺴﻔﻴﻪ ﻓﻼ ﺗﺠﺒﻪ
ﻓﺨﻴﺮ ﻣﻦ ﺇﺟﺎﺑﺘﻪ ﺍﻟﺴﻜﻮﺕ
ﻓﺈﻥ ﺃﺟﺒﺘﻪ ﻓﺮّﺟﺖ ﻋﻨﻪ
ﻭﺇﻥ ﺗﺮﻛﺘﻪ ﻛَﻤَﺪﺍً ﻳﻤﻮﺕ
Ma'ana:
Idan wawa na maka magana da bakaken maganganu da sharri Da kage kala kala.. to Kada ka amsa shi mafi alkhairin amsa shine kayi masa shiru. Saboda idan ka amsa shi zaka farranta masa rai..
Amma idan kayi watsi dashi zaiji k**ar ya mutu...

Ustaz Gurban Zade ya kawo tashi shawarar da yake cewa:
ﻳﺨﺎﻃﺒﻨﻲ ﺍﻟﺴﻔﻴﻪ ﺑﻜﻞ ﻗﺒﺢ
ﻓﺄﻛﺮﻩ ﺃﻥ ﺃﻛﻮﻥ ﻟﻪ ﻣﺠﻴﺒﺎ
ﻳﺰﻳﺪ ﺳﻔﺎﻫﺔ ﻓﺄﺯﻳﺪ ﺣﻠﻤﺎ
Ma'ana:
Wawa na mani magana da munanan maganganu marasa kan gado na sharri. Sai naki yarda na zamo mai amsa shi. Ma'ana naki yarda na zamo wawa irinsa... Wawancinsa na karuwa,
ni kuma hakuri na karuwar mani. Ina ganin a takaice wannan zai taimakawa dan uwa mai hadafi kuma mai mutunci samun saukin magance dukkanin shirman wawaye masu neman suna ta hanyar zagi ko cin mutunci ko sharri da hassada.

Kada ku manta wawa bashi da hadafi ba shi da samfur a rayuwa shi ne ke iya zagin kowa domin bashi da wanda za'a taba masa a rayuwa ya ji zafi, kuma wawa mutum ne marar anfani mai yawan hassada da maganganun sharri mai takurarren tunani da matsalar kwakwalwa da rashin fahimta... Ya shigo sahar yanar gizo ne don ya nemi suna ta hanyar tsokano mutane masu mutunci da s**a san girman masu girma. Saboda haka ana bukatar kowanne irin shugaba ko jagora yasan yadda zai yi mu'amala da wawayen da s**a yi masa yawa a rayuwa musamman mabiyansa ko kuma abokan adawarsa... Shugaba ya zama mai kame bakinsa daga yawan sa-in-sa ko jayayya... Ya yi shiru a inda yake da karfin ramawa ya daina yawan bata lokacinsa wajen yin musu da wawaye... Yin shiru shine dattako da nuna gogewa bisa jagoranci... Allah ya kara kare mu daga sharrin Fasiqai marasa hadafi a rayuwa da kuma wawayen cikin mu, amin ya Allah.

31/05/2024

Ko tsawon shekara nawa za kayi a raye, a kwai wanda ba za su taba sanya hoton ka ko ambatar sunan ka ba, har sai ranar da ka Mutu.

"Qarfin mu, ba shine yawan mutane mabiya ba, Qarfin mu shine danfaruwar mu da Allah Ta'ala".— _Shaikh Ibarahim Zakzaky a...
29/05/2024

"Qarfin mu, ba shine yawan mutane mabiya ba, Qarfin mu shine danfaruwar mu da Allah Ta'ala".
— _Shaikh Ibarahim Zakzaky a jawabin Fitina Tawayiyya._

MAS'ALA AKAN YIWA SHUGABANNI BIYAYYASHIN WADANNE SHUGABANNI ALLAH YACE AYIWA BIYAYYA?A lokuta da yawa al'ummar mu, musam...
28/05/2024

MAS'ALA AKAN YIWA SHUGABANNI BIYAYYA

SHIN WADANNE SHUGABANNI ALLAH YACE AYIWA BIYAYYA?

A lokuta da yawa al'ummar mu, musamman wadansu daga yan arewa, kai a wasu lokutan ma harda wasu yan tsirarin maluma zakaji nacewa abi shuwaganni, Allah yace abi shuwagabani. Tambaya shin wadanne shuwagabanin Allah ya ce mubi?

Wannan Abu shine Wanda har yau akasarin al'umma s**a jahilta. Abin yana kara ta'azzara ta yadda ko da yaushe wasu daga maluma ke kambama, abi shuwagabanin fiye da kaji sunce ayi biyayya ga Allah. A addinin musulunci biyayya ga shuga wajibine, domin umarnin Allah ne, madamar yana biyayya ga Allah da manzan sa (sawa).

Abin da al'umma ya k**ata su sani, Wanda akasari s**a jahilta, ana bin shuwaganine, akan duk wani Abu da bai saba da dokokin Allah ba, bugu da kari ba'a biyayya ga shugaba a duk lokacin da ta tabbata ya bijirewa umarnin Allah (T) koda ko da juya masa baya danuna fushi ta hanyar da sharia ta nuna a nuna masa kuskuransa, idan ko zaiyu a gayamasa ya sauya to wajibi a fito a gayamasa, wala kuwa ko wanne Irin shugabane, Domin biyayya ga Allah (T) ita ce biyayya sama da dukkan wata biyayya.

Amman kuskurene, al'umma suga shuwagabanin sun taka dokar Allah ko wanne Irin shugabane, ace abishi akai, da kuma anyi magana ace ai shugabane, Allah yace abi shi, SHIN DAMA HAKA ALLAH YACE KU BI SHUWAGABANNI A DUK IRIN UMARNIN DA S**A BAKU KADA KU SABA MUSU?.

Hatta hasalima me maluma s**ace, babu biyayya ga abin halitta abisa sabawa Allah, madamar ba tursasaka akayiba, kai hasalima akwai malaman da ke ganin cewar tsaya war kyam a wajan bin Allah shi yafi ko da ko za karasa ranka, domin biyayya ga Allah itace biyayya fiye da ko wacce Irin biyayya.

Sabo da haka babu laifi mu bi shuwagabanin ko dokokin kasa madamar basuci karo da addinin mu, idan harko sunyi karo to wajibi a yi watsi da wannan dokokin, Sabo da haka a duk lokacin da Allah da manzan sa s**ace ayi, sai wani shugaba yace a'a ga yadda za'ayi sabanin yadda Allah yace ayi, to madamar kabishi to ka tabbata kayi wa Allah kishiya wannan shugaban yazamo shine ubangijinka, madamar ba tursasaka akayiba.

Ya k**ata al'umma su fahimci wannan biyayya da Allah yace ayi ga shuwagabanin sune shuwaganin da suke umarni da kyak_kyawan aiki da hani, shuwagabanin da suke biyayya ga Allah. A Irin wannan lokaci namu da muka tsinci kan mu na mulkin turawa a yau sai abin da s**a zarar a majalisar dinki duniya, dama dokokin kasa ba laifi bane, biyayya da dokokin da ba su saba da addini ba, idan harko sun saba, biyayya ga Allah da manzan sa sune wajibi ga duk wani MUSULMI.

Sabo da haka al'umma su fahimta, biyayya ga shuwagabani ana binsune a duk kan wani Abu da baisaba da yiwa Allah da manzan sa tawayeba.

Ni Muhammad Ibrahim Zakzaky!Nine Dan Sheikh Ibrahim Zakzaky daya  tilo Namiji daya Rage Cikin Mu  Bakwai, Sai Mata Guda ...
25/05/2024

Ni Muhammad Ibrahim Zakzaky!

Nine Dan Sheikh Ibrahim Zakzaky daya tilo Namiji daya Rage Cikin Mu Bakwai, Sai Mata Guda Biyu Suhaila Da Nusaiba, Yan uwa Nane Sojojin Nigeria S**a Kashesu Su Shida Kanneina Ne Sojojin Nigeria s**a K**a da Ransu S**a Azabtar dasu da Wuta da Yankawa da Wuqa Da Kakkaryawa Kafin Su Sanya Bindiga Su Harbesu Ahmad Hameed da Mahmoud , Yan uwa nane Sojojin Nigeria S**a Harbe aGaban Mahaifana S**a Tarwatsa Kwakwalwar Hammad S**a Harbi Kanina Humaid A Hanci S**a Tarwatsa Kansa S**ayiwa Kanina Hydar Ruwan wuta ajikinsa, Dukkansu Sunyi Shahada Ne Domin Kare Rayuwar Babana Da Sojojin Nigeria s**axo Kashewa! Nine Dan Malam Zakzaky Wanda Akayiwa Ruwa Wuta ajikinsa Nine Dan Malama Zeenatu Wadda Harsashi Marasa Adadi s**a Sauka A jikinta Domin Kare Mijinta Babana ,Nine Dan Wanda Aka Konawa yayarsa Gwaggo Fatima Da Ranta sojoji S**a Banka Mata Wuta S**a Hanata ta zo ta gana da Dan uwanta wato Babana, Nine Dan Wanda Aka kashewa Almajirai Sama 1000+ Nine Dan Wanda Aka Qona Almajiran Babana da Ransu Har s**a Mutu, Nine Dan Wanda Aka Biznewa Almajiransa Sama da Mutum347 a Rami Daya Batare da An Banbance Namiji da Macce Ba Babba da yaro Wasu Ma Da Sauran Ransu Haka aka Tur buda Masu Kasa Aka Rufe su A Mando dake Kaduna, Nine Dan wanda Aka ja Gangar Jikinshi akan Gawar Yayansa da Aka Kashe a gabansa Aka Sanya shi Cikin Baro aka tu rashi K**ar Bola, Nine Dan Wanda aka Hana su Ganin Likita dukda Rashin Lafiyar dake Damunsu; Nine Dan Wanda Ake tsare dashi Fiye da Shekara bakwai Batare daya Aikata Laifin Komai ba, Nine Dan Wanda Ake cigaba da cutarwa da Keta ma Haddi A matsayinsa Na Mutum , Nine Dan Wanda S**a so Ketawa Haddi Lokacin Kaishi Kotun Kaduna Da Nufin Zasu kai shi Tsirara.

Wazai Taimakeni???????

Irin waɗannan abubuwan da suke faruwa, shi ya sa kullum mu ke faɗa wa al'ummar Musulmin Nijeriya cewa; mu Musulmin Nijer...
25/05/2024

Irin waɗannan abubuwan da suke faruwa, shi ya sa kullum mu ke faɗa wa al'ummar Musulmin Nijeriya cewa; mu Musulmin Nijeriya ba mu sa buƙatar wata tsiyar ƙasa wai ita NIJERIYA. Su waɗanda s**a ƙirƙiri ƙasar nan ba su ƙirƙire ta domin ku ba.

Sun ƙirƙiri Nijeriya ne domin manufofi da burorinsu na mamaya, matuƙar kuwa Nijeriya ta wanzu, kuma a irin wannan tsarin da ta ke akai, to, ba za ta taɓa amfanar wani ɗan Nijeriya ba (musamman Musulmi). Matuƙar Nijeriya ta wanzu, to, an dinga cin zarafi da wulaƙanta addininmu da Annabinmu (S) kenan, mafitar ba wai ta zaɓe ba ce, mafitar ta me ake ɗora ƙasar ne, ko kun zaɓi Musulmi ɗan Arewa, ko ma wa za ku zaɓa indai a tsarin tsinannen ‘constitution’ ɗin Nijeriya ne, ba wata mafita da za ku samu, kullum kun dinga ganin ƙasƙanci da wulaƙanci kenan. Yadda Buhari bai zamo maku mafita daga wahaloli ba, haka babu wani da zai zamo ma ku mafita a wannan shegen tsarin ‘constitution’ ɗin da Turawa s**a ɗora ƙasar nan.

Ko dai ku farka daga dogon barcin da ku ke yi (ku nemawa kanku mafita ta din-din-din) ko kuma ku ci gaba da rayuwa a wulaƙance, ƙarshe ku mutu a banza.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'unHaƙiƙa wannan rashi ne mai radadi da girgiza zukatan Muminai da ma'abota mutuntaka. M...
20/05/2024

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un
Haƙiƙa wannan rashi ne mai radadi da girgiza zukatan Muminai da ma'abota mutuntaka. Mun shaida Sayyid Ebrahim Ra'isi bawan Allah ne, Muminai, mai sallamawa ga Ma'abocin al'amari, mai taimakon raunana, mai sadaukarwa a tafarkin Allah Ta'ala.
Mun shaida ya yi aiki a aikace wajen cika alwashin Waliyul Amril Muslimina akan jabberan sahayoniyawa, inda ba kawai marinsu ya yi ba, ya mangare su ne, s**a kife, ya tattake su, s**a muzanta. Muna masa fatan samun babban matsayi a wajen Allah kan kaskanta jabberai da faranta ran raunana Muminai da Mazlumai a wannan lokacin. Kun koma ga Allah kuna madaukaka akan kafircin duniya, ba ku rusuna musu ba.
Mun ƙadu matuka da rashin ku. Allah Ta'ala Ya karbe ku a matsayin Shahidan AddininSa, kai da mukarrabanka da kuka kasance tare a cikin wannan jirgi.
Lahadi 11 ga Zulka'ada 1445 (19/5/2024) ba za ta mantu a zukatanmu ba, k**ar yadda wayewar garinta ya kasance safiya mai radadi a yayin da aka gano tsaunin da jirginku ya faɗa, aka ga jikkunanku masu daraja ba tare da ransu ba. Allah Ya sanyaya ran Imam Khamenie akan wannan musiba mai girma na rashin mabiyi mai biyayya.
Ya Allah 😭😭😭

Jama'a, na kara fahimtar HIKIMA da kuma babban DALILIN da yasa tun farko Allah ya Haramta yin Auren da babu Soyayyar jun...
19/05/2024

Jama'a, na kara fahimtar HIKIMA da kuma babban DALILIN da yasa tun farko Allah ya Haramta yin Auren da babu Soyayyar juna tsakanin Namiji da Mace.A Mazhabin AHLULLBAYTI Auren da babu Soyayya a cikin sa baya Halatta.

Abinda na fahimta shine,ita Soyayya tsakanin namiji da Mace ita ce babban Alkalin dake warware matsaloli tsakanin Ma'aura muddin dama suna yiwa junan Soyayyar gaskiya.

Na taba jin Allama Sayyid Zakzaky yana cewa, anfi so kafin ayi Aure ya zama an yi Soyayya na dan wani lokaci domin su samu fahimtar junansu da sanin halayyar juna,domin su koyi yadda za su zauna da dabi'un juna,domin shi Aure idan anyi ba ana so arabu bane.

Har Sheikh Zakzaky ya ke cewa, kai ko Auren Soyayya ma bayan anyi shi akan jarabce su da kiyayyar juna na dan wani lokaci,kuma lallai idan ba daurewa akayi ba to aureb yana iya mutuwa a wannan lokacin.

Kuma na ta6a jin Sheikh Zakzaky yana cewa, koda anzo ana taron daurin aure ne kafin a daura auren,sai Yarinyar ta ce bata son Auren,to dole a dakatar da daura Auren, domin ba ayin aure sai amincewa su wayanda za a daura wa Auren.

Abinda yasa na kawo wannan maganar shine, sau dayawa wani lokaci shi namiji yakan kasa fahimtar WACECE MACE, Imam Ali(as) yana cewa Dabi'un Mata K**ala ce a wurin su. Wani lokaci shi namiji ya kan so Mace ta zama daya da irin tunanin sa, kuma wannan bazai tab yiwuwa ba.

Hatta ma ko a zamantakewa ne tsakanin iyalin gida zaka ga ana samun rashin jituwa tsakanin Yara Maza da Yara Mata a wani lokacin. Shi namiji yakan yi kokari ya ga cewa ya birge Mace,amma ita kuma alokacin idan bata jin Annashuwa ko kallon sa baza tayi ba, shi kuma zai haushi,amma idan ya kyaleta,ko kuma ya lallashe ta,to shi ma zai samu farin ciki.

Lokuta da dama na ganka yadda wasu ma'auratan ke kasancewa, na rashib jituwa tsakani. Abin mamaki mafiya yawan Auren dole akeyiwa Mata a cikin kashi 95 za ka samu Iyaye Maza sune kan gaba wurin kulla auren dole, ba kasafai ake samun Mahaifiya ta goyi bayan yi ma 'Yar ta aurwn dole ba.

Na ga wasu daga cikin Mazan da s**a kisa rasa ran su a sanadiyyar auren Matar da bata Son sa, na ga wayanda s**a rasa lafyar su, na ga wayanda su ka rasa walwala da kwanciyar hankali.

Akwai wata Yar uwa da mahaifinta ya aurar da ita ga wanda bata so,kuma ya san bata Son namijin,amma ya aurar da ita gare shi, Wallahi tsawon shkara biyu auren babu kwanciyar hankali,kuma ta ki amincewa da shi,daga karshe dole ya sake ta.

Ya Allah kar ka jarabce mu yi rayuwar Aure da Matan da bata Sona.

JINJINA GA ALKALUMAN MARUBUTAN HARKA ISLAMIYYA Ya zama dole nayi jinjina ga gwaraza kuma hazikan Marubutan Harka Islamiy...
18/05/2024

JINJINA GA ALKALUMAN MARUBUTAN HARKA ISLAMIYYA
Ya zama dole nayi jinjina ga gwaraza kuma hazikan Marubutan Harka Islamiyya, karkashin jagorancin Shaikh Zakzaky (H). Lallai kun cancanci yabo da jinjina bisa ga irin kokari da kuke na yin rubututtuka na wayar da kan al'umma akan Harka Islamiyya da kuma casa duk wani wanda ya nemi ya yiwa Harka Islamiyya sharri da kage!
Jinjina musamman ga:
1. Ibrahim Musa
2. Danjuma Katsina
3. Abdulmumin Giwa
4. Adamun Adamawa
5. Harun Elbinawi
6. M. I. Gamawa
7. Aliyu Saleh
8. Saifullahi M. Kabir
9. Sameer El-Hajj
10. Ammar Muhammad Rajab
11. Hassan Bala Al-Rafhidy
12 Ibraheem El-Tafseer
13. Ibrahim Daurawa
14. Shu'aibu Ahmad
15. Haruna Uba
16. Muhammad Darazo
17. Bilya Hamza Dass
18. Shariff Awwal
19. Bilkisu Y. Maitaya
20. Sakina I. Gwadabe
Da sauran su...

Dan Tsokaci:Manufar Da'awar Harkar Musulunci a karkashin Jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) shine yunkuri don dawo d...
18/05/2024

Dan Tsokaci:
Manufar Da'awar Harkar Musulunci a karkashin Jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) shine yunkuri don dawo da ikon addini a wannan nahiyar da muke ciki.
Yunkurin dawo da addini din nan, ana yinsa ne ta hanyar sadaukarwa da tsayawa kyam wajen fuskantar zalunci da azzalumai har a kai ga nasara, nasarar zahiri ta tabbatar addini ko nasarar hakika ta komawa ga Allah cikin biyayyarsa ana masu neman uzuri a wajensa.
Kafin nasara, a kan sha wahala sosai, a kan samu Shahidai da s**a sadaukar da rayukansu saboda Allah. A kan samu masu rauni da aka raunata a wannan tafarkin saboda Allah. A kan kuma samu wadanda aka daure a kurkuku aka azabtar duk saboda Allah.
A irin wadannan wahalhalun da a kan fuskanta ne a ke samun wasu su daure duk runtsi su tsayu kyam a tafarki, a kuma samu wasu su zama masu raki har rakin nasu ya fara sa su fara shinshina wasu hanyoyin neman rangwame da sauki, wanda daga haka da yawa suke lalacewa su kauce daga tafarkin gaskiya. Allah Ya tsare mu.
Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya sha bayyanawa cewa bai yiwuwa a aiko wani Annabi don ya kawo gyara, ko wani mai Da'awa zuwa ga komawa tafarkin Allah, sai kuma ya zama ya shiga aikata irin abin da wadanda ake bukatar a kawar suke aikatawa wai da nufin ta hakan zai kawo gyara. Lallai gyare shi ake yi.
A kan hakan, lallai yan uwa ma'abota gwagwarmaya kar su sake su shiga rudu, mu yi kokarin fahimtar cewa lallai Jagora (H) ba zai taba sauya hadafi ba, kira yake zuwa ga komawa tafarkin Allah tun fiye da shekaru 40, kuma a kan wannan yake har gobe. A kan haka ya sadaukar da komai nasa. Babban burinsa shine wannan maguzancin da Bature ya kafa ya dankara mana da sunan Damukuradiyya a wannan kasar, ya zama miyagu, fasikai, fajirai, ashararan mutane suke jansa, ya zama an nannade shi an kawar da shi baki daya, an shimfida Musulunci na hakika.
Ya k**ata kuma mu iya lura da cewa akwai abin da ake kira 'principle', k**ar yadda Jagora (H) ya sha faɗa, shine manufa ko hadafi. Kuma hadafin nan na Harka shine yunkurin tabbatar addini. Sannan akwai abin da ake kira 'policy', wanda shine hanyar bi don cimma hadafi, shi yana iya canzawa daidai da canzawar yanayi. Wanda kuma hanyoyi suna da yawa, daga cikin hanyar da Jagora ya sha faɗa su yake bi don cimma manufarsa akwai amfani da Ilimi, da Hankali da Sahihin addini.
Ilimi shine, magana da mutane a irin sigar da suke fahimta, da bayyana musu dalilai a ilmance wanda wannan ke sa su amsa kiran. Hankali kuwa shine ke sa ya zama ba ana dira a kan mutane da duka ko zagi bane, bare kisa ko barnata dukiya, wanda wannan ke sa a gane mu ba barazana bane. Sannan kuma Sahihin addini na nufin bin irin tafarkin Manzon Allah (S) da Ahlulbaiti (AS) na nunawa azzalumai yatsa da kin yi musu sassauci ko da za su cire kai sai dai su ciren, ba tare da an rusuna ko an bi kazamin tafarkinsu ba.
Daukar makami a yi yaki, ko shiga siyasa, ko shirya karairayi da sharruka da sauransu duk suna daga 'Policies', hanyoyi ne da za a iya bi don kokarin cimma wata manufa, kuma duk wasu mutane ko Kungiyoyi daban-daban su kan tafi a kansu, amma matafiyar Jagora (H) sune wadannan abubuwan da ya saba faɗa, Ilimi, Hankali da Ingantaccen addini.
A kan wadannan ya k**ata mu doru. In har dan uwa na bibiyar jawaban Jagora (H) har na ziyarar karshe da aka yi, tun bayan fitowarsu, kullum yana nanata mana mafitarmu na a daukewa kyam ne a tafarkin addini, yana kuma nunawa mutane cewa mafitarsu ba shi a wannan rudadden tsarin da ke basu damar su zabi sabo ko tsohon macucinsu a matsayin maceci.
Na'am, kun tuna a baya can kafin Waki'a bayan da aka samu kyakkyawar alaka da fahimta da wasu Kiristoci, har Pasto ya roki Jagora (H) kan sun aminta, kuma suna rokon a samar musu da Dandalin Kiristoci a karkashin Harkar Musulunci, take Sayyid (H) ya amsa, aka kira su da 'Christian Forum under the Islamic Movement', ya zama su suna nan a Kiristocinsu, amma sun yarda da manufar Harka na a dawo da addinin Musulunci ya zama shi ke iko, a tsai da adalci a kasa ga kowa maimakon wannan tsarin da ke tafi da kasar a rikice.
Sai ya zama Kiristoci ne su, amma suna taimakon Harkar Musulunci ta wata fuska na kusanto da mutanensu zuwa ga fahimtar fadin Imam Ali (AS) cewa "Mutum ko dai dan uwanka ne a addini ko kuma abokin gwaminka a halitta." Suna ta aikinsu na wanzar da zaman lafiya tsakanin Kiristoci da Musulmi, suna aikinsu na sanar da yan uwansu cewa Musulunci ba barazana bane, wannan barna da ake da sunan Musulunci ba Musulmi ke yi ba, kuma ko Musulmi ne mai yi, ba sunansa Musulunci ba. Suna ta kokarin fahimtar da su manufar Harkar Musulunci a irin yaren da suke ganewa.
To, babu mamaki, tattare da dagulewar lamuran kasar nan, da yadda siyasarta ke kazancewa, idan aka samu wasu kuma wadanda suke su yan Siyasar ne, kila suna cikinta da su ake damawa, kila sun san ta daga waje, sai s**a fahimci Harkar Musulunci, s**a ga cewa su tare da cewa yan Siyasa ne, amma sun gamsu da cewa za su iya ba Harkar Musulunci gudummawa a janibinsu a siyasance. Mai sauki ne su nemi a basu dama, Jagora (H) yace ku je an baku sunanku Dandalin Siyasa a karkashin Harkar Musulunci. Wannan kuma bai sabawa 'policy' din Harka ba, don ba bangaren hadafi bane.
Ka ga yadda Kiristoci a karkashin Harkar Musulunci suke hulda da yan uwansu suke ba da gudummawarsu ta wasu fuskoki, su ma wadannan 'yan siyasar sai su je tunda suna haduwa da yan uwansu suna kokarin wayar da kansu a kan manufa da hadafin Harka, ba tare da kyale miyagun Malamai da makusanta suna sanar da su ba.
Ko da yake aiki ne mai hadari, musamman ga ma'abocin addini da shiriya ya mai da kansa layin 'yan siyasar kasar nan, domin gaskiyar magana kazanta ce da in mutum ya fada mata yana wahalar wankuwa, dilmiyewa yake yi ya yi nitson da sai dai kuma wani rahamar Allah Ta'ala. K**ar yadda dangwalawa wani da nufin zuwansa karaga na nufin amincewarka da ayyukan da zai aikata a yayin da ya ci, kuma tunda Allah Yace, wanda ya aikata misalin zarra na Alkairi ko sharri zai gani a ma'auninsa ranar Alkiyama. Kuma ya bayyana taimakon azzalumi a matsayin tarayya da shi a zalunci, to fa makoma abin ji ne.
Don haka, ga dan uwa mai gwagwarmayar addini, shawara gareka, ka tsaya kyam a kan tafarkin gwagwarmayarka. Ka tsaya a matsayar Jagora (H) da ka santa yake ta jaddada maka ita. Babu wata rana da Jagora (H) zai ce ka je ka shiga wannan tsarin, ko ka je ka dangwala kuri'arka ga wani macuci don ya ceceka. Wallahi babu wannan ranar. Amma in ka ga wasu sun je ga Jagora sun ce za su ba da gudummawa ta fuska kaza, ya musu ijaza, wannan bai k**ata ya zama maka damuwa ko abu mai nauyi ba, tunda ba abu ne da ya shafi hadafi ko manufa ba, bangare ne da za su ba da gudummawa daidai da Layin da suke kawai.
Kai in ma aka ace Jagoran ne ya samar da su (alal misali), to babin 'Policy' ne, bai shafeka ba, kai ka tsaya kyam a bangarenka ka zura ido gare su yi aikinsu. Sai ka yi musu fatan Allah Ya basu ikon cika alkawarin nauyin da s**a dorawa kansu. Barsu su yi abinsu, ba ma sai ka yi magana a kansu ko zargi ko kushe ba.
Kai kila kana Dandalin Dalibai na Harkar Musulunci, ka ga wani kuma yana Dandalin Mawaka, wata rana Dandalin Kiwon Lafiya, wata na Dandalin Marubuta na Harka, wasu suna Lajanonin tsaro, wasu na Dandalin Ma'aikata ko na masu kudi, kuma duk na Harkar Musulunci. Shikenan, kila cigaba ya kawo an samu Dandalin 'yan siyasa. Duk sai kowa ya yi ta ba da gudummawarsa har zuwa lokacin da za a rusa tsarin da ke ba kazamai damar rike muk**an Siyasar kasar, a maye gurbin siyasar Mu'awiyyanci da irin ta Amirulmuminin (AS) wacce za ta zama bisa turbar Allah da Annabi yace, kuma ya zama Muminai masu tsoron Allah ne ke rike da muk**anta.
Allah Ya tabbatar da mu a kan tafarkinSa. Ya karawa Jagoranmu Sayyid Zakzaky (H) lafiya da kariya. Ya cika burinsa na ganin mun shiryu, mun tsayu kyam mun kau da wannan tsarin kafircin, addinin Musulunci ya yi iko da mu a doron kasa.

Address

Saminaka

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mu'asasatu Aliyul Akbar. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mu'asasatu Aliyul Akbar.:

Share


Other Media/News Companies in Saminaka

Show All