26/04/2024
Wani daga cikin Magabata na kwarai yace, "Abubuwa uku ana jaraba hankalin Mazaje dasu
- Yawan Dukiya
- Masifa,(ma'ana Jarabawa)
- Da Mulki."
Abdullahi Dan Muhammad al-Harwiy(R) yace, "Bayyananniyar Biyayya ga Allaah itace, boye Masifa(idan ta sameka) har a rinqa tsammanin masifa bata taba samunka ba."
Aun Bin Abdullahi yace, "Alherin da ba Sharri a tattare dashi shine, Godiya a yayin yalwa da haquri idan Masifa ta sameka."
Aliyu Bin Abiy-Dhālib(R) yace, "Haquri iri uku ne, Haquri da Masifa da haquri akan yima Allaah biyayya da haquri akan qin sabama Allaah, Wanda yayi haquri da musiba har ya dankwafar da ita da mafi kyawon haquri to za a rubuta mishi daraja dari uku, Wanda yayi haquri da yima Allaah biyayya za a rubuta mishi daraja dari shidda, Wanda yayi haquri akan qin sabama Allaah za a rubuta mishi daraja dari Tara."
Maimūn Dan Mihraan(R) yace, "Haquri da Masifa(idan ta sameka) abune Mai kyau, amma mafi falalar hakan shine haquri akan qin sabama Allaah."
Ahmad yace, Baban Mu'awiya ya bamu labari, A'amash ya fada Mana, daga Mujāhid, yace, Umar Dan Khaddāb yace, "Mun riski alheran rayuwarmu ne da haquri."
Aliyu Bin Abiy-Dhālib(R) yace, "Matsayin Haquri ga Imani kamar matsayin Kai ne ga Jiki, idan aka yanke Kai to an rusa Jiki, said ya daga Murya yace, ku dakata! Ba imani ga Wanda baida haquri."
Umar Bin AbdulAziz(R) yace, "Ba Wata ni'imar Allaah da zata gushe daga bawa face sai haquri ya dawo da ita, Kuma face abinda haqurin zaizo dashi sai yafi abinda ya gushe da farko alheri."
Yunus dan Zaid yace, na Tambayi Rabee'ata Dan Abiy-AbdulRahman minene matuqar haquri?, sai yace, "Ya kasance Ranar da Masifa ta samu bawa ta zamana kamar ranar da take kafinsa."
ma'ana ya fawwala komai ga Allaah, domin duka dai ya faru ne bisa qaddarawarSa, da saninSa hakan ta faru, Kuma Yasan zata farun tun kafin ta farun.
Allaah Ya datar da mu.