Radio Kano

Radio Kano Wannan Shi ne Shafin Gidan Rediyon Kano. Za ku iya turo mana sakonnin Ra'ayoyinku da Shawarwarinku.
(2)

Gwamna Yusuf Ya Bukaci Sababbin Shugabannin NNPP Na Kasa Su kasance Masu Kishin Jam’iyya Da Hadin KaiDisamba 20, 2025Gwa...
21/12/2025

Gwamna Yusuf Ya Bukaci Sababbin Shugabannin NNPP Na Kasa Su kasance Masu Kishin Jam’iyya Da Hadin Kai

Disamba 20, 2025

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi kira ga sabbin shugabannin kasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) da aka zaba da su zamo masu jajircewa, aiki tukuru da kuma rungumar kowa da kowa domin ƙara wa jam'iyyar karsashi da kwarin guiwa domin cimma manufofinta.

Wakilin mu Hussain Kabir minjibir ya ruwaito mana, cewa Gwamna Yusuf ya yi wannan kiran ne yayin da yake jawabi ga wakilan jam’iyyar a bikin rantsar da sababbin shugabannin kasa na NNPP, wanda aka gudanar a birnin Abuja.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sake jaddada kudirin jam’iyyar na tabbatar da nagartaccen shugabanci, walwalar al’umma da kuma kare ka’idojin dimokiradiyya a fadin Najeriya.

Ya kuma bukaci mambobin jam’iyyar da su rungumi hadin kai, biyayya da sadaukarwa wajen matsayar da muhimman ginshikai na cimma burin al’ummar kasa baki daya.

Taron ya samu halartar manyan shugabannin jam’iyyar da wakilai daga jihohi 36 na kasar nan, inda aka tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi alkiblar siyasa da makomar jam’iyyar NNPP.

Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) ta gudanar da Babban Taron Kasa (National Convention) a Abuja, inda wakilai s...
21/12/2025

Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) ta gudanar da Babban Taron Kasa (National Convention) a Abuja, inda wakilai s**a gudanar da zaɓe tare da rantsar da sabbin shugabannin ƙasa da za su jagoranci jam’iyyar na tsawon shekaru huɗu.

A yayin taron dai, Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso an sake tabbatar da shi a matsayin Jagoran NNPP na Kasa, yayin da Dr. Ajuji Ahmad ya sake zama Shugaban Jam’iyyar na Kasa.
Haka kuma, an zaɓi Hon. Dipo Olayokun a matsayin Sakataren Jam’iyya na Kasa, sannan Hon. Oladipo Johnson ya zama Sakataren Yaɗa Labarai na Kasa.

An gudanar da zaɓen cikin lumana, tare da rantsar da dukkan waɗanda aka zaɓa domin fara aiki nan take.

Kai tsaye daga Dakin taro na Grand Pela Hotel dake Area One Garki Abuja inda ake gudanar da taron jam'iyyar NNPP, wato E...
20/12/2025

Kai tsaye daga Dakin taro na Grand Pela Hotel dake Area One Garki Abuja inda ake gudanar da taron jam'iyyar NNPP, wato Elective National Convention of NNPP.

20/12/2025

Kashi na biyu
SHIRIN KAN DAKI NA YAU ASABAR YA KARBI BAKUNCIN MANAJAN DARAKTAN HUKUMAR RAYA BIRANE TA JIHAR KANO WATO KNUPDA ARC. HAUWA HASSAN TUDUN WADA

20/12/2025

SHIRIN KAN DAKI NA YAU ASABAR YA KARBI BAKUNCIN MANAJAN DARAKTAN HUKUMAR RAYA BIRANE TA JIHAR KANO WATO KNUPDA ARC. HAUWA HASSAN TUDUN WADA

20/12/2025

Aslm.
"جمادي الآخرة ١٤٤٧ هجرة"
Yau.........................
Assabar(السبت) 29
Jumadal-Akhir(جمادي الآخرة)
29/6/1447 Hijrah dai dai da
20/12/2025.
{وَالَّذِينَ يَكْنِزُونَ الذَّهَبَ وَالْفِضَّةَ وَلَا يُنْفِقُونَهَا فِي سَبِيلِ اللَّهِ فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيم}.
(التوبة ٣٤).
"Kuma wadanda suke tara zinariya da azurfa, kuma ba su ciyar da su a cikin tafarkin Allah to ka yi musu bushara da wata azaba mai radadi."
(At-taubat 34).
إنما الصدقات للفقراء والمساكين والعاملين عليها والمؤلفة قلوبهم وفي الرقاب والغارمين وفي سبيل الله وابن السبيل فريضة من الله والله عليم حكيم. (التوبة ٦٠)
Abin sani kawai, dukiyoyin sadaka(zakka) na faqirai ne da miskinai da ma'aikanta da wadanda ake lallashin zukatansu(zuwa ga musulunci) da kuma acikin fansar wuyoyi('yanta bayi), da wadanda ake bi bashi, da acikin hanyar Allah da dan tafarki(matafiyi wanda guzirinsa ya yakare). Farilla ce daga Allah. Allah kuwa Masani ne, Mai hikima.(Altauba 60).
NISABI DA DINAR(الدينار)
SADAKI:------------------
#148,750:00.
ZAKKA:-------------------
#11,900,000:00.
DIYA:-----------------------
#595,000,000:00.
Allah me girma yace:-
"ان الصلاة كانت على المؤمنين كتابا موقوتا". ( النساء ١٠٣).
"Lalle ne Sallah ta kasance akan Mumunai, farilla me kaiyadaddun lokuta".
(An-Nisaa 103).
LOKUTAN SALLAH A KANO, NIGERIA.
K.Alfajar:. 5.25. A.M.
H. Rana:. 6.41. A. M
Zuhur:..... 12.24. P. M.
Asar......... 3.40. P. M.
Magrib.... 6.06. P. M.
Isha......... 7.22. P. M.
(ان شاء الله)
Allah yabamu lafiya da zaman lafiya da karuwar arziki.
Sheikh Ibrahim Falaki.

19/12/2025

Duniya Ina Labari Tare Da Abdussalam Na'iya Gwammaja

Fittacen malamin addinin musulunci a nan jihar Kano, Farfesa Umar Sani Fagge ya miƙa kyautar Al-Qur'ani Mai Girma ga sas...
19/12/2025

Fittacen malamin addinin musulunci a nan jihar Kano, Farfesa Umar Sani Fagge ya miƙa kyautar Al-Qur'ani Mai Girma ga sashen da ke kula da ɓangaren masu larura gani ta hukumar kula da ɗakunan karatu ta jihar Kano

Fittacen malamin addinin musulci a nan jihar kano Farfesa Umar sani fagge ya Mika kyautar alqura,ni Mai girma ga sashen da ke Kula da bangaren masu larura gani ta hukumar…

19/12/2025

Fassarar Khudubar Juma'ar Masallacin Madinah tare da Dr. Ashir Harun Muhammad.

19/12/2025

Kai-tsaye daga Zauren Majalisar Tarayya yayinda shugaba Bola Ahmad Tinubu yake gabatar da Kasafin Kudin shekara mai kamawa 2026.

‎19/12/25Gwamnatin Kano ta dauki sabbin ma'aikata 120 a hukumar tattara haraji ta jihar, da nufi samar da karin kudin sh...
19/12/2025

‎19/12/25

Gwamnatin Kano ta dauki sabbin ma'aikata 120 a hukumar tattara haraji ta jihar, da nufi samar da karin kudin shiga, da samawa matasa ayyukan yi.

‎Da yake ƙaddamar da raba takardun aikin Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jaddada wa sabbin ma'aikatan kudirin gwamnatin sa na karfafa hanyoyin tattara haraji domin bunkasa kudin shiga ta yadda gwamnati zata samu sukunin gudanar da ayyukan ci gaba yadda ya kamata.

‎Gwamnan ya kuma bukaci sabbin ma’aikatan da su kasance masu gaskiya, rikon amana da bin ka’idojin aiki, domin cimma manufofin da aka dora wa Hukumar Tattara Harajin ta Kano.

‎A nasa jawabin Shugaban Hukumar Tattara Haraji ta Kano, Dr Zaid Abubakar, ya bayyana cewa daukar sabbin ma’aikatan zai taimaka matuka wajen inganta ayyukan hukumar da kara yawan kudaden haraji da jihar ke samu.

‎Da suke jawabi jim kadan da karbar takardun wasu daga cikin wadanda s**a rabauta sun bayyana godiyar su tare da alƙawarin aiki tsakani da Allah.

‎Wakilin mu na gidan gwamnati Hussain Kabir minjibir yace taron ya samu halartar kwamishinoni da masu baiwa Gwamna Shawara da daraktaocin hukumar tattara kuɗin shiga na jihar Kano.

‎HKM

19/12/2025

SALLAR JUMA'A DAGA MASALLACI CIKIN GARI NA FADAR MAI MARTABA SARKIN KANO MALAM MUHAMMADU SUNUSI II

Address

No. 1 Ibrahim Taiwo Road, Gidan Bello Dandago
Kano
700234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Radio Kano posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Radio Kano:

Share